Sashe 6
Hafsatu Manga Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cike da bacin rai Yarima ya kwanta saboda abunda ya faru, daman duk abunda ya aikata Anty Ummi Dada Yalwa take blaming saboda be da gurin zuwa sai can kuma be da abokiyar shawara sai ita. Wannan dalilin ne yasa be farka cikin walwala ba, as usual Masallacin fadar yai sallah asuba, sannan ya dawo part dinsa yai azkar din safe.
Around nine o'clock Abida ta kawo masa abincin safe wato breakfast, sai da ya shiga yai wanka ya shirya cikin kananan kaya ya shefe jikinsa da turare mai kamshin sannan ya nufi falon dan karyawa.
Dinning room ya zauna yana bude abinci, it's his favorite indomie da kwai da kuma kifi sai ginger tea da. Spoon ya dauka ya soma cin indomie sai kawai yarinyar daya gani jiya ta fado masa a rai, ya tuna jiya gaba daya a mafarkinsa yarinyar nan ce har ruwa yana dukanta, kuma yasan jiyan anyi ruwa maybe bata samu gurin fakewa ba tun da yaga gurin da take zaune ba inda zata fake har tana kukan yunwa.
Da sauri ya tashi daga cin abincin da yake ya koma bedroom ya dauki wayarsa da keys ya fice daga part din.
A al'adarsa baya fita daga gidan har sai yaje ya gaishe da Mai Martaba da kuma Dada amman yau saboda hankalinsa ya dauko yana fitowa ya nufi parking space, motarsa ya shiga yai mata key tun kan ya karasa Babban Gate ya soma horn, cikin rawar jiki masu gadin suka bude masa suna gaisheshi.
@360 ya hau titi, daga kan wurin sarkin zuwa gada biyu tafiyar 32 minute ce sai gashi ya isa cikin 18 minute saboda gudun da yai, a gurin ya fara tsayawa da motar ya bude ya fito hankalinsa duk a tashe sai a yanzu yake jin rashin kyautawar barinta a nan duk da be san ko wacece ba. Hangota kwance kamar matacciya yasa gabansa faduwa cike da sanyin jiki ya karasa kusa da ita.
Ba a jin tafiyarsa dan haka bata san da mutum ba sai da ta ganshi tsaye a kanta, cikin rashin kuzari ta tashi zaune tana shirin fashewa da kuka jikinta sai rawa yake. Dukawa yai yana kallonta kamar yadda itama ta sako masa manyan idanuwanta tana masa kallon tsoro, a hankali ya kai hannu ya taba ta so yake ya tabbatar idan mutum dince da gaske. Sai akwai ta gantsara masa cizo, da sauri ya janye hannunsa yana dan bude ido tare da kare mata kallo, yarinya ce karama da ba zata wuce shakara takwas zuwa tara ba, gashin kanta yai bujibuji kamar mahaukaciya.
Baya baya ta soma yi cike da tsoronsa.
“Ke ke ke ba cutar da ke zan yi ba”
“Ni ban yarda da kai ba...”
Ta furta cikin shagwaba da son fashewa da kuka.
“Ke listen....”
“Ni ba lesa ne sunana ba, kai mugu ne...”
“No no nono...”
Be karasa ba ta zaro ido.
“Kai dan iska ne ko? Ni bani da Nono”
Ta dafe kirjinta tare da fasa wani uban ihu, aiko ba shiri ya tashi tsaye da sauri ya bar gurin har yana shirin faduwa...
*HAFSATU MANGA*
_Yarinyar Kauye_
Wattpad @KhadeejaCandy
6⃣
Zaunawa yai saman kujera ya dafe kansa, sam be jidadin tafiyar Hafsat ba, yasan bata da gurin zuwa kuma bata san ko ina ba a garin nan bayan haka kuma gata yarinya karama.
“Uncle wacece ta tafi?”
Amal ta tambaya tana kama hannunshi, dagowa yai ya kalleta kamin ya bata amsa Anty Ummi ta turo kofar falon ta shigo tare da sallama.
Yaranta ne suka amsa mata suka je da sauri suna mata oyoyo ita kuma ta rumgume su fuskarta dauke da murmushi.
“My headache an dawo ko?”
Duk suka hada baki gurin cewa
“Yes Anty Ummi”
A hankali Zain ya juyo ya kalleta, sannan ya mike tsaye ya karasa bakin kofar inda take tsaye.
“Wai mahaukaciyar yarinyar nan ta bude mata ta fita”
“Farhat?”
“Ita”
Yana fadar hakan ya kai hannu ya bude kofar falon ya fice ba tare da ya kara cewa komai ba.
“Zain kana son ganin laifin Farhat Wallahi to idan bata bude mata ta fita ba ya zata mata”
Ta fada cikin yanayin damuwa, sannan ta nufi bedroom dinta Amal na biye da ita a baya, Ali da Muhammad kuma suka nufi kitchen dan neman abunda zasu ci.
Ya samu kansa cikin yanayin damuwa sosai, yasan ko ya kansa a neman yarinyar nan be san inda zai ganta ba. Wani haushin Farhat yaji ya karu a ransa, duk ita ya dorawa laifi, kamar marar lafiya haka ya isa Kanwurin Sarki, tun daga bakin babban gate fadawa keta gaisheshi amman be kulasu ba har ya faka motarsa a babban kofar Mai Martaba, ya dade zaune cikin motar sannan ya bude ya fito ya nufi babar hanyar da zata sadashi da fadar mai martaba, a iya saninsa Mai martaba na fada yanzu dan yana shiga fada a duk Monday a daidai wannan lokacin gashi kuma dazu ya fita be gaishe ba da dada, dan haka ya kamata a yanzu ya shiga ya gaishe shi kamin ya karasa sashen Dada, tun da ya hango kofar fadar a kunne abun ya bashi mamaki, kawar da kwankwanto yasa ya kai hannu ya taba kofar fadar, sai ya samu kofar a kulle, hakan ya sashi fitowa gaba daya ya dawo ya zagaya ya mike doguwar hanyar da zata sadashi da cikin gidan.
Duk gaisuwar da ake masa be ji ba saboda hankalinsa baya gurin, ko da ma yana gurin ba zai amsa ba dan be saba amsa gaisuwarsu ba. Tsakar gidan katon tsakar gidane mai cike da shuke shuken fulawoyi, an kawata jikin ginin da fanti fari sai aka kawatar tsakiyar da fenti golden mai haske da sheki, kowa da part dinsa gate ya raba su, daga gefen gate dinsu akwai wani gate na bayi da ma'aikatan gidan, daga bangaren hagu kuma akwai sashen da ake dafa abincin gidan na kowa da kowa, dama da kau kuma babban hanya ce da zata sadaka da sashen mai martaba.
Bangare Hajiya Hadiza ya fara shiga katsancewar ita ce uwargidan mai Martaba, Sisters din ya tarar a cikin falon, cikin girmamawa da mutumci suka gaisheshi, be amsa musu ba kasancewar daya bayan daya suke gaisheshi, sai kawai ya ce
“Ina Hajiya?”
“Bata nan sun fita tare da Mama da kuma Dada Yalwa da Mai Martaba”
Rafila ta amsa masa
“Gurin me?”
“Gurin gaisuwa, wani kauye wai Yayan Hajiya dake sarautar garin aka kashe”
Juyawa kawai yai ya fice, hannayensa zube cikin aljihu, yana takawa a hankali har ya fita daga sashen gaba daya, part dinsa ya nufa kai tsaye yana ciro wayarsa dake ringing a aljihu, yai parking ya kara a kunne amman ya kasa magana kamar ba babban abokinsa ne ya kira shi ba.
“Zain kasa muna da tiyata uku da rabi fa kuma ka fita yanzu”
Sauke wayar yai a kunnesa ya katse kiran, a duniya ya tsani a tuna masa abu, ko da kuwa ya manta din ne balle kuma ba kasafai yake yawan mantawa da abubuwa. Keys yasa ya bude kofarsa, idan zai fita baya rufe janyowa kawai yake amman idan ya dawo sai ya bude da keys. Yana saka kafarsa cikin falon wani dadadden kamshi ya daki hancinsa, abun mamaki an gyara komai na falon an cire hotunan matarsa.
Dada ce kawai take da keys din part dinsa, idan ma za a masa gyara a hannunta ake karbar keys a bude dakin, bacin ran dake cikin ransa ne ya karu, har ya soma jin numfashinsa na taushewa.
Freezer ya nufa ya bude ya dauko gorar ruwa ya bude marfin ya kafa gorar a baki be sauke ba sai da ya shanye ruwan cikin gaba daya, sannan ya rufeta ya nufi kitchen ya jefata a kwandon shara.
Miyasa Dada Yalwa zata masa haka? Saboda yai fada da Hameeda ko kuma saboda yau fita be gaisheta ba? Ko kuma tana nunanin ganin hoton Haleema ne ke sakashi yin fada da Hameeda.
“Ban ga dalilin da zaisa ki dauke min hoton Mata ba Dada”
Ya fada a haka kamar mai rada, kana ya sauke ajiyar zuciya kallon windows kitchen din. Ya dade a tsaye kamar sannan ya juyo ya nufo bedroom yana cire yellow T-shirt din dake jikinsa, sannan ya daurawa tawul ya shiga wanka. Be wani dade ba ya fito ya shirya cikin wasu kananan kayan ya fito da sauri dan lokacin shiga tiyarsu ya kusa.
Be shiga wata motar ya shiga wacce ke part dinsa ba wacan ta dazu ba, a gagauce ya fita daga gidan, ko kadan baya son saba dokar aikinsa, yakan kiyayen duk abunda ya shafi aikinsa saboda yasan muhimmancinsa. 3:20 ya isa asibitin, a gurin sa aka tanada ma manyan likitoci su aje motocinsu ya faka motarsa. Sannan ya fito ya nufi cikin asibitin.
“Allah ya taimaki Doctor”
Wani mutun dake fitowa daga Emergency ya fada yana masa irin gaisuwar nan ta girmamawa. Sai a lokacin hankalin Zain ya kai gurinsa.
“Sadiq me kake a nan?”
Ya fada sanin mutumen da yai dan unguwarsu su Anty Ummi.
“Wallahi wata karamar yarinya wani mutum ya kade shine muka raka biyo mutumen nan saboda ba a san kowa nata ba”
“Ayyah Sorry Allah bata lafiya, zan shiga tiyata”
Ya fada yana kokarin wuce, dan hankalinsa gaba daya yanzu yana gun tiyatar da zasu shiga.
“Okay Allah yasa ayi a sa'a”
Ya fada cike da girmamawa.
FARHAT POV.
“Marar mutunci bulutu, ai daman na san ba so na kike ba tunda uwarki ma ba sona take ba, yanxu duk hallacin da Bashir yai miki ki rasa da abunda zaki saka masa sai wannan? Idan ma da gaske ne miyasa baki zo kin same da maganae ba, sai kije xan wani guri kina fadar sirrin gidana, daman haka kuke da Ummi shiyasa baki da gurin zuwa sai can ko?”
Faduwa tai zaune, idonta ya rufe ruf bata ganin komai saboda hawaye. Kalma daya ta Anty rukaiya bata shiga kunnenta bata ganin komai sai pre-wedding picture din Auwal da wannan yarinya.
Around nine o'clock Abida ta kawo masa abincin safe wato breakfast, sai da ya shiga yai wanka ya shirya cikin kananan kaya ya shefe jikinsa da turare mai kamshin sannan ya nufi falon dan karyawa.
Dinning room ya zauna yana bude abinci, it's his favorite indomie da kwai da kuma kifi sai ginger tea da. Spoon ya dauka ya soma cin indomie sai kawai yarinyar daya gani jiya ta fado masa a rai, ya tuna jiya gaba daya a mafarkinsa yarinyar nan ce har ruwa yana dukanta, kuma yasan jiyan anyi ruwa maybe bata samu gurin fakewa ba tun da yaga gurin da take zaune ba inda zata fake har tana kukan yunwa.
Da sauri ya tashi daga cin abincin da yake ya koma bedroom ya dauki wayarsa da keys ya fice daga part din.
A al'adarsa baya fita daga gidan har sai yaje ya gaishe da Mai Martaba da kuma Dada amman yau saboda hankalinsa ya dauko yana fitowa ya nufi parking space, motarsa ya shiga yai mata key tun kan ya karasa Babban Gate ya soma horn, cikin rawar jiki masu gadin suka bude masa suna gaisheshi.
@360 ya hau titi, daga kan wurin sarkin zuwa gada biyu tafiyar 32 minute ce sai gashi ya isa cikin 18 minute saboda gudun da yai, a gurin ya fara tsayawa da motar ya bude ya fito hankalinsa duk a tashe sai a yanzu yake jin rashin kyautawar barinta a nan duk da be san ko wacece ba. Hangota kwance kamar matacciya yasa gabansa faduwa cike da sanyin jiki ya karasa kusa da ita.
Ba a jin tafiyarsa dan haka bata san da mutum ba sai da ta ganshi tsaye a kanta, cikin rashin kuzari ta tashi zaune tana shirin fashewa da kuka jikinta sai rawa yake. Dukawa yai yana kallonta kamar yadda itama ta sako masa manyan idanuwanta tana masa kallon tsoro, a hankali ya kai hannu ya taba ta so yake ya tabbatar idan mutum dince da gaske. Sai akwai ta gantsara masa cizo, da sauri ya janye hannunsa yana dan bude ido tare da kare mata kallo, yarinya ce karama da ba zata wuce shakara takwas zuwa tara ba, gashin kanta yai bujibuji kamar mahaukaciya.
Baya baya ta soma yi cike da tsoronsa.
“Ke ke ke ba cutar da ke zan yi ba”
“Ni ban yarda da kai ba...”
Ta furta cikin shagwaba da son fashewa da kuka.
“Ke listen....”
“Ni ba lesa ne sunana ba, kai mugu ne...”
“No no nono...”
Be karasa ba ta zaro ido.
“Kai dan iska ne ko? Ni bani da Nono”
Ta dafe kirjinta tare da fasa wani uban ihu, aiko ba shiri ya tashi tsaye da sauri ya bar gurin har yana shirin faduwa...
*HAFSATU MANGA*
_Yarinyar Kauye_
Wattpad @KhadeejaCandy
6⃣
Zaunawa yai saman kujera ya dafe kansa, sam be jidadin tafiyar Hafsat ba, yasan bata da gurin zuwa kuma bata san ko ina ba a garin nan bayan haka kuma gata yarinya karama.
“Uncle wacece ta tafi?”
Amal ta tambaya tana kama hannunshi, dagowa yai ya kalleta kamin ya bata amsa Anty Ummi ta turo kofar falon ta shigo tare da sallama.
Yaranta ne suka amsa mata suka je da sauri suna mata oyoyo ita kuma ta rumgume su fuskarta dauke da murmushi.
“My headache an dawo ko?”
Duk suka hada baki gurin cewa
“Yes Anty Ummi”
A hankali Zain ya juyo ya kalleta, sannan ya mike tsaye ya karasa bakin kofar inda take tsaye.
“Wai mahaukaciyar yarinyar nan ta bude mata ta fita”
“Farhat?”
“Ita”
Yana fadar hakan ya kai hannu ya bude kofar falon ya fice ba tare da ya kara cewa komai ba.
“Zain kana son ganin laifin Farhat Wallahi to idan bata bude mata ta fita ba ya zata mata”
Ta fada cikin yanayin damuwa, sannan ta nufi bedroom dinta Amal na biye da ita a baya, Ali da Muhammad kuma suka nufi kitchen dan neman abunda zasu ci.
Ya samu kansa cikin yanayin damuwa sosai, yasan ko ya kansa a neman yarinyar nan be san inda zai ganta ba. Wani haushin Farhat yaji ya karu a ransa, duk ita ya dorawa laifi, kamar marar lafiya haka ya isa Kanwurin Sarki, tun daga bakin babban gate fadawa keta gaisheshi amman be kulasu ba har ya faka motarsa a babban kofar Mai Martaba, ya dade zaune cikin motar sannan ya bude ya fito ya nufi babar hanyar da zata sadashi da fadar mai martaba, a iya saninsa Mai martaba na fada yanzu dan yana shiga fada a duk Monday a daidai wannan lokacin gashi kuma dazu ya fita be gaishe ba da dada, dan haka ya kamata a yanzu ya shiga ya gaishe shi kamin ya karasa sashen Dada, tun da ya hango kofar fadar a kunne abun ya bashi mamaki, kawar da kwankwanto yasa ya kai hannu ya taba kofar fadar, sai ya samu kofar a kulle, hakan ya sashi fitowa gaba daya ya dawo ya zagaya ya mike doguwar hanyar da zata sadashi da cikin gidan.
Duk gaisuwar da ake masa be ji ba saboda hankalinsa baya gurin, ko da ma yana gurin ba zai amsa ba dan be saba amsa gaisuwarsu ba. Tsakar gidan katon tsakar gidane mai cike da shuke shuken fulawoyi, an kawata jikin ginin da fanti fari sai aka kawatar tsakiyar da fenti golden mai haske da sheki, kowa da part dinsa gate ya raba su, daga gefen gate dinsu akwai wani gate na bayi da ma'aikatan gidan, daga bangaren hagu kuma akwai sashen da ake dafa abincin gidan na kowa da kowa, dama da kau kuma babban hanya ce da zata sadaka da sashen mai martaba.
Bangare Hajiya Hadiza ya fara shiga katsancewar ita ce uwargidan mai Martaba, Sisters din ya tarar a cikin falon, cikin girmamawa da mutumci suka gaisheshi, be amsa musu ba kasancewar daya bayan daya suke gaisheshi, sai kawai ya ce
“Ina Hajiya?”
“Bata nan sun fita tare da Mama da kuma Dada Yalwa da Mai Martaba”
Rafila ta amsa masa
“Gurin me?”
“Gurin gaisuwa, wani kauye wai Yayan Hajiya dake sarautar garin aka kashe”
Juyawa kawai yai ya fice, hannayensa zube cikin aljihu, yana takawa a hankali har ya fita daga sashen gaba daya, part dinsa ya nufa kai tsaye yana ciro wayarsa dake ringing a aljihu, yai parking ya kara a kunne amman ya kasa magana kamar ba babban abokinsa ne ya kira shi ba.
“Zain kasa muna da tiyata uku da rabi fa kuma ka fita yanzu”
Sauke wayar yai a kunnesa ya katse kiran, a duniya ya tsani a tuna masa abu, ko da kuwa ya manta din ne balle kuma ba kasafai yake yawan mantawa da abubuwa. Keys yasa ya bude kofarsa, idan zai fita baya rufe janyowa kawai yake amman idan ya dawo sai ya bude da keys. Yana saka kafarsa cikin falon wani dadadden kamshi ya daki hancinsa, abun mamaki an gyara komai na falon an cire hotunan matarsa.
Dada ce kawai take da keys din part dinsa, idan ma za a masa gyara a hannunta ake karbar keys a bude dakin, bacin ran dake cikin ransa ne ya karu, har ya soma jin numfashinsa na taushewa.
Freezer ya nufa ya bude ya dauko gorar ruwa ya bude marfin ya kafa gorar a baki be sauke ba sai da ya shanye ruwan cikin gaba daya, sannan ya rufeta ya nufi kitchen ya jefata a kwandon shara.
Miyasa Dada Yalwa zata masa haka? Saboda yai fada da Hameeda ko kuma saboda yau fita be gaisheta ba? Ko kuma tana nunanin ganin hoton Haleema ne ke sakashi yin fada da Hameeda.
“Ban ga dalilin da zaisa ki dauke min hoton Mata ba Dada”
Ya fada a haka kamar mai rada, kana ya sauke ajiyar zuciya kallon windows kitchen din. Ya dade a tsaye kamar sannan ya juyo ya nufo bedroom yana cire yellow T-shirt din dake jikinsa, sannan ya daurawa tawul ya shiga wanka. Be wani dade ba ya fito ya shirya cikin wasu kananan kayan ya fito da sauri dan lokacin shiga tiyarsu ya kusa.
Be shiga wata motar ya shiga wacce ke part dinsa ba wacan ta dazu ba, a gagauce ya fita daga gidan, ko kadan baya son saba dokar aikinsa, yakan kiyayen duk abunda ya shafi aikinsa saboda yasan muhimmancinsa. 3:20 ya isa asibitin, a gurin sa aka tanada ma manyan likitoci su aje motocinsu ya faka motarsa. Sannan ya fito ya nufi cikin asibitin.
“Allah ya taimaki Doctor”
Wani mutun dake fitowa daga Emergency ya fada yana masa irin gaisuwar nan ta girmamawa. Sai a lokacin hankalin Zain ya kai gurinsa.
“Sadiq me kake a nan?”
Ya fada sanin mutumen da yai dan unguwarsu su Anty Ummi.
“Wallahi wata karamar yarinya wani mutum ya kade shine muka raka biyo mutumen nan saboda ba a san kowa nata ba”
“Ayyah Sorry Allah bata lafiya, zan shiga tiyata”
Ya fada yana kokarin wuce, dan hankalinsa gaba daya yanzu yana gun tiyatar da zasu shiga.
“Okay Allah yasa ayi a sa'a”
Ya fada cike da girmamawa.
FARHAT POV.
“Marar mutunci bulutu, ai daman na san ba so na kike ba tunda uwarki ma ba sona take ba, yanxu duk hallacin da Bashir yai miki ki rasa da abunda zaki saka masa sai wannan? Idan ma da gaske ne miyasa baki zo kin same da maganae ba, sai kije xan wani guri kina fadar sirrin gidana, daman haka kuke da Ummi shiyasa baki da gurin zuwa sai can ko?”
Faduwa tai zaune, idonta ya rufe ruf bata ganin komai saboda hawaye. Kalma daya ta Anty rukaiya bata shiga kunnenta bata ganin komai sai pre-wedding picture din Auwal da wannan yarinya.