← Book details Hafsatu Manga Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 93

Sashe 24

Hafsatu Manga Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Zain ka cika matsala Wallahi, matukar muna son Hafsat ta rike mana yarinyar nan dole ne mu fada mata gaskiya, beside baka da wani gurin kaita daya wuce can, kasan dai Anty Ummi tace ba zata karbeta ba, ba kuma zaka kaita gidanku ba, ina zaka kaita?”

Iskar dake bakinsa ya busar ya kalli Hafsatu manga wacce ta kwanta saman hannayenta.

“Zain, ina tunanin ya kamata ka amince da bukatar Anty Ummi”

“Ko da hakan na nufin na cutu? Kai ma ka zabi bangareta”

“This is not the right time to take anyone side, kawai ina baka shawara ne ga abunda nake ganin ya dace”

“Auren Farhat kamar salwantar da rayuwata ne Ibrahim and you know it”

“Ita bata salwantar da tata rayuwar akanka ba? Saboda kai aurenta a farin ya mutu? Saboda kai mijinta ya daketa har tai miscarriage, ka manta lokacin da Mai Martaba ya koreka ita ta dauki kaddarar zama da kai, a gabana ta furta cewar dan'uwanta yafi mata mijinta, ya fi mata yayanta kuma rayuwar dan'uwanta tafi mata rayuwar aurenta ko da hakan na nufin karshen rayuwarta ne, dukan abunda zai faranta maka rai Anty Ummi tana kokarin yinsa ko da kuwa ita zai bakanta mata maka rai ne, Anty Ummi da Hameeda su suka fi kowa baka gudummawa a lokacin da aka shiga takaninka da Mai Martaba ko ka manta hakan?

Zain kai da kanka kake fada min kana neman ranar da Anty Ummi zata bukaci wani muhimmin abu kai mata saboda ta san tana da kane kuma dan'uwan da zai iya share mata hawayenta, amman yau kai da kanka kake son zubar hawayenta....? Am totally confused”

Zain yayi saurin mikewa tsaye saboda hawayen da suka cika masa ido ya nufi window yana saka hannayensa aljihu.

“Idan na amince da auren Farhat, nai yaya da Hameeda?”

“Mai Martaba yafi son ka fiye da komai daya mallaka a duniyar nan, zai goya maka baya ka auri matar da kake so, kuma dole na Dada Yalwa da Hameeda su sakar maka marar yin fitsari, dole ne ka zama Namiji Zain, ko za a kada a raya karka yarda ya janye ra'ayinka akan aurenta matukar ka gabatar da ita a gurin Mai Martaba, aurenta saukeki ne a gareka Zain, zaka samu damar zama da Yarinyar nan a cikin gidanka...”

Shiru ne ya biyo baya dakin yai tsif kamar babu kowa a ciki. Zuwa can Zain ya juyo ya kalli Ibrahim.

“Ka tunatar da ni abunda be kamata na manta ba, zan yi komai saboda farincikin yar'uwata kuma uwata...”

Ya karasa yana girgiza kai, sai Ibrahim yai murmushi ya tashi yaje ya dafashi.

“Good, abu na biyu kuma ina son ka amince yarinyar nan ta zauna gurin Hafsat da zarar ka yi auren sai ka maidata hannunka”

Zain ya kalli Hafsatu manga data bata fuska garin lake kafada har munduwar hannunta ta fadi, dan Murmushi ya sakar mata yaje ya dauki munduwar ya kama hannunta zai saka mata sai ya tsaya kallon sunanta dake rubuce. H A F S A T aka rubuta a rarrabe, wani abun mamaki munduwar ta azurfa ce mai tsada irin azurfar nan da sai wane da wane ke sakawa idan ma ba wanda ya sani ba babu wanda zai banbanceta da zinari.

“Waya siya miki wannan abun hannun?”

Ta nuna sama.

“Babanki?”

Ta girgirza kai alamar a a.

“Mamanki?”

Ta gyada masa kai, kama hannun nata yai ya saka mata, fuskarsa da mamaki.

“Wannan azurfar mai tsada ce, anya yarinyar nan yar hudun hijira ce kuwa?”

“Alamunta ya nuna haka, itama kuma haka tace”

“Amman waya taba wannan zinarin haka mai sunanta?”

“Azurfa ce”

“Amman yayi kama da gold, mamanki mai kudi ce?”

Ibrahim ya karasa yana tambayarta, sai ta girgiza masa kai idonta na cika da kwalla.

“Tace mun mahaifiyarta mahaukaciya”

“Amman.... ”

Zain ya daga masa hannu.

“Karka takura mata dan Allah, bata da bakin amsa tambayoyinka a yanzu”

Sai ya kama duka hannayenta biyu ya hada guri daya ya rike yana mata murmushi.

“Mama Doc zata tafi da ke gidansu ki zauna na wani lokaci kamin Anty Ummi ta yarda ki zauna gurinta”

Ta lake kafada tana hawaye, alamar bata yarda ba ita ba zata zauna ba.

“Zata kula da ke sosai kuma duk abunda kike so zata miki, kuma kullum zan dinga zuwa ina dubaki, zan siya miki duk abunda kike so”

Ta kara bata fuska tana ta hawayen dole. Hakan yasa Zain jin babu dadi.

“Kina son madara da nama?”

Ta gyada kai da sauri.

“To zan dinga siya miki kinji?”

Ta sake gyada kai, sai yasa dayan hannunsa ya share mata hawayenta, sannan ya mike tsaye ya kalli Ibrahim.

“Ka fada mata bata bachi ita kadai saboda tana tsoro, kuma idan zata kwanta ana mata addu'a, sannan k tambayeta nawa za a rika biyanta every month or week”

“Wow...”

Cewar Ibrahim yana dariya. Zain be kula shi ba ya fice hannayensa zube a aljihu.

Misalin uku da rabi ya tashi aiki kai tsaye gidan Anty Ummi ya wuce, cikin kuzari ya tura kofar falonsa ya shiga zuciyarsa na mugun bugawa kamar zata fito. Yana shigowa ta juyo ta kalleshi fuskarta da murmushi tana kokarin cire hijabin da ke jikinta.

“Yau kuma an tuna damu dirar rana aka mana”

“Na dauka fushi kike da ni”

Ya fada, bayan ya zauna saman kujera. Sai tai murmushi ta soma nade hijabin tana cewa.

“Akwai wata rana da muka yi fada da kai saboda littafin makarantana da ka yaga, sai na dauki fushi da kai bana maka magana, da Mama ta lura da hakan sai ta kirani ta umarceni da na kama hannunka, sai na kama na rike cikin fushi, sai tace saki fuskarki Amina, karki sake fushi da dan'uwanki komai zai miki kiyi hakuri shi yaro ne, wata rana kuma ke uwarsa ce kinga uwa ai bata fushi da danta, ina son ki so dan'uwanki fiye da komai a duniyar nan, baki samu komai a ko wane lokaci amman ban da mahaifiya da mahaifi da kuma yan'uwa, kuma babu wani abu mai maye gurbinsu har abada!

A lokacin ina da shekara goma, amman Allah ya bani hankalin da ban sake fushi da kai ba, komai zaka min zan kyaleka ko da raina ya bace, idan kuma naga wanda zai taba ka sai inda karfina ya kare, akan wannan turbar nake har yau, ban yi fushi da kai kana karaminka ba ba zan taba fushi da kai yanzu da girmanka ba, ko da nayi fushi da kai na dan lokaci ne idan shaidan ya ribance ni amman ba mai dorewa ba”

Ta kai hannu ta share hawayen idonta, sannan ta tashi tsaye ta nufi hanyar bedroom dinta tana fadin.

“Yau ban je aiki ba, kauye naje kuma ban samu na girka abinci ba, ka hada wani abun ka sha kamin na dora girki”

Tashi Zain yai tsaye ya saka hannayensa aljihu ya ce.

“Idan har auren Farhat na nufin farincikinki na shirya aurenta.... Zan kuma koyi hakurin zama da ita daga yanzu...”

Da sauri Anty Ummi ta juyo ta kalleshi.

[2/26, 10:39 AM] Ayusher P: *HAFSATU MANGA*
_Yarinyar Kauye_

Wattpad @KhadeejaCandy

1⃣9⃣

Misalin goma na safe ya fito daga sasshensa, yau kam yayi bachin safe wanda a manta rabon da yayi irinsa saboda jinyar Hafsatu da yake. Part din Dada ya nufa, yau kam ya tararda Hameeda ita kadai na zaune falon Dada tana karyawa.

“Ina kwana?”

Ta gaisheshi muryarta na rawa, ba tare da ta bari sun hada ido ba. Be amsa ba be kuma fasa kallonta ba har ya zauna kusa da ita kasancewar ita tana kasa ne shi kuma yana saman cushion.

“Akwai wani abun da kike son mu tattauna ne?”

Ta dago idonta ta kalleshi sai kuma ta sauke.

“Aa ba komai”

“Feel free ki fada min abunda yake damunki, zan saurareki”

“Kamar da?”

Ta tambaya idonta narau-narau. Shiru yai kamar ba zai ce komai ba.

“Fiye da da”

Zata sake wata maganar sai ga Dada ta fito daga bedroom dinta sanye da wani tsadadden lace.

“Kai Amaryata kin fito fes...”

“Kasan fa kai dana ne ba jika ba”

Ta fada tana murmushin kasaita.

“Aa yau dai bangaren jika na dauka, ki bar da sai idan nayi laifi, ko da yake na kusa yinsa tun da kishiya zan miki kwanan”

Dam gaban Hameeda ya fadi, zuciyarta nata raya mata ita ce. Dada ta bude baki.

“Kai kai wace mai dajara ce wannan?”

“Wata kyakkyawar yarinya ce kama da indiyawa”

“Ciki ko wajen masarautar nan?”

“Bata da alaka da masarautar nan, amman dai mai tarbiya ce”

A take murmushi da annashuwar dake fuskar Dada ya gushe, ta murtuke fuska kamar an aiko mata da mutuwa.

“Tarbiya bata burge mu, domin cikinta muke kuma munyi gadonta, ko da wasa be kamata ka tsallake marautar nan ka dauko wata ba, ba zaka burgemu ba, mai martaba da ni ba zamu lamunta ba, ba zamu yarda ka kawo mana bare ba...”

Hameeda ta hade yawun bakinta da suka mata daci ta tari numfashin Dada.

“Ko da baren nan ita ce silar farincikinsa? Kuma ita yake so kamar ransa? Haba Dada tun yaushe kuke jiran zuwan wannan ranar ranar da Yarima zai gabatar da wata mace a matsayin matar aurensa?
Dada baki tunanin lokaci yayi daya kamata a bar kowa yabi zabin ransa? Kar kankancinta ya dameki ke dai abunda kika sani wanda zai aurota mai daraja ne a gurinki, dan Allah dan girman Allah ku bar mu mu auri wadanda muke so”

Ta karasa tana hade hannayenta guri daya alamar roko. Zain was shocked irin yadda take defending dinsa. Dada was shocked too da abunda yake fitowa daga bakinta, ga kuma fuskarta na nuna gaskiyar rokon da take.

“Yaushe tarbiyarki ta lalace haka da har zaki iya daga baki ki fadi wannan maganar?”

“Auren biyu zan yi bana daya ba Dada, daga ni har ita muna da damar zaben abar da muke so ko da kuwa wajen masarautar nan ne, ke dai ce gatana a duniyar nan Dada idan kika tsaya min ko mai martaba ba zai musa ma bukatata ba, ke uwace a gareni shiyasa na kawo bukatata a gareni Dada ki taimaka ki zame min uwar da kike ikirari dan Allah”

Ya marairaice mata sosai kamar zai yi kuka..
Chapter 24 · 0% Book details