Sashe 23
Hafsatu Manga Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta tashi da sauri ta fice daga dakin. Hannu ya kai ya bude plate din da aka aje masa abinci sai kuma yaji ba zai iya ci ba, Hameeda ta tsaya masa a rai, zuciyarsa nata raya masa ita din abar tausayi dukan abunda ta fada gaskiya ne tana da bukatar wani kusa da ita, yasan yanayin gidansu sisters dinsa duk ji suke da kansu ko kuma ko wacce da mahaifiyarta a gidan, ita kadaice sai ragowar wadanda ake riko ne basa da iyaye a gidan, amman a waje suna da iyaye amman ita fa? Ba uwa ba uba, gashi ta tashi a hannun Dada bata saba da kowa ba sai shi da Dada da kuma Haleema duk da kasancewar ita Haleema ba a gidan take ba.
Sallamarsa ce tasa ya dago ya kalli kofar, wata tafiya take daidai hijab din dake jikinta na kokarin tadeta ta fadi kanta a kasa ta zauna kusa da Dada.
“Muhammad yace kanki na ciwo”
Dada ta fada tana shafa kanta cike da tausayinta da kuma kulawa.
“Ee ina son bachi ne”
“Aa idan Muhammad ba zai dubaki ba, sai a kira Doc Hashimu ya dubaki”
Sai Zain yai karaf yace.
“Na bata magani.”
Daga Dada har ita Hameeda din kallonsa suka yi, sai kuma Hameeda ta maida kanta kasa tana fadin
“Ee ya bani magani, shiyasa nake son na kwanta”
“To je ki kwanta Allah baki lafiya”
Sai da ta amsa da amin sannan ta tashi ta fice, Zain ya bita da kallo zuciyarsa nata raya masa abubuwa.
*** *** ***
Around 4pm Doc Hafsat ta isa gida tare da takwararta Hafsatu manga, da fari Hafsatu tai kafuwar kin shiga gidan har sai da Doc ta lallabata sannan ta yarda ta shiga shima dan ta rike rigar da Doc Hafsat take sanye da ita.
“Assalamu Alaikum ga bakuwa.... ”
Doc Hafsat na saka kafarta cikin falon ta fadi haka cike da annashuwa, daman ta sanar da su tun lokacin da Ibrahim ya sanar da ita. Sai Momy ta amsa mata da far'ah tana taba hannayenta.
“Lalle marhabun da bakuwar gidanmu.. Maraba da ke”
Dukansu fuskarsu a sake take, daga Momy har Auwal da kuma Sapna. Kusa da Yayanta Auwal Doc Hafsat ta zauna tana fadin.
“Amman fa bakuwar tsoron mutane take”
Auwal ya kai hannu zai rikata sai tai saurin shigewa jikin Hafsat, amman hakan be hanashi fisgota ba.
“Indai tsoron mutane kike kin shiga uku da ni, fada min inda na sanki dan ni nasan na taba ganin wannan fuskar”
Ya fada yana lasa hancinsa, buge masa hannu tai tana murguda masa baki.
“Really ashe dai kema yar duniya ce”
Sai duk suka sa dariya har Momy, ita kuma tai saurin rufe fuskarta wai taji kunya. Hannunsa yasa ya janye mata nata hannun daga fuskarta yana kokawar rabata da katon Hijab din dake jikinta, a dayan bangaren kuma yana ta kokarin tuna inda ya san fuskarta.
“I remember, ki ce na kade ranar nan, ga fuskarki nan, a lokacin ina sauri zanje aiki kuma na bi ta gidansu Farhat”
“Au ita ce?”
Cewar Momy.
“Yeah amman yau ta min kyau sosai kamar ba ita ba”
“Ai dole tai kyau Doc Zain fa yake kula da ita”
Hafsat ta fada tana dariya.
“Amman kin san shegen doctor nan ya sha da ni, assume as I'm ace kamarsa ya tsaya yana katsa min tsawa ban rama ba, i tot wani yayanta ne ko jininta that time i was very stupid da ban rama ba Wallahi”
“Kai dan sarki ne fa, kuma asibitinsa ce”
“Dan sarki? Like seriously? Ina ruwana da sarautarsa idan sarautar yake takama da ita mu kuma muna takama da kudi da kuma mulki, fada min akwai uban daya isa ya takani?”
“No amman Dsp ai komai da muhallinsa”
“Yeah amman ya shamace ni da yawa”
Sapna ta kalleshi
“Ni fa ban gane kan maganar ka ba”
Sai ya labarta musu abunda ya faru bayan ya kadeta, domin acan farko ya fada musu cewar ya kade wata amman be fada musu yadda abun ya faru ba.
“Wata kila kadewar da ka mata ne ya haddasa bata magana”
“What”
Ya fada yana kallon Doc Hafsat.
“Yes aiki aka mata a halshenta be fada min dalilin jumuwanta ba, amman baya rasa nasaba sa wannan kuma har yanzu bata magana idan tana son abu sai dai ta nuna, gashi ba a san inda kowa nata yake ba”
“Ayyah”
Momy ta fada cikin tausayawa. Auwal kuma ya kalli Hafsatu manga cike da tausayi ya aje Hijab din dake hannunsa sama kujera ya daga ta ya zaunar saman kafafunsa.
“Am sorry dear it wasn't intentionally”
Har ga Allah tausayinta duk ya rufe shi, musamman da yaji shine dalilin rashin maganarta.
FARHAT POV.
Kana ganin yadda take tafiya kasan dole aka mata, fuskarta kamar bakin hadari babu annuri ko kadan a tare da ita. Tana zuwa ta juya masa baya.
Shi kuma sai yai murmushi ya sauke hannayensa ya ce.
“Ki kwantar da hankalinki Farhat ni ba zan miki dole ba, ko can baya ni ban nemi a hada aurena da ke ba, iyayenki ne suka ga dacewar hakan shiyasa suka gabatar min da ke ni kuma ba zan iya musa musu ba saboda yarana suma ina son su samu farinciki”
Yayi Shiru tare da sauke ajiyar zuciya sai kuma ya cigaba.
“Na zo ne kawai dan na fada miki, ko kuma na baki shawara, idan akwai wanda kike so ki fito da shi kamin lokacin da aka dibar miki ya cika, no ba zan cilasta miki zama da ni ba, amman karya nake na ce bana son ki Farhat, son ki ne ya jani na kasa hakura har na kusa fadawa halaka, abunda ban aikata a waje ba nai unkurin aikata shi a cikin gidana, da ace na san da zuwan wannan ranar da ban furta wata kalma a gareki ba, kuma da nasan hakan zai yi silar mutuwar Rukaiya da ban furtata ba ko da kuwa hakan na nufin ajalina ne... Nayi nadamar abunda nai....”
Wani banza tsaki ta buga masa ta juyo ta dawo cikin gida ta barshi can waje.
[2/19, 9:48 PM] خديجة أبو بكر القلوي😍: *HAFSATU MANGA*
_Yarinyar Kauye_
Wattpad @KhadeejaCandy
1⃣7⃣
Kuka tai sosai har sai da Anty Ummi ta gaji da rarrashinta, sannan tai shiru idonta duk ya kumbura ya canja kala.
“Ina ciki matsala Anty sun kasa fahimtata, nayi nadamar fallasa sirrin nan da nai da ace ban yi haka ba da Anty Rukaiya tana nan a raye da basu cilasta min aurensa, da yanxu ina cikin garin gusau da zama, sai dai naji d abunda Auwal yai min...”
Cikin kuka take magabar, Anty Ummi jikinta duk yayi sanyi, ko Farhat bata fito fili ta fada mata ba, tasan da ita take da ace bata fadawa Anty Rukaiya ba da duk abun be kwabe kamar haka ba. Cikin rashin kuzari Anty Ummi ta kama hannunta ta rike.
“Farhat ki kaddara haka Allah yaso a gareki, maganar Bashir kuma ba zaki taba shiga hannunsa da sunan aure ba matukar yan'uwanki zasu yarda ki auri wani”
“Bani da wanda zan tsaida Anty, na kori kowa saboda Auwal shi kuma ya juya min baya ya canja min, bani da waya ma balle har na kira wani...”
“Baki bukatar kiran kowa Farhat matukar zasu aminta ki auri wani to Zain zai aureki...”
Cike da zarani da firgici ta kalli Anty Ummi baki sake.
“Yes na san baku jutuwa, amman bamu da wata mafita bayan wannan”
“Idan akwai wanda na tsana a duniyar nan kamar mutuwata Zain ne Anty kin sani, shima kuma ya tsaneni, wannan abun ba zai taba yiyuwa ba”
“Ke dai kike tsanenshi, amman shi yana kaunarki, kawai dai halayinki ne baya so wanda nasan shi ma a yanzu ya daina, domin sai da ya zubar da kwalla akan abunda ya sameki, shi ma da kansa yake cewa da ace zaki amince da ya aureki...”
Sanda kanta tai kasa ta hade yawun bakinta, ita kanta tasan wata karya da hankali zai dauka, wannan kam bata shiga ba.
“Bayan shi ba muda wata mafita Farhat, kunma ina ganin ya cancanta ki auri Zain ko dan alakar dake tsakaninmu, sannan kuma Auwal ya gane kuskuren da yai ta hanyar ganin kin aure wanda ya fishi komai, mulki kudi kyau da komai ma”
“Ba zan iya ba Anty ba zan iya auren dan'uwanki ba, nafi tsanarsa fiye da Ya Bashir, idan har na yarda na aureshi shima cutuwa zan yi”
“Ba zaki cutu b Farhat na miki alkawari, kuma indai har na isa dake na kai na rokeke abu kiyi min to ki amince da auren nan saboda da ni!”
Da sauri Farhat ta kalleta tana girgixa kai hawaye na cika idonta.
“Idan har baki amince da auren nan ba Farhat, ba zan sake zuwa garin nan ba, ba zan taba mantawa da wannan butulcin da kika min ba har abada, kuma na rabu da ke kenan!”
Anty Ummi na kaiwa nan ta tashi tsaye ta dauki jakarta tana fadin
“Gobe ko jibi zai zo ganinki idan kin ga dama karki fito, ko kuma ki fada masa baki sonsa sai nasan kin cika yar halak”
Juyawa tai ta fice Farhat ta bita da kallo baki sake tana hawaye.
YARIMA ZAIN POV.
Yana yin parking ya fito cikin bacin rai ya nufi Mr Zain rooms, sai da ya kai dakin da Hafsatu take sannan ya sauke ajiyar zuciya ya tura kofar ya shiga. Doc Hafsat ya samu tare da ita suna taba waya da alama game ta kunna mata ko kuma wani abun take nuna mata a ciki.
“Ina kwana, Doc Ibrahim ne ya kirani yace na zo naje da Hafsat yayi min bayanin komai, amman sai zuwa anjima idan zan wuce zanje da ita”
A tare ta jeru nasa bayanin, kai kawai ya daga mata ta karbi wayarta dake hannun Hafsatu manga ta fice. Kusa da ita ya zauna ba tare da ya kalleta ba ya fiddo wayarsa ya kira Ibrahim be yi picking ba ya shigo dakin hannunsa rike da wayar tana ringing.
“Miyasa zaka fada mata komai? Ce maka nai ka turo min ita?”
Ibrahim din be amsa masa ba be kuma daina murmushin da yake ba, sai da ya zauna.
Sallamarsa ce tasa ya dago ya kalli kofar, wata tafiya take daidai hijab din dake jikinta na kokarin tadeta ta fadi kanta a kasa ta zauna kusa da Dada.
“Muhammad yace kanki na ciwo”
Dada ta fada tana shafa kanta cike da tausayinta da kuma kulawa.
“Ee ina son bachi ne”
“Aa idan Muhammad ba zai dubaki ba, sai a kira Doc Hashimu ya dubaki”
Sai Zain yai karaf yace.
“Na bata magani.”
Daga Dada har ita Hameeda din kallonsa suka yi, sai kuma Hameeda ta maida kanta kasa tana fadin
“Ee ya bani magani, shiyasa nake son na kwanta”
“To je ki kwanta Allah baki lafiya”
Sai da ta amsa da amin sannan ta tashi ta fice, Zain ya bita da kallo zuciyarsa nata raya masa abubuwa.
*** *** ***
Around 4pm Doc Hafsat ta isa gida tare da takwararta Hafsatu manga, da fari Hafsatu tai kafuwar kin shiga gidan har sai da Doc ta lallabata sannan ta yarda ta shiga shima dan ta rike rigar da Doc Hafsat take sanye da ita.
“Assalamu Alaikum ga bakuwa.... ”
Doc Hafsat na saka kafarta cikin falon ta fadi haka cike da annashuwa, daman ta sanar da su tun lokacin da Ibrahim ya sanar da ita. Sai Momy ta amsa mata da far'ah tana taba hannayenta.
“Lalle marhabun da bakuwar gidanmu.. Maraba da ke”
Dukansu fuskarsu a sake take, daga Momy har Auwal da kuma Sapna. Kusa da Yayanta Auwal Doc Hafsat ta zauna tana fadin.
“Amman fa bakuwar tsoron mutane take”
Auwal ya kai hannu zai rikata sai tai saurin shigewa jikin Hafsat, amman hakan be hanashi fisgota ba.
“Indai tsoron mutane kike kin shiga uku da ni, fada min inda na sanki dan ni nasan na taba ganin wannan fuskar”
Ya fada yana lasa hancinsa, buge masa hannu tai tana murguda masa baki.
“Really ashe dai kema yar duniya ce”
Sai duk suka sa dariya har Momy, ita kuma tai saurin rufe fuskarta wai taji kunya. Hannunsa yasa ya janye mata nata hannun daga fuskarta yana kokawar rabata da katon Hijab din dake jikinta, a dayan bangaren kuma yana ta kokarin tuna inda ya san fuskarta.
“I remember, ki ce na kade ranar nan, ga fuskarki nan, a lokacin ina sauri zanje aiki kuma na bi ta gidansu Farhat”
“Au ita ce?”
Cewar Momy.
“Yeah amman yau ta min kyau sosai kamar ba ita ba”
“Ai dole tai kyau Doc Zain fa yake kula da ita”
Hafsat ta fada tana dariya.
“Amman kin san shegen doctor nan ya sha da ni, assume as I'm ace kamarsa ya tsaya yana katsa min tsawa ban rama ba, i tot wani yayanta ne ko jininta that time i was very stupid da ban rama ba Wallahi”
“Kai dan sarki ne fa, kuma asibitinsa ce”
“Dan sarki? Like seriously? Ina ruwana da sarautarsa idan sarautar yake takama da ita mu kuma muna takama da kudi da kuma mulki, fada min akwai uban daya isa ya takani?”
“No amman Dsp ai komai da muhallinsa”
“Yeah amman ya shamace ni da yawa”
Sapna ta kalleshi
“Ni fa ban gane kan maganar ka ba”
Sai ya labarta musu abunda ya faru bayan ya kadeta, domin acan farko ya fada musu cewar ya kade wata amman be fada musu yadda abun ya faru ba.
“Wata kila kadewar da ka mata ne ya haddasa bata magana”
“What”
Ya fada yana kallon Doc Hafsat.
“Yes aiki aka mata a halshenta be fada min dalilin jumuwanta ba, amman baya rasa nasaba sa wannan kuma har yanzu bata magana idan tana son abu sai dai ta nuna, gashi ba a san inda kowa nata yake ba”
“Ayyah”
Momy ta fada cikin tausayawa. Auwal kuma ya kalli Hafsatu manga cike da tausayi ya aje Hijab din dake hannunsa sama kujera ya daga ta ya zaunar saman kafafunsa.
“Am sorry dear it wasn't intentionally”
Har ga Allah tausayinta duk ya rufe shi, musamman da yaji shine dalilin rashin maganarta.
FARHAT POV.
Kana ganin yadda take tafiya kasan dole aka mata, fuskarta kamar bakin hadari babu annuri ko kadan a tare da ita. Tana zuwa ta juya masa baya.
Shi kuma sai yai murmushi ya sauke hannayensa ya ce.
“Ki kwantar da hankalinki Farhat ni ba zan miki dole ba, ko can baya ni ban nemi a hada aurena da ke ba, iyayenki ne suka ga dacewar hakan shiyasa suka gabatar min da ke ni kuma ba zan iya musa musu ba saboda yarana suma ina son su samu farinciki”
Yayi Shiru tare da sauke ajiyar zuciya sai kuma ya cigaba.
“Na zo ne kawai dan na fada miki, ko kuma na baki shawara, idan akwai wanda kike so ki fito da shi kamin lokacin da aka dibar miki ya cika, no ba zan cilasta miki zama da ni ba, amman karya nake na ce bana son ki Farhat, son ki ne ya jani na kasa hakura har na kusa fadawa halaka, abunda ban aikata a waje ba nai unkurin aikata shi a cikin gidana, da ace na san da zuwan wannan ranar da ban furta wata kalma a gareki ba, kuma da nasan hakan zai yi silar mutuwar Rukaiya da ban furtata ba ko da kuwa hakan na nufin ajalina ne... Nayi nadamar abunda nai....”
Wani banza tsaki ta buga masa ta juyo ta dawo cikin gida ta barshi can waje.
[2/19, 9:48 PM] خديجة أبو بكر القلوي😍: *HAFSATU MANGA*
_Yarinyar Kauye_
Wattpad @KhadeejaCandy
1⃣7⃣
Kuka tai sosai har sai da Anty Ummi ta gaji da rarrashinta, sannan tai shiru idonta duk ya kumbura ya canja kala.
“Ina ciki matsala Anty sun kasa fahimtata, nayi nadamar fallasa sirrin nan da nai da ace ban yi haka ba da Anty Rukaiya tana nan a raye da basu cilasta min aurensa, da yanxu ina cikin garin gusau da zama, sai dai naji d abunda Auwal yai min...”
Cikin kuka take magabar, Anty Ummi jikinta duk yayi sanyi, ko Farhat bata fito fili ta fada mata ba, tasan da ita take da ace bata fadawa Anty Rukaiya ba da duk abun be kwabe kamar haka ba. Cikin rashin kuzari Anty Ummi ta kama hannunta ta rike.
“Farhat ki kaddara haka Allah yaso a gareki, maganar Bashir kuma ba zaki taba shiga hannunsa da sunan aure ba matukar yan'uwanki zasu yarda ki auri wani”
“Bani da wanda zan tsaida Anty, na kori kowa saboda Auwal shi kuma ya juya min baya ya canja min, bani da waya ma balle har na kira wani...”
“Baki bukatar kiran kowa Farhat matukar zasu aminta ki auri wani to Zain zai aureki...”
Cike da zarani da firgici ta kalli Anty Ummi baki sake.
“Yes na san baku jutuwa, amman bamu da wata mafita bayan wannan”
“Idan akwai wanda na tsana a duniyar nan kamar mutuwata Zain ne Anty kin sani, shima kuma ya tsaneni, wannan abun ba zai taba yiyuwa ba”
“Ke dai kike tsanenshi, amman shi yana kaunarki, kawai dai halayinki ne baya so wanda nasan shi ma a yanzu ya daina, domin sai da ya zubar da kwalla akan abunda ya sameki, shi ma da kansa yake cewa da ace zaki amince da ya aureki...”
Sanda kanta tai kasa ta hade yawun bakinta, ita kanta tasan wata karya da hankali zai dauka, wannan kam bata shiga ba.
“Bayan shi ba muda wata mafita Farhat, kunma ina ganin ya cancanta ki auri Zain ko dan alakar dake tsakaninmu, sannan kuma Auwal ya gane kuskuren da yai ta hanyar ganin kin aure wanda ya fishi komai, mulki kudi kyau da komai ma”
“Ba zan iya ba Anty ba zan iya auren dan'uwanki ba, nafi tsanarsa fiye da Ya Bashir, idan har na yarda na aureshi shima cutuwa zan yi”
“Ba zaki cutu b Farhat na miki alkawari, kuma indai har na isa dake na kai na rokeke abu kiyi min to ki amince da auren nan saboda da ni!”
Da sauri Farhat ta kalleta tana girgixa kai hawaye na cika idonta.
“Idan har baki amince da auren nan ba Farhat, ba zan sake zuwa garin nan ba, ba zan taba mantawa da wannan butulcin da kika min ba har abada, kuma na rabu da ke kenan!”
Anty Ummi na kaiwa nan ta tashi tsaye ta dauki jakarta tana fadin
“Gobe ko jibi zai zo ganinki idan kin ga dama karki fito, ko kuma ki fada masa baki sonsa sai nasan kin cika yar halak”
Juyawa tai ta fice Farhat ta bita da kallo baki sake tana hawaye.
YARIMA ZAIN POV.
Yana yin parking ya fito cikin bacin rai ya nufi Mr Zain rooms, sai da ya kai dakin da Hafsatu take sannan ya sauke ajiyar zuciya ya tura kofar ya shiga. Doc Hafsat ya samu tare da ita suna taba waya da alama game ta kunna mata ko kuma wani abun take nuna mata a ciki.
“Ina kwana, Doc Ibrahim ne ya kirani yace na zo naje da Hafsat yayi min bayanin komai, amman sai zuwa anjima idan zan wuce zanje da ita”
A tare ta jeru nasa bayanin, kai kawai ya daga mata ta karbi wayarta dake hannun Hafsatu manga ta fice. Kusa da ita ya zauna ba tare da ya kalleta ba ya fiddo wayarsa ya kira Ibrahim be yi picking ba ya shigo dakin hannunsa rike da wayar tana ringing.
“Miyasa zaka fada mata komai? Ce maka nai ka turo min ita?”
Ibrahim din be amsa masa ba be kuma daina murmushin da yake ba, sai da ya zauna.