← Book details Abokin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 120 OF 177

Sashe 120

Abokin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Khadeeja Candy* Page 5 Emily ya hade wani kunci daya tokare zuciyarta. "Kin yi gaskiya, ban san darajar iyaye ba" Ta juya ta kalli Mama Barakat. "Kin gani ko? Yarki tana ganin na zafafa, dan Allah bana son na sake fadar wata magana ina girmama mutuncinki ki fita dan Allah karki sake dawowa" Jikin Mama Barakat ya kara yin sanyi. "Me kika sani game da uwa?" Ta juyar da idonta ta wani bangare na dakin tana sosa wani kurji da ya dade yana mata kaikayi. "Ban san komai ba, saboda tarihin rayuwata be taba wanzuwa da uwa ko uba ba, na tashi ba tare da uwa, uba ko. Yan'uwa ba, dan haka ban san dadin uwa ba sai rashin dadinta, ban san komai game da uwa ba domin tawa uwar bata taba rumguma ta ba, taba nuna min tarbiya ko akasinta ba, bata banbance min yadda zan yi rayuwa da mutane ba, shiyasa ban iya rike halshe ba, ban san zafin da ake ji idan an ci ma uwa mutuncin ba, amman ni ina fatan yata zata sani, domin na tsaya kanta, na iya yadda zan iya na rayu saboda ita, na yi ma kaina alkawari ba zan taba bari ta ji abun da na ji ba, ba zan bari ta yi irin rayuwar da na yi ba, zan hade duk wani bakinciki saboda ta yi farinciki" Ta juyo ta kalli Mama Barakat idonta na zubar da hawaye. "Dan Allah ki tafi bana son na sake fadar wata magana marar dadi a gareki" Mama Barakat ta nufi kofa ta bude ta fice tana zubar da hawayen da suka fi na Emily zafi da kuna a zuci, Hakima na binta a baya. Emily ta daga kanta sama ta shanye hawayenta sannan ta sauke ta shiga bandaki ta yi wanka ta fito ta zauna gaban madubi ta shafa mai ta saka turare kasancewar babu wasu kayan kwaliya ya saka ta lakaci man shafi ta shafa a lebenta ta shace kanta. Wandon balazo da rigarsa da Ummi ta bata ta dauka ta saka blue ne mai wani zane zanen baki sai rigarsa ta yadi baki da karamin dankwali baki, da dankwalin da daure gashinta madadin ribbons sannan ta dauki wayarta ta tsaya gaban madubi ta kalli kanta with full confidence. Ta yi kyau babu karya, tabon dukan da Vito yayi mata ya bace confidence din data sakawa kanta ya kara mata kyau da kwarjini, bakin data shafawa mai sai shinning yake, ta juya ta nufi inda talkaminta suke ta saka ta bude dakin ta fita, ta sauko falon a daidai lokacin da Ummi ta zauna a kujerar dake facing din ta Mama Barakat tana fadin. "Ki yi hakuri fa na barki a nan, na tsaya sallamar mai gida da abun karyawa ne" "Ba komai, wata magana nake son mu yi dake ta fahimta, na kira Aliyu jiya ba daga ba, wata kil yana tunanin ko saboda Kameela ne..." Mama Barakat bata karasa ba saboda saukowa Emily, daga Ummi har ita kallon Emily suke. "Na ce Nafisa ta kawo miki abun karyawa ta kawo?" Kamin Emily ta amsa tambayar Ummi Mama Barakat ta ce. "Na zo mata da abinci amman bata ci ba" Ummi ta kalleta da mamaki. "Abinci kuma? Abinci aka ce mun rasa a gidan ne da har sai an dauko daga gidanki an kawo?" "Aa na yi nufin kyautatawa ne kawai" "Gaskiya karki sake Hajiya Barakat kin ga dai daga bangaren Kameela kike, duk abun da ya faru ya faru saboda Emily kar a zo a cutartar da ita ba tare da mun sani ba" Mama Barakat na yi shiru ta sauke kai kasa, Emily ta kalli Ummi ta ce. "Ina son zan tafi gidansu Turhan ko zaki iya sakawa a kai ni?" Ummi ta kalleta cike da mamaki. "Gidansu Turhan?" Emily ta daga kai, Mama Barakat ta kalleta, Ummi was speechless for a little bit kamin ta ce. "Lafiya?" "Ummi yata tana can, zan je na yi magana da su ne" "Zazzzaki iya?" Ta daga kai with full confidence. "Amman ki bari ki yi breakfast tukuna" "Hankali ba zai kwanta ba har sai na tafi, idan na dawo zan karya" "Okay, bari na yi ma direba kwatacen gurin, ina zuwa" Ummi ta tashi rike da wayarta ta fita. "Zaki iya zuwa ke kadai ko na raka ki? Kuma tafiyarki ba zata zama da matsala ba?" Emily ta kalli Mama Barakat ya wacce ta yi maganar ta gafen ido. "Na saba rayuwa da yin abubuwa ni kadai wannan ma zan iya" Ta nufi kofa ya bude ta fita, a Entrance din ta tsaya tana sauraren Ummi dake fadawa direban inda zai kai Emily. "Number gidan dai na manta, bari na tambayi Aliyu" Ta daga wayarta a gurin ta kira Aliyu ta tambaye shi house number nawa ne gidansu Turhan, sai da ya fada mata sannan ya bukacin jin dalilin tambayar. "Za mu yi magana daga baya" Ummi ta kashe wayar ta kalli direban. "Number 7" "Tohm Hajiya" Ya juya ya sauka ya nufi wata farar mota sai da ya juyo da ita sannan ta sauka ta nufi motar ta bude gidan baya ta shiga ta zauna, direba ya dauki hanya. TURHAN POV. Be yi nisa da gida ba kiran mahaifinsa ya shigo min wayarsa direct international call from Sudan to Nigeria, cikin hanzari yayi fakin yana dan jin faduwar gaba, domin abu ne mai wahala mahaifinsa ya kira shi, idan ma wani abu ne yawanci sai dai ya bar masa sako ta whatsapp ko kuma ya sanar yace a sanar masa. Ya amsa kiran cikin ladabi mahaifin nasa be ko tsaya gaisuwa ba ya gabatar masa da dalilin kiransa. "Wani labari na ji yanzu akanka.... kuma ina fatan ba gaskiya ba ne" Ya fada da yalshen larabci, Turhan ma ya mayar masa da yaren da suka fi fahimta. "Wane labari ne?" Mahaifin yayi shiru ma tsawon lokaci. "Cewar kana da ya da wata mata da ban sani ba?" Turhan ya ji gabansa ya fadi, amman hakan be hana amsawa mahaifinsa ba. "Eh gaskiya ne, amman ni ma ban san da yar ba sai a yanzu, tana tare da ni yanzu haka" "Hmmmmmm... Shiyasa na samu kira cewar mu iyaye ya kamata mu tsawatar saboda a bawa kowa hakkinsa, taya abubuwa suka faru haka ban sani ba?" Cikin isa da isa da kasaita yake maganar kuma cike da zafin ran dake bayyana bacin ransa. Turhan zai yi magana ya kashe wayar sai ya maida masa kira be daga ba. Babu tantama ya san mahaifinsa yayi fushi, sai dai fushinsa ba zai hana shi bayyana gaskiyar komai a yanzu ba, ya san zai fuskanci kalubale daga gurin mahaifinsa da kuma matarsa amman ya shiryawa hakan, kuma ko za aje sama a dawo na zai saki Emily ba saboda yarsa da kuma lokarin gyara abun da ya bata, and of course Emily ta cancanci zama matarsa. Juya motar yayi ya dauki hanyar gida, ya faka harabar gidan ya fito motar zuciyarsa da kansa cike da tarin abubuwa da suke kokarin rinchabe masa, amman dai yana jin zai iya dauka ko dan bawa marasa a kunya.. Ya tura kofar falon ya shiga, sai ya hango Ammy a inda ya barta zaune a dinning tana karyawa. "Ammy Ina Fatima?" Ita ya fara tambaya domin tabbatar tana gidan ko aa what if bayan fitarsa an fita da ita and the way da ya ga Mahaifiyarsa ta dauki zafi akan Emily tsab zata iya damka mata ita ba tare da saninsa ba. Ammy ta kalli Stairs as her response, wani Sighs of relief yayi sannan ya sake kallonta ya ce. "Ammy ke kika kira Mai Martaba kika nemi ya tsawarta saboda bawa kowa hakkinsa?" Ammy ta maa kallon rashin fahimta da kuma mamaki. "Ko da mafarki kar zuciyarka ta raya maka zan iya daga waya na kira mahaifinka balle har na nemi ya shiga cikin wani lamari da ya shafe ni, ka tofar da wannan yawun, bana son shi...!!!" Ya fara takawa zai karasa inda take yana mata bayanin kiran da aka masa, aka turo kofar falon sai ya juya Ammy ma ta kalli kofar dukansu suka yi arba da Emily fuska babu annuri, juyowa Turhan yayi yana kallon Confidence din dake tare da ita wanda ya kara mata kyau da haiba, babu murmushi ko alamarsa a fuskarta amman haka be hana goga fahimtar kyaun surar da Allah ya tsaga a fuskarta da sigar jikinta ba, ga tufafin sun karbe a color kuma sun mata cif in size domin palazon irin wannan ne mai matsewa a sama ya bude a kasa. Emily ta taka ta shiga cikin falon tana wani taku dake nuna ta shiryawa duk wani hargitsu na su. Ba shiri Ammy ta mike tsaye tana kallonta sai kuma murmushi ya cika fuskarta. "Aisha kin zo? Yau kin tuna gida?" "Eh na zo na tabbatar da abun da kika min alkawari, kuma na tafi da yata" Turhan ya maida hannayensa baya ya cira kafa daga ya fara takawa har ya isa inda take tsaye ya tsaya gabanta, yana wani sham kamshi. "Wannan ba Aisha da muka sani ba ce, me yasa kika bari suka cusa miki wannan tunanin da wannan rayuwar a zuciya?" Emily ta kara ta ku biyu forward. "Sautin murya nake ji, amman bana ganin mai magana, saboda mai maganar ba mutum ba ne, kusa ce da fatar akuya" Turhan ya kalli bakinta dake motsi yana kyalli da man data shafa masa, ya hade yawu a hankali, kamin ya kalli kwayar idonta mai matukar daukar hankali. "Na yi kuskure, na bata abubuwa da yawa, amman yanzu lokaci ne da zan gyara, kina da damar ki tsane ni ko ki aiwatar da duk abun da kike so a kaina, amman Please ban da zancen rabuwa" "Kana da karfin hali, har a yanzu umarnin kake ba ni? To wacan Aisha ta mutu, wacan Aisha ita ce kaza, ni kuma Zabuwa ce fira nake, ban zo nan dan na yi musayar kalamai ga wanda be san mutunci kansa da na mahaifiyarsa ba, So...." Ta kauce gabansa ta nufi gurin da Ammy take tsaye tana kallonta rai a bace. "Taya kika sauya Haka Aisha tun daga kan sutura da hali da addini ba wanda muka san ki da shi
Chapter 120 · 0% Book details