Sashe 92
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
jin haka Jamal ya sanar da Papy wacce yake so domin a haďe auren gaba ďaya,
Farin ciki a gurin Anty Reemah ba'a cewa komai domin Allah ya gama mata komai,
ta samu nagartattun surukai wadanda zatayi alfahari dasu...
*(wannan shine result of kyakykyawar zuciya)*
********
Tun ana saura sati ďaya biki Maleekah da kawayenta suka fara shagalin biki,
abinka da yar drama,
babu inda labarin aurenta bai zaga ba,
daga mai kushe Hilal saboda bai kamo kafar samarinta a haďuwa ba, sai mai yabawa zarrarshi na samun Maleeka da maza kewa rububi,
babu wanda yasan abinda Allah ya ganar dasu ya sanyasu suke kaunar junansu sai su biyun da kuma wanda yasan waye *Hilal Kangiwa....*
*******
"Ya kira wayarta yafi a kirga bata ďaga ba,
tun yana kira cikin marmari har ranshi ya baci ya ajiye wayar a gefe,
duk yaji ringing sai ya dauka itace yayi saurin daukar wayar,
in yaga ba ita bace sai ya ajiye wayar ya saki tsaki,
rabon da ya sata a idonshi tun shekaranjiya da suka tafi Egypt yin wani bikin a can..
bai san fushi takeyi na kin binta da yayi,
taso su tafi bikin tare yaki, dan ya fi son yayi zamanshi yayi hidimarshi cikin yan uwanshi...
Karfe Sha ďaya ya kira layinta na Egypt yaji shi a kashe,
hakan ya tabbatar mishi da yanzu ta shigo tunda jibi ne daurin auren,
Shiryawa yayi cikin kananan kayan sanyi masu taushin gaske,
yana matukar missing dinta dan ta koyar dashi soyayyarta mai sanyi,
gashi bai iya soyayya ba dan in yana yinta gaba daya zuciyarshi yake sallamarwa wanda yake so...
Saida ya biya ta wani gift shop ya siyo mata wani abu dan yaji dadin bata hakuri...
A kofar gida ya sameta tare da kawayenta tana musu sallama,
cikin shigar da yake matukar so ya sameta, jallabiya har kasa da gyalenta,
Cikin gidan ya shigar da motarshi ya fito ya tsaya haďe da harďe hannu yana jiran dawowarta,
Minti biyu kaďai ta kara tazo tana shirin wucewa ciki,
kallo ya bita dashi har ta kusa yi mishi nisa,
"A wife is angry wit her Hubbi!!, ya faďi cikin wata irin muryar da baisan yana da ita ba,
Duk da taji sanyin jin muryarshi da kuma sunan da ya kirata dashi hakan bai sa ta tsaya ba,
“Getting angry doesn’t solve problems,
"Ana Aseef “ya Radhi’a”
plss don't be mad at me...
Ajiyar zuciya tayi haďe da tsayawa zuciyarta na maimaita kalmar
*Radhi'a*
duk wani bacin rai da ta kunsa na tunanin Hilal baya sonta kamar yadda take sonshi ta kaudashi,
Sanyin dake kadawa a garin ya haďu da wanda ke kaďuwa cikin zuciyarta ya sanyata cikin wani irin yanayin da takeji tamkar su biyu kadai Allah ya halitta a duniya,
"plss my love, ya faďi cikin raďa a saitin kunnenta,
Lumshe idanuwansu sukayi a tare saboda qamshin da kowannensu ya shaka na juna,
a hankali ta juyo ta fuskance shi haďe da shagwabe fuska,
yadda ta turo baki yasan magana ce zata biyo baya,
Cikin sauri ya fiddo wata red flower dake makale a bayan wandonshi,
Saitin hancinta ya sata haďe da furta mata wasu rikitattun kalmomin da baisan ranar da ya iya su ba,
Shidai yasan ya horu matuka da rashin jin muryar dake kwantar mishi da hankali,
sannan idanuwanshi sunyi matukar kewarta,
tayi matukar sabar mishi da kaunarta mai sanyin dadi,
a halin da yake ciki yanzu baya jin zai iya koda yini ne ba tare da ganinta ba,
"Ikon Allah kenan,
shi yakan sanya so a lokacin da yaso,
Ko a cikin mafarkinshi bai taba tunanin zai iya samarwa wata mace gurbi a zuciyarshi ba, bayan wacce ya kira da mamallakiyar Qalbinshi,
*Zuciyar gaba daya*..
Sai gashi cikin kankanin lokaci soyayyar Maleekah na neman shafe babin dake adane da boyayyar soyayyar da tun yarinta yake dakonta,
Wasu lokutan in ya zauna yana tunani sai ya alakanta abun da cewar saboda ita din jinin Nadeeyah ce,
sai yanzu ne da ta hora shi na ďan kwanaki ya tabbatar wa kanshi irin kaunar da yake mata...
"Fushin masoya hutu,
cikin kankanin lokaci Maleekah ta manta komai ta saki jiki suka sha soyayyarsu wacce armashinta yafi na baya saboda amintar dukkan zuciyoyin biyu..
Sai da dare ya tsala sosai sannan Hilal ya rakata har cikin parlo ya juya ya tafi cike da kewarta....
Maleekah is very nice,
halayyarta da kyakykyawar zuciya irin ta Mahaifinta shi ya kara mata matsayi a zuciyar Hilal...
Har ya kai gida bai bar tunaninta ba,
koda yayi parking mota saida ya dan jima cikin motar sannan ya fito fuskar nan cike da annashuwa,
ta steps yabi zuwa sama,
duk inda yazo wucewa sai an mishi congrat harda masu bashi gift din aure,
"Al'adar larabawa da yan Nigerian dake cikin estate din kenan,
musulmi da arne in abun farin ciki ko bakin ciki ya sameka to fa tare za'a raba jajen da farin cikin,
wayewarsu tasa suka dauki juna tamkar jini ďaya...
Yana karasawa kofar flat dinsu ya soma jiyo hira da shewa cikin parlon kasa,
hakan ne ya bashi tabbacin yan uwa sunzo,
farin cikin da yake ciki ya mantar dashi miskilin halinshi,
nan ya murda kofar da sauri yagansu cike da parlon yan kangiwa da su Mummy,
Cike da farin ciki ya karaso ya dauki Fadeel ya jefa shi sama,
Sannunku da zuwa,
kun sha hanya,
gefen da Goggo ke zaune tana karkaďa kafa ya kalla yace "Harda su Goggo,
Lallai yau muna da manyan baki,
bata kalli inda yake ba ta cigaba da kaďa kafa tana sakucen hakori,
"Tunda ta shigo gidan taga hoton Maleekah shikenan farin cikin da ta guntso ya tafi,
da fari ta fara masifa akan duk matan duniya ya rasa wacce zai auro sai mai zubin karuwai,
saida Mummy tayi tsaye akanta sannan ta maida hankalinta ta zauna a gefe tana cika tana batsewa..
"Ina Anty Rally, ya tambaya yana duban mahaifiyarshi,
"Suna sama da su Raudha,
wani aiki suke ma Hinad,
Musaddiq na ďaki tun dazu yake jiranka,
Hanyar saman ya nufa da sauri cike da farin ciki,
yasan zaman su Mummy a parlon ne ya hanashi zama ayi hira dashi...
"Hey Mr Soft,
kana ina ne?
Kafin Musaddiq ya bashi amsa ya karaso balcony din inda Musaddiq ke tsaye yana duban sararin samaniya,
Jingina yayi jikin karfen yanda zasu fuskanci juna,
"how r u Kyari?
Gyaďa kai Musaddiq yayi fuskarshi dauke da Murmushin da yafi kama da na ciwo,
ganin Hilal ne ya sanya zuciyarshi karyewa har murmushin ya fito,
A ko da yaushe in ya kasance shi kaďai yana jin sam rayuwarshi bata da amfani,
Ya kasa daukar hakurin mantawa da ita,
ita din mace ce da take da wuyar mantawa,
rayuwa yinta kawai saboda mahaifinshi da kuma Hilal,
amma yasan tabbas zuciyarshi na gab da bugawa dan ya kasa yin rayuwa mai dadi babu ita...
Gyara tsayuwa Hilal yayi cike da damuwar yanayin da yake mishi ciwo a duk lokacin da suka haďu da Musaddiq,
kafaďunshi ya dafa can cikin zuciyarshi yace
"Nasan yadda kake ji,
naji makamancin hakan,
saidai nawa mai sauki ne dan nesa nesa nayi da ita,
shakuwar mu bata kai ta ma'auratan da sukayi wa juna dandani haukaci ba...
Amma a fili zancen Maleekah yayi mishi dan ya mantar dashi damuwa,
labarinta ya dinga bashi ya kuma bashi labarin irin karamcin mahaifinta,
"Inaa kayan mu,
zamu kafa tarihi,
dan nasan sai munyi faďa da Maleekah akan kayan da zan sa,
dazu take faďa min tayi ordern kayan da zamu sa,
muje inga yanayin dinki...
Dakin suka koma Musaddiq na yaba tsarin dinkin da akayi musu,
Hilal yayi matukar farin cikin ganin kayan dan daga shaddar har dinki sunci kudinsu,
ga wasu huluna masu matukar kyau kalar aikin kayan,
baje kayan sukayi suka cigaba da hira cike da debewa juna kewa.....
A katafaren masallacin gidan sheik aka daura auren,
farin cikin da wannan zuri'a take ciki a wannan ranar ba mai misaltuwa bane,
musamman Papa da Anty Reemah wacce saida tayi kukan farin ciki,
'yayanta Allah ya aurar mata dasu rana ďaya kuma cikin irin wannan zuri'a,
ita kuwa me zata cema Allah banda godiya,
yanzu Zainab ce kaďai a gabanta wacce take da burin faranta mata ta jiyar da ita dadin duniya....
Biki ne akayi shi mai kayatarwa dan an ci an sha kamar baza'a mutu ba,
sai kusan uku suka shirya tafiya reception,
yadda Hilal yayi zaton Maleekah sai ta bashi mamaki dan itama wani lace tasa wanda Anty Reemah tasa aka dinko mata,
riga da skirt ne Ash yasha duwatsu,
sunyi matukar kyau,
hakan da sukayi yazo da sabon salo, hotunansu suka dinga yawo a kafafen sadarwa na kasa da duniya baki ďaya,
wanda ma basu taba tunani ba yaga hoton,
domin babu inda hotunansu bai zaga ba,
Balarabiya da bahaushe cikin shiga ta hausawa,
A wannan daren boyayyen ruhi na nesa yayi kukan farin ciki da kuma na kewar makusanta,
hoton zamewa yayi tamkar wani kwai domin ya sanya ma'abocin kallonshi cikin shaukin son kasancewa da yan uwa..........
*6 years later*
*Cambridge Montessori Elementary School.*
The final round is here, *Expression words*
we have only three players left,
1 *Naurah Josephine*
2 *Mukhtar Hilal M Kyari*
3 *Victoria vertran*
Nan fa filin ya sake barkewa da ihu,
kowa na kiran sunan dan uwanshi....
Naurah ce farko,
tayi matukar kokarinta sai a wasu guraren ta kakare,
Sai Mukhtar,
kafin ya fara saida ya kalli inda wani mai irin kayanshi yake, kyakyawan mutum wanda hutu ya ratsa shi sosai,
Nuni yayi mishi da addu'a da hannu sannan ya sumbaci hannun ya hura mishi iska,
Lumshe ido Junior yayi ya rungume hannunshi haďe da jero adduoin da ya iya wanda ake koyar dashi a gida duk dare,
*Suratul nasr*
ya karanta karshe dan ya riga ya saba duk in zai zauna a aji sai ya karanta ta,
Bayan gaisuwar da ya gabatar cikin kwarewa sannan ya rufe da godiya haďe da kambama makarantarsu,
sannan ya rufe da wata siga ta marasa jin magana haďe da buga kwallon da ta gangaro gurin kafarshi,
bayan ya gama ya rufe da wata godiyar ya jero sunayenshi kamar haka..
Yours most lovely one
*HABIBI MUKHTAR HILAL MUSADDIQ KYARI*
A.K.A
*MHK TAHEER*.....
Farin ciki a gurin Anty Reemah ba'a cewa komai domin Allah ya gama mata komai,
ta samu nagartattun surukai wadanda zatayi alfahari dasu...
*(wannan shine result of kyakykyawar zuciya)*
********
Tun ana saura sati ďaya biki Maleekah da kawayenta suka fara shagalin biki,
abinka da yar drama,
babu inda labarin aurenta bai zaga ba,
daga mai kushe Hilal saboda bai kamo kafar samarinta a haďuwa ba, sai mai yabawa zarrarshi na samun Maleeka da maza kewa rububi,
babu wanda yasan abinda Allah ya ganar dasu ya sanyasu suke kaunar junansu sai su biyun da kuma wanda yasan waye *Hilal Kangiwa....*
*******
"Ya kira wayarta yafi a kirga bata ďaga ba,
tun yana kira cikin marmari har ranshi ya baci ya ajiye wayar a gefe,
duk yaji ringing sai ya dauka itace yayi saurin daukar wayar,
in yaga ba ita bace sai ya ajiye wayar ya saki tsaki,
rabon da ya sata a idonshi tun shekaranjiya da suka tafi Egypt yin wani bikin a can..
bai san fushi takeyi na kin binta da yayi,
taso su tafi bikin tare yaki, dan ya fi son yayi zamanshi yayi hidimarshi cikin yan uwanshi...
Karfe Sha ďaya ya kira layinta na Egypt yaji shi a kashe,
hakan ya tabbatar mishi da yanzu ta shigo tunda jibi ne daurin auren,
Shiryawa yayi cikin kananan kayan sanyi masu taushin gaske,
yana matukar missing dinta dan ta koyar dashi soyayyarta mai sanyi,
gashi bai iya soyayya ba dan in yana yinta gaba daya zuciyarshi yake sallamarwa wanda yake so...
Saida ya biya ta wani gift shop ya siyo mata wani abu dan yaji dadin bata hakuri...
A kofar gida ya sameta tare da kawayenta tana musu sallama,
cikin shigar da yake matukar so ya sameta, jallabiya har kasa da gyalenta,
Cikin gidan ya shigar da motarshi ya fito ya tsaya haďe da harďe hannu yana jiran dawowarta,
Minti biyu kaďai ta kara tazo tana shirin wucewa ciki,
kallo ya bita dashi har ta kusa yi mishi nisa,
"A wife is angry wit her Hubbi!!, ya faďi cikin wata irin muryar da baisan yana da ita ba,
Duk da taji sanyin jin muryarshi da kuma sunan da ya kirata dashi hakan bai sa ta tsaya ba,
“Getting angry doesn’t solve problems,
"Ana Aseef “ya Radhi’a”
plss don't be mad at me...
Ajiyar zuciya tayi haďe da tsayawa zuciyarta na maimaita kalmar
*Radhi'a*
duk wani bacin rai da ta kunsa na tunanin Hilal baya sonta kamar yadda take sonshi ta kaudashi,
Sanyin dake kadawa a garin ya haďu da wanda ke kaďuwa cikin zuciyarta ya sanyata cikin wani irin yanayin da takeji tamkar su biyu kadai Allah ya halitta a duniya,
"plss my love, ya faďi cikin raďa a saitin kunnenta,
Lumshe idanuwansu sukayi a tare saboda qamshin da kowannensu ya shaka na juna,
a hankali ta juyo ta fuskance shi haďe da shagwabe fuska,
yadda ta turo baki yasan magana ce zata biyo baya,
Cikin sauri ya fiddo wata red flower dake makale a bayan wandonshi,
Saitin hancinta ya sata haďe da furta mata wasu rikitattun kalmomin da baisan ranar da ya iya su ba,
Shidai yasan ya horu matuka da rashin jin muryar dake kwantar mishi da hankali,
sannan idanuwanshi sunyi matukar kewarta,
tayi matukar sabar mishi da kaunarta mai sanyin dadi,
a halin da yake ciki yanzu baya jin zai iya koda yini ne ba tare da ganinta ba,
"Ikon Allah kenan,
shi yakan sanya so a lokacin da yaso,
Ko a cikin mafarkinshi bai taba tunanin zai iya samarwa wata mace gurbi a zuciyarshi ba, bayan wacce ya kira da mamallakiyar Qalbinshi,
*Zuciyar gaba daya*..
Sai gashi cikin kankanin lokaci soyayyar Maleekah na neman shafe babin dake adane da boyayyar soyayyar da tun yarinta yake dakonta,
Wasu lokutan in ya zauna yana tunani sai ya alakanta abun da cewar saboda ita din jinin Nadeeyah ce,
sai yanzu ne da ta hora shi na ďan kwanaki ya tabbatar wa kanshi irin kaunar da yake mata...
"Fushin masoya hutu,
cikin kankanin lokaci Maleekah ta manta komai ta saki jiki suka sha soyayyarsu wacce armashinta yafi na baya saboda amintar dukkan zuciyoyin biyu..
Sai da dare ya tsala sosai sannan Hilal ya rakata har cikin parlo ya juya ya tafi cike da kewarta....
Maleekah is very nice,
halayyarta da kyakykyawar zuciya irin ta Mahaifinta shi ya kara mata matsayi a zuciyar Hilal...
Har ya kai gida bai bar tunaninta ba,
koda yayi parking mota saida ya dan jima cikin motar sannan ya fito fuskar nan cike da annashuwa,
ta steps yabi zuwa sama,
duk inda yazo wucewa sai an mishi congrat harda masu bashi gift din aure,
"Al'adar larabawa da yan Nigerian dake cikin estate din kenan,
musulmi da arne in abun farin ciki ko bakin ciki ya sameka to fa tare za'a raba jajen da farin cikin,
wayewarsu tasa suka dauki juna tamkar jini ďaya...
Yana karasawa kofar flat dinsu ya soma jiyo hira da shewa cikin parlon kasa,
hakan ne ya bashi tabbacin yan uwa sunzo,
farin cikin da yake ciki ya mantar dashi miskilin halinshi,
nan ya murda kofar da sauri yagansu cike da parlon yan kangiwa da su Mummy,
Cike da farin ciki ya karaso ya dauki Fadeel ya jefa shi sama,
Sannunku da zuwa,
kun sha hanya,
gefen da Goggo ke zaune tana karkaďa kafa ya kalla yace "Harda su Goggo,
Lallai yau muna da manyan baki,
bata kalli inda yake ba ta cigaba da kaďa kafa tana sakucen hakori,
"Tunda ta shigo gidan taga hoton Maleekah shikenan farin cikin da ta guntso ya tafi,
da fari ta fara masifa akan duk matan duniya ya rasa wacce zai auro sai mai zubin karuwai,
saida Mummy tayi tsaye akanta sannan ta maida hankalinta ta zauna a gefe tana cika tana batsewa..
"Ina Anty Rally, ya tambaya yana duban mahaifiyarshi,
"Suna sama da su Raudha,
wani aiki suke ma Hinad,
Musaddiq na ďaki tun dazu yake jiranka,
Hanyar saman ya nufa da sauri cike da farin ciki,
yasan zaman su Mummy a parlon ne ya hanashi zama ayi hira dashi...
"Hey Mr Soft,
kana ina ne?
Kafin Musaddiq ya bashi amsa ya karaso balcony din inda Musaddiq ke tsaye yana duban sararin samaniya,
Jingina yayi jikin karfen yanda zasu fuskanci juna,
"how r u Kyari?
Gyaďa kai Musaddiq yayi fuskarshi dauke da Murmushin da yafi kama da na ciwo,
ganin Hilal ne ya sanya zuciyarshi karyewa har murmushin ya fito,
A ko da yaushe in ya kasance shi kaďai yana jin sam rayuwarshi bata da amfani,
Ya kasa daukar hakurin mantawa da ita,
ita din mace ce da take da wuyar mantawa,
rayuwa yinta kawai saboda mahaifinshi da kuma Hilal,
amma yasan tabbas zuciyarshi na gab da bugawa dan ya kasa yin rayuwa mai dadi babu ita...
Gyara tsayuwa Hilal yayi cike da damuwar yanayin da yake mishi ciwo a duk lokacin da suka haďu da Musaddiq,
kafaďunshi ya dafa can cikin zuciyarshi yace
"Nasan yadda kake ji,
naji makamancin hakan,
saidai nawa mai sauki ne dan nesa nesa nayi da ita,
shakuwar mu bata kai ta ma'auratan da sukayi wa juna dandani haukaci ba...
Amma a fili zancen Maleekah yayi mishi dan ya mantar dashi damuwa,
labarinta ya dinga bashi ya kuma bashi labarin irin karamcin mahaifinta,
"Inaa kayan mu,
zamu kafa tarihi,
dan nasan sai munyi faďa da Maleekah akan kayan da zan sa,
dazu take faďa min tayi ordern kayan da zamu sa,
muje inga yanayin dinki...
Dakin suka koma Musaddiq na yaba tsarin dinkin da akayi musu,
Hilal yayi matukar farin cikin ganin kayan dan daga shaddar har dinki sunci kudinsu,
ga wasu huluna masu matukar kyau kalar aikin kayan,
baje kayan sukayi suka cigaba da hira cike da debewa juna kewa.....
A katafaren masallacin gidan sheik aka daura auren,
farin cikin da wannan zuri'a take ciki a wannan ranar ba mai misaltuwa bane,
musamman Papa da Anty Reemah wacce saida tayi kukan farin ciki,
'yayanta Allah ya aurar mata dasu rana ďaya kuma cikin irin wannan zuri'a,
ita kuwa me zata cema Allah banda godiya,
yanzu Zainab ce kaďai a gabanta wacce take da burin faranta mata ta jiyar da ita dadin duniya....
Biki ne akayi shi mai kayatarwa dan an ci an sha kamar baza'a mutu ba,
sai kusan uku suka shirya tafiya reception,
yadda Hilal yayi zaton Maleekah sai ta bashi mamaki dan itama wani lace tasa wanda Anty Reemah tasa aka dinko mata,
riga da skirt ne Ash yasha duwatsu,
sunyi matukar kyau,
hakan da sukayi yazo da sabon salo, hotunansu suka dinga yawo a kafafen sadarwa na kasa da duniya baki ďaya,
wanda ma basu taba tunani ba yaga hoton,
domin babu inda hotunansu bai zaga ba,
Balarabiya da bahaushe cikin shiga ta hausawa,
A wannan daren boyayyen ruhi na nesa yayi kukan farin ciki da kuma na kewar makusanta,
hoton zamewa yayi tamkar wani kwai domin ya sanya ma'abocin kallonshi cikin shaukin son kasancewa da yan uwa..........
*6 years later*
*Cambridge Montessori Elementary School.*
The final round is here, *Expression words*
we have only three players left,
1 *Naurah Josephine*
2 *Mukhtar Hilal M Kyari*
3 *Victoria vertran*
Nan fa filin ya sake barkewa da ihu,
kowa na kiran sunan dan uwanshi....
Naurah ce farko,
tayi matukar kokarinta sai a wasu guraren ta kakare,
Sai Mukhtar,
kafin ya fara saida ya kalli inda wani mai irin kayanshi yake, kyakyawan mutum wanda hutu ya ratsa shi sosai,
Nuni yayi mishi da addu'a da hannu sannan ya sumbaci hannun ya hura mishi iska,
Lumshe ido Junior yayi ya rungume hannunshi haďe da jero adduoin da ya iya wanda ake koyar dashi a gida duk dare,
*Suratul nasr*
ya karanta karshe dan ya riga ya saba duk in zai zauna a aji sai ya karanta ta,
Bayan gaisuwar da ya gabatar cikin kwarewa sannan ya rufe da godiya haďe da kambama makarantarsu,
sannan ya rufe da wata siga ta marasa jin magana haďe da buga kwallon da ta gangaro gurin kafarshi,
bayan ya gama ya rufe da wata godiyar ya jero sunayenshi kamar haka..
Yours most lovely one
*HABIBI MUKHTAR HILAL MUSADDIQ KYARI*
A.K.A
*MHK TAHEER*.....