← Book details Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 113

Sashe 33

Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Shiryawa tayi cikin wata koriyar atamfa mai ratsin ja,
dinkin zamani riga da straight skirt mai tsagu,
rigar kuma matsatstsa mai budadden hannu,
tayi kyau sosai,
Husnah ce ta bata a cikin kayanta da suka dan kamata dan tafi Nadeeya fadi kadan,
dankwali ta daura ta kunshe kanta ta dauko hijab zata sa,
fisgewa Husna tayi tace "u are a joker,
wa zaki bi da wannan hijab din,
gyale ta miko mata tace "dankwalin ma cireshi zakiyi,
kallon Husna tayi tace "da wannan matsatsun kayan zan fita babu hijab?
gyada mata kai tayi tace "hango kanki har kin fita ma,
zatayi magana Husnah ta kwacee dan dankwali ta turasu cikin drawer ta rufe,
shiryawa tayi tana waka tana rawa tana ma Nadeeyah gwalo,
ita abin dariya ma ya bata ta sake kallon kanta a jikin madubi,
babu ta inda kayan nan basu bayyana surorin ta ba,
marairecewa tayi tace "kiyi hakuri Husna ko dankwali ne in daura,
bata saurereta ba ta fara shafa mata powder tana fadin "ki cigaba da butulcewa Allah,
dan dai So ba samu bane,
wallahi da nice tsirara ne kadai bazanyi yawo ba,
lallausan gashinta ta taje mata tayi mata parking da katon ribon,
light janbaki ja ta bata tace "ki dan sa kadan kiga yadda zakiyi, amsa tayi tadan goga a bakinta, gurin madubin Husna ta jata tace "dan Allah kalla, kamar a bakinki aka halicceshi,
mtsww taja tsaki hade da cije lips tana hango inama akai Nadeeyah school dinsu tayi ma gayu iskanci, ta nunawa *SABRINAH BILAL* ba ita kadai aka halitto da kyau da sura ba,
gyale ta daura ma Nadeeyah a kanta irin yadda tayi tace "muje ko,
a kunyace Nadeeyah ta bi bayanta tana tunanin yadda zata fita da kayan nan ba hijab,

Fitowarsu tayi daidai da mikewar Badariyya, hade da fitowar mummy daga parlon Daddy,
fassara yadda idon Badar ke nuna tsantsan tsana da kishin Nadeeyah mai wuyar fadi ne a alkalami,
bata ankara ba taji Mummy ta sake furto maganar da taji ta kamar saukar Aradu,
"yawwa Nadeeyah gobe ki shirya da wuri zaku je makaranta tare dasu Husnah,
wani irin tsalle Husna tayi tace "so quick Ya Allah, lallai luck is on her side today,

kallon Badariyya Mummy tayi tace "ke bazaki kitson bane? dauke kanta tayi tace "umm bazanje school ba gobe,
tana kaiwa nan tayi hanyar daki, dakatar da ita Mummy tayi tace "saboda me?
Kafin ta bata amsa Musaddiq ya shigo parlon yana hamma, tsayawa yayi daga nesa yana kallon Nadeeyah daga sama har kasa..

Karasowa yayi ya kewayeta yana kallon fuskarta da ta sunkuyar kasa,
murmushi yayi yace "tsarki ya tabbata ga ubangijin da halicci kyawawan mata a cikin gidan mu,
ina zaku je da irin wannan kwalliyar,
Kusa dashi Husna ta matso tace "saloon, ko zaka kaimu ne?
bata fuska yayi yace "na kwaso rana,
bacci nakeji amma bazan iya refusing daukar kyawawan kannena a mota ba,
kallonshi Mummy tayi tace "kyalesu su tafi Diku,
jeka ka huta abinka,
girgiza kanshi yayi yace "bari in kaisu Mummy, zanyi aski nima,

jin haka ya sa Badariyya sakin ranta tace "Mummy su jirani nima zanje kitson,
bata rai Husna tayi tace "wallahi Mummy Badar bata mana lokaci zatayi,
harara mummy ta sakar mata tace "in ma zata kai la'asar sai kun jirata,
turo baki Husnah tayi suka dawo parlon suka zauna,

Wayarshi kirar iPhone x max ya ciro a aljihu ya kalli Husnah yace "meye zai bata ran autarmu,
tashi muje waje inyi miki hoto da portrait camera,
sanin halinta nasan hoto yasa shi fadin haka dan ya kwantar mata da hankali,
da sauri ta bi bayanshi tana kiran Nadeeyah da tazo suyi tare,
kin fitowa Nadeeya tayi saboda yadda mummy ta kafa mata ido,
kyawunta da ta gani na yau da yafi na ko yaushe shi ya daga hankalinta,
bata so samm Musaddiq ya fada tarkon kyawun nan,
taci buri akan nema mishi 'yayan abokan Daddy ministoci dan samun karin girma a idon kawayenta,
dole ta san abin yi akan irin wannan kwalliyar da Nadeeya ta fara yi,
dawowa Husna tayi taja hannunta suka fita dan yin hoton..

Hotuna sukayi masu matukar kyau kamar an wankesu,
wanda sukayi su biyu shi yafi komai yi mishi kyau,
suna gama hotunan ya gyarasu ya daurasu akan status dinshi da instagram,
bai rage ko daya cikin goman da suka dauka ba,
yana gama daurasu ya sauka dan ganin fitowar Badariyya,
gaba Badariyya ta bude da sauri ta shiga ta zauna,
kallonta yayi ya kasa cewa komai yashiga ya waigo ya kalli su Husna a baya,
tada motar yayi suka wuce,
ta gefen ido Badar ke satar kallonshi, shi kuwa hankalinshi na kan titi yana tambayar inda zasu, cikin doki Husnah tace *MEENA'S TOUCH* Sabon saloon din da Anty Amina ta bude,
ta madubi ya harereta yace "inada Allahn misirun sanin shagon kenan,
kafin Husnah ta bashi amsa Badar tayi saurin cewa " *Kura plaza* bai sake magana ba ya dauki hanyar Yakubu gawon way..

Yana saukesu ya bawa Husna dubu shidda yace "bani da enough ku kara,
kinsan nima sammin akeyi babu aikin yi,
dariya tayi tace aiki kam zaka samu yaya, kaima kasani, lokaci ne, dariya yayi ya wuce yana dagawa Nadeeyah hannu...

Wayarshi ya dauko a inda ya ajiyeta, yana bude ta kiran *Haidar Galadanci* ya shigo..

Dauka yayi yana dariya yace "Head Boy how far, ya kake,
daga daya bangaren Haidar yace "fine kyari, kana ina ne?
Taka birki yayi da karfi saboda mai mashin din da shigo mishi, tsakii yaja yace "ina gurin Leventis zanje waff road any probs?
Kwantar da murya yayi yace "Kyari naga bebs din story dinka, plss farar fa,
kanwarka ce?,
nasan Husna, ban dai gane farar bane,
dariya sosai Musaddiq yayi yace "kanwata ce Galadanci,
kafin ya karashe maganar yaji kiran Hilal ya shigo wayarshi a karo na uku,
hakuri ya bashi ya katse wayar dan ya dauki ta Hilal, kafin ya dauka ma ta katse,
duba missed calls yayi sunfi hamsin,
Hilal kadai talatin da uku yayi mishi,
sai sauran daga abokanshi,
kafin ya kira Hilal wayarshi ta shigo,
bai jira jin kalmar Hello ba saboda baya cikin nutsuwa da hankalinshi yace "dis is madness Kyari,
in banda rashin hankali ya zaka sanya hoton yarinyar nan a ig,
a story is understandable, but ig is very bad, duk inda ka zaga su arewa cuties nd co hotonta ne ke trending,
ya zakayi exposing dinta haka, wat is the need of all dis,
kuma baka ma duba kayan jikinta ba kawai ka tashi ka sata a social media,
idon mazan duniya su gama ganeta,
am very angry with u wallahi,
tunda ya fara masifar musaddiq yayi parking, saida ya gama zazzaga masifar yace "ka gama?

Tsaki Hilal yayi yace "ban gama ba, ka hau kaga banzayen comments din da akeyi maka,
na rokeka ka hau ka cire hotunan nan, cikin fada musaddiq yace "Bazan cire ba,
nace bazan cire ba,
hoton ta ita kadai nasaka,
au su sauran matan da suke saka hotonsu ba mata bane,
a fusace Hilal yace "ba irin su bace kyari,
ka kasa fahimtar ba irin matan da za'a dinga exposing bace,
yawo kalmar ta dingayi cikin kwakwalwar musaddiq yace
"wat do u mean, kana nufin bata kai matsayin da zata hau instagram ba,
ko kuwa tana da makusar da--- katse shi Hilal yayi yana share zufar da ta addabashi tun ganin hotunan da comments din abokan musaddiq yace "bazaka gane ba Kyari,
taushi yayi da muryarshi ya cigaba da cewa "rayuwarta zaka duba, marainiya ce, a yanzu gatanta shine ilimi,
wannan gayun ba nata bane, ilimin shine zai zamo gatanta gaba da baya,
yanzu wannan hoton baka san abubuwan da zai janyo mata ba,
samari zasu fara kawo mata hari, daga nan shikenan zasu zo su--- runtse idonshi yayi kafin ya furta kalman *aureta*, at end of the day kuma rayuwarta zata kare a bauta,
wasu kuma will come su yaudareta, wasu su lalata ta,
plss Musaddiq ka cire hoton nan,

cike da gamsuwa Musaddiq yace "very true, kamar kasan yanzu *Galadanci* ya kirani akanta and lots more, gara da ka fahimtar dani,
bari inyi maza in cire...

Safa da marwah ya dinga yi a cikin dakinshi,
pencil din da yake zane dashi yayi dagaga a bakinshi saboda tauna,
hoton ya sake kallo kashi na ba adadi yace "ya Allah ka cire idon duk wani namiji akan hoton nan,
yana cikin haka yaji karar notification din story a ig, *Husnah_kyari is live on instagram* da sauri ya hau,
yana budewa ya zauna dabass, *what is dis, ya ilahi!!
Ya fadi yana rike kanshi,
video Husna tayi musu da kai a bude,
gashin Nadeeyah ya sakko har baya,
a juye take tana parking din kanta, bata san Husna na mata video ba,
tsaki yaja sannan ya lalubi number wayarta, a zuciyarshi yace "kasheshi suke so suyi,
Chapter 33 · 0% Book details