Sashe 108
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da karfi ya janyo gudan jininshi cikin kirjinshi ya rungumeshi tsamm yana kuka mai taba zuciya,
Sai a lokacin zuciyar Musaddiq ta karye ya soma rero kuka mai cike da sambatu.....
Mrs Tijjani Shattima.......
[22/06 10:21 PM] +234 807 161 1811: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 7⃣5⃣
By *Aysha Ya'u kurah*
Jugummm jugummm..
sukayi a parlon kowa da abun da yake sak'awa a cikin ransa,
fitowar likitan da Hilal ne ya sanya su nufarsu da sauri,
"Doctor yaya?
Hope all is well?
Daddy ya tambaya cike da damuwa,
Guri likitan ya samu ya zauna haďe da ajiye akwatin taimakon gaggawarshi,
"Ka kwantar da hankalinka Alhaji,
komai lafiya kalau,
jinin da ya zubar ne kaďai ya sanyashi zama weak,
amma ya farfaďo, saidai ya samu bacci, yana bukatar hutawa da kulawa sosai..
yana kaiwa nan ya kalli mutanen dake zaune a parlon,
ganin rabinsu duk mata ne yasa shi mikewa yace
"Alhaji anjima ka sameni a office, akwai abin da zamu tattauna, Allah ya bashi lafiya ya karashe yana dafa kafadun Daddy haďe da yin hanyar waje....
Kasa zama Daddy yayi ya bi bayanshi da sauri dan baijin zai iya kaiwa anjima baiji abinda yake son su tattauna ba wanda ya tabbatar akan ciwon ďanshi ne....
Hilal kuwa zama yayi a can gefe, hawayen dake zarya a idanuwanshi sun kafe saboda tsananin tashin hankali
"Ta ina zai fara,
wace hanya zai bi dan ganin ya samar wa Musaddiq abun da yakeso ba tare da hankalin kowa ya tashi ba,
yafi karfin awa ďaya yana tufka da warwara amma bai samo mafita ba,
runtse idonshi yayi saboda yadda yake jin nauyi a kan kirjinshi, dakyar ya iya mikewa da taimakon Maleekah suka koma can dakin da Musaddiq yake....
Cikin kalaman hikima irin na likita, Doctor Lawal yake wa Daddy magana,
"Ya taba samun attack a yanda na lura,
saboda halin da na riskeshi a yau ban taba tunanin zai rayu ba..
Alhaji Mukhtar,
ďanka na cikin critical condition, zuciyarshi na iya bugawa at any time,
dan Allah ku kula a daina sanyashi cikin damuwa sannan a taimaka a samo mishi abinda yake so,
Cike da damuwa Daddy ya dubi Doc Lawal bayan ya gama mishi jawabi yace
"Samun abin da yake so wannan na Allah ne,
nidai zanyi kokarin ganin ya daina shiga damuwa da bacin rai...
Shawarwari Dr Lawal ya bashi kafin suyi Sallama....
Parlon ya koma jiki a sanyaye yana tunanin kalaman Doctor, yadda ya barsu a parlon haka ya dawo ya samesu saidai wannan karan suna dan tattaunawa da su Papy...
Bayan ya zauna ne suka shiga kum kum wannan na cewa wannan tayi magana suna ki,
a tare suka daure dan suna ganin hakan shine kaďai mafita ga rayuwar Musaddiq domin zaifi samun kula daga gurin uwa..
"Daddy dan Allah kayi ma Mummy afuwa,
ta gane kuskurenta,
dan Allah kayi hakuri ka sassauta mata...
Kallon 'ya'yan nashi yayi fuskar nan babu walwala zaiyi magana muryar Baffa ta katseshi....
"Me ya faru Rilwanu?
Me ya samu gidan nawa?
To to to gamu nan zuwa yanzu da yardar Allah ya karashe haďe da mikewa,
mikewa su Daddy sukayi suna tambayarshi ko lafiya?
"To nima dai ban sani ba,
Rilwanu yace inzo gida ba lafiya, a hanzarce suka fita dan zuwa gidan suga abinda ke faruwa..
Mummy dake can sama gurin Musaddiq itama tayi saurin mikewa ta biyo bayan Radiya da ta kawo mata rahoto...
Da sauri Malam Mato mahaifin Rilwanu ya debo ruwa ya mikawa matarshi dake tsaye kan Goggo tana taimaka mata,
wani irin ihu takeyi tana fisgar gashin jikinta haďe da firzar da ruwan da ake zuba mata a baki,
"Gishiri,
Gishiri,
hakan ta dinga faďi tana zaro harcenta da yayi fari tass kamar mayya,
Gishirin rilwanu ya debo a cikin buhu ya kawo musu dan a tunaninsu ciwukan jikinta zata sawa,
yana kawo mata ta yafa kusan rabin kofin a bakinta,
A firgice suka fara kokarin kwace kofin suka kasa saboda a wannan lokacin karfin ba ďaya bane,
ko jariri ne wanda bashi da zunubin komai sai ya fuskanci barazanar wannan rana bare mutum irin Goggo wacce ta naďi kayayyakin bil adama marasa adadi...
Sarketa gishirin yayi ta shiga tari kirjinta na ďagawa sama kamar zai rabu da jikinta,
yaye zanin jikinta tayi saboda tsabar azaba ta mike ta fara zubar da kayan dakinta tana ihu sosai..
Halacci da iyayen Rilwanu suke ganin an yiwa dansu shi ya hanasu barin dakin duk ko da irin warin dake fita a jikin Goggo...
Wasu gungun hotuna ta zubo har gaban malam mato, saura kiris glass din da ya fashe ya taba kafarshi,
da sauri ya matsa baya ya tsuguna ya fara tattara hotunan ya umurci Rilwanu da matarshi da su riketa,
yana gama tattara hotunan ya ajiyesu a kan table zai komo gurinta..
Tsayawa yayi cakk ya waigo da sauri ya sake duban hoton saman wanda bashi da kala samm, dauko hoton yayi jiki na rawa yace "Ma'un Ukari,
*Nankwat Manasir*
shigowar su Baffa ne yasashi mayar da hoton da bazai taba manta ranar da akayi shi ba,
"Innalillahi wa inna ilaihir rajiun..
shi kawai yake maimaitawa cikin ranshi tare da tunanin inda mutanen nan masu matukar karamci suka san mace marar imani irin Ma'u...
Mummy ce ta karaso ciki ta dauko zani dan rufe mata tsiraicin jikinta tana kuka sosai,
Baffa kuwa hannunta ya rike yana faďin
"Ma'u zauna kiyi ta salati,
a yanzu ihu ba naki bane,
da karfinta ta fisge tayi hanyar waje tana ihun da ko gida uku ne tsakaninku zakaji ta,
da azama suka bita suka rikota suka maidata daki suka garkameshi dan yadda take jiyar da mutane ciwo....
Malam Mato kasa rike abun yayi a ranshi yace
"Marar lafiyar nan itace Ma'u wacce naga hotonta da kananan yara biyu?
Da sauri Baffa yace "Eh itace, ka santa ne?
Juyayi Malam Mato ya shiga yana tunanin ta yanda zai fara sanar dasu abubuwan da ya sani shekaru da dama wanda babu wanda yasan dasu sai ubangijin talikai sai shi da ita kanta Ma'un,
Nufar inda yake Baffa yayi zaiyi magana sukaji ihun Goggo tana faďin
"Na shiga uku,
ku kira min Bokan Ukari yazo ya tamaikeni,
yagar naman jikina akeyi,
wayyo,
wayyo,
ku kirashi yazo ya taimakeni,
yayi min alkawarin bazan mutu ba,
yayi min alkawarin karashe rayuwata har kowa ya mutu ya barni..
"Mai kashewa shi ke tsoron mutuwa,
shin akwai adalci a cikin wannan?
Malam ya Mato yayi tambayar ba tare da jiran amsar kowa ba,
da sauri ya nufi dakin ya buďeshi domin a yanzu samm ya daina tausaya mata...
"Ai bai kamata wanda yake da karfin zuciyar sanadiyyar rayukan mu'imunai da dama tsoron mutuwa ba,
*JUMMA'ATU BABBAN RANA*
Ranar yin katako daga kauyen ukari zuwa Gembu,
*Ma'u yar gidan Manasir*...
Tunaninki zai iya tafiya shekaru hamsin da doriya suka wuce,
in kin manta ni bazan manta ba,
zan fara tuna miki in yaso sai ki karasa da bakinki..
Tunda ya fara maganar azababben jikin Goggo ya saki,
maganarshi tafi ciwon azaba...
"Harďejo,
Musulman kauyen Gembu,
suna Sallar Jumma'a...
ko zaki iya tuna abun da faru a ranar,
cikin dabara yace
"Faďin ainihin abin da ya faru shine kadai zai taimaki rayuwarki ki dawo kamar yadda kike da, sannan babu zancen mutuwa har sai dan kanki kinji duniyar ta isheki...
Saboda jahilci da kuma tsabar son duniya, Goggo ta fara faďin dukkan labaran da suka faru a baya,
har kawo mutuwar Atika da yunkurin kashe Papy da kuma irin ukubar da ta bawa Mamma Suwaiba, har yadda tayi ta raba Daddy da Mamma suwaiba ta hanyar asiri,
wannan confession din tayi shi ne cike da sa ran ciwon zai barta sannan bazata mutu ba,
ta sa rai bayan ta rayu zata yi asirin da zai mantar dasu komai...
*Goggo dai tazo duniya zama ne, tazo ne kawai ta karaci rayuwarta cikin asarar da lokacinta gurin yiwa wasu sihiri domin kawai gamsar da zuciyarta*....
Ajiyar Zuciya Malam Mato yayi ya kalli duk mutanen gurin da suka mutu a tsaye saboda jin rashin imanin Goggo,
"Alhamdulillah da Allah ya taimakeni ta faďi da bakinta domin inata tunanin yadda zan gamsar daku,
a lokacin da Ma'u ta sanar da yan ta'addan nan cewa akwai Musulmai a kauyen Gembu, bani da bakin magana domin na riga na ce musu ni ba musulmi bane, bayan mun shiga garin na saukesu sai na nufi can wani guri na samu maboya,
ganin irin kisan gillar da sukayi ma musulman kauyen yasani barin garin Taraba gaba dayanta saboda tsabar tsoron wata rana wannan abun zai faru dani ko wani nawa,
a kullum kwanan duniya cikin shekarun nan sai na tuno da wannan al'amarin,
rashin sanin inda zanga mai aika aikar yasani barin wa cikina komai,
da nasan a gidan nan take wallahi da kaina zan mikata ga hukuma su hukunta ta tun da sauran karfinta,
amma yanzu ko an mikata ga hukuma babu amfani domin hukuncin ubangiji ya fara tun anan duniya kafin ta riskeshi a lahira....
Wani irin kuka Baffa ya durkushe a gurin ya fara yi cikin kunan rai, shekara da shekaru yana tare da wacce ta rabashi da ahalinshi,
a harzuke bayan kukan ya lafa ya mike ya nufi inda take zaune tana yakushin jikinta ya kaiwa wuyanta shaka..
A gaggauce su Papy suka share hawayensu suka nufi gurin Baffa, dakyar suka iya rabashi da Goggo wacce take ihun ceton rai..
"Karka zama irinta Baffa,
sai ka kwashe dukkan zunubbanta,
ka barta da abunta ta girbe abun da ta shuka da hannunta..
Daddy ne ke magana cike da takaicin haďa iri da wannan zuri'a karo na ba adadi,
dole ya dinga fuskantar kalubale kala kala a cikin tashi zuri'ar...
Mummy samm ta kasa motsawa daga inda take,
juya maganganun ta dingayi a cikin kwakwalawarta,
rashin imanin mahaifiyarta har ya kai haka,
tabbas dole ta dinga ganin jarabawa kala kala,
Allah bai bata uwa ba,
wannan wacce irin uwa ce wacce sam babu kwayar halittar imani a cikin zuciyarta...
Zaburar da Goggo ta sakeyi ita ta dawo dasu daga duniyar sake saken da suka tafi,
babu wanda yayi yunkurin bin ta sai Papy da Anni,
kafin su kai inda take har ta kusa kofar gida....
Sai a lokacin zuciyar Musaddiq ta karye ya soma rero kuka mai cike da sambatu.....
Mrs Tijjani Shattima.......
[22/06 10:21 PM] +234 807 161 1811: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 7⃣5⃣
By *Aysha Ya'u kurah*
Jugummm jugummm..
sukayi a parlon kowa da abun da yake sak'awa a cikin ransa,
fitowar likitan da Hilal ne ya sanya su nufarsu da sauri,
"Doctor yaya?
Hope all is well?
Daddy ya tambaya cike da damuwa,
Guri likitan ya samu ya zauna haďe da ajiye akwatin taimakon gaggawarshi,
"Ka kwantar da hankalinka Alhaji,
komai lafiya kalau,
jinin da ya zubar ne kaďai ya sanyashi zama weak,
amma ya farfaďo, saidai ya samu bacci, yana bukatar hutawa da kulawa sosai..
yana kaiwa nan ya kalli mutanen dake zaune a parlon,
ganin rabinsu duk mata ne yasa shi mikewa yace
"Alhaji anjima ka sameni a office, akwai abin da zamu tattauna, Allah ya bashi lafiya ya karashe yana dafa kafadun Daddy haďe da yin hanyar waje....
Kasa zama Daddy yayi ya bi bayanshi da sauri dan baijin zai iya kaiwa anjima baiji abinda yake son su tattauna ba wanda ya tabbatar akan ciwon ďanshi ne....
Hilal kuwa zama yayi a can gefe, hawayen dake zarya a idanuwanshi sun kafe saboda tsananin tashin hankali
"Ta ina zai fara,
wace hanya zai bi dan ganin ya samar wa Musaddiq abun da yakeso ba tare da hankalin kowa ya tashi ba,
yafi karfin awa ďaya yana tufka da warwara amma bai samo mafita ba,
runtse idonshi yayi saboda yadda yake jin nauyi a kan kirjinshi, dakyar ya iya mikewa da taimakon Maleekah suka koma can dakin da Musaddiq yake....
Cikin kalaman hikima irin na likita, Doctor Lawal yake wa Daddy magana,
"Ya taba samun attack a yanda na lura,
saboda halin da na riskeshi a yau ban taba tunanin zai rayu ba..
Alhaji Mukhtar,
ďanka na cikin critical condition, zuciyarshi na iya bugawa at any time,
dan Allah ku kula a daina sanyashi cikin damuwa sannan a taimaka a samo mishi abinda yake so,
Cike da damuwa Daddy ya dubi Doc Lawal bayan ya gama mishi jawabi yace
"Samun abin da yake so wannan na Allah ne,
nidai zanyi kokarin ganin ya daina shiga damuwa da bacin rai...
Shawarwari Dr Lawal ya bashi kafin suyi Sallama....
Parlon ya koma jiki a sanyaye yana tunanin kalaman Doctor, yadda ya barsu a parlon haka ya dawo ya samesu saidai wannan karan suna dan tattaunawa da su Papy...
Bayan ya zauna ne suka shiga kum kum wannan na cewa wannan tayi magana suna ki,
a tare suka daure dan suna ganin hakan shine kaďai mafita ga rayuwar Musaddiq domin zaifi samun kula daga gurin uwa..
"Daddy dan Allah kayi ma Mummy afuwa,
ta gane kuskurenta,
dan Allah kayi hakuri ka sassauta mata...
Kallon 'ya'yan nashi yayi fuskar nan babu walwala zaiyi magana muryar Baffa ta katseshi....
"Me ya faru Rilwanu?
Me ya samu gidan nawa?
To to to gamu nan zuwa yanzu da yardar Allah ya karashe haďe da mikewa,
mikewa su Daddy sukayi suna tambayarshi ko lafiya?
"To nima dai ban sani ba,
Rilwanu yace inzo gida ba lafiya, a hanzarce suka fita dan zuwa gidan suga abinda ke faruwa..
Mummy dake can sama gurin Musaddiq itama tayi saurin mikewa ta biyo bayan Radiya da ta kawo mata rahoto...
Da sauri Malam Mato mahaifin Rilwanu ya debo ruwa ya mikawa matarshi dake tsaye kan Goggo tana taimaka mata,
wani irin ihu takeyi tana fisgar gashin jikinta haďe da firzar da ruwan da ake zuba mata a baki,
"Gishiri,
Gishiri,
hakan ta dinga faďi tana zaro harcenta da yayi fari tass kamar mayya,
Gishirin rilwanu ya debo a cikin buhu ya kawo musu dan a tunaninsu ciwukan jikinta zata sawa,
yana kawo mata ta yafa kusan rabin kofin a bakinta,
A firgice suka fara kokarin kwace kofin suka kasa saboda a wannan lokacin karfin ba ďaya bane,
ko jariri ne wanda bashi da zunubin komai sai ya fuskanci barazanar wannan rana bare mutum irin Goggo wacce ta naďi kayayyakin bil adama marasa adadi...
Sarketa gishirin yayi ta shiga tari kirjinta na ďagawa sama kamar zai rabu da jikinta,
yaye zanin jikinta tayi saboda tsabar azaba ta mike ta fara zubar da kayan dakinta tana ihu sosai..
Halacci da iyayen Rilwanu suke ganin an yiwa dansu shi ya hanasu barin dakin duk ko da irin warin dake fita a jikin Goggo...
Wasu gungun hotuna ta zubo har gaban malam mato, saura kiris glass din da ya fashe ya taba kafarshi,
da sauri ya matsa baya ya tsuguna ya fara tattara hotunan ya umurci Rilwanu da matarshi da su riketa,
yana gama tattara hotunan ya ajiyesu a kan table zai komo gurinta..
Tsayawa yayi cakk ya waigo da sauri ya sake duban hoton saman wanda bashi da kala samm, dauko hoton yayi jiki na rawa yace "Ma'un Ukari,
*Nankwat Manasir*
shigowar su Baffa ne yasashi mayar da hoton da bazai taba manta ranar da akayi shi ba,
"Innalillahi wa inna ilaihir rajiun..
shi kawai yake maimaitawa cikin ranshi tare da tunanin inda mutanen nan masu matukar karamci suka san mace marar imani irin Ma'u...
Mummy ce ta karaso ciki ta dauko zani dan rufe mata tsiraicin jikinta tana kuka sosai,
Baffa kuwa hannunta ya rike yana faďin
"Ma'u zauna kiyi ta salati,
a yanzu ihu ba naki bane,
da karfinta ta fisge tayi hanyar waje tana ihun da ko gida uku ne tsakaninku zakaji ta,
da azama suka bita suka rikota suka maidata daki suka garkameshi dan yadda take jiyar da mutane ciwo....
Malam Mato kasa rike abun yayi a ranshi yace
"Marar lafiyar nan itace Ma'u wacce naga hotonta da kananan yara biyu?
Da sauri Baffa yace "Eh itace, ka santa ne?
Juyayi Malam Mato ya shiga yana tunanin ta yanda zai fara sanar dasu abubuwan da ya sani shekaru da dama wanda babu wanda yasan dasu sai ubangijin talikai sai shi da ita kanta Ma'un,
Nufar inda yake Baffa yayi zaiyi magana sukaji ihun Goggo tana faďin
"Na shiga uku,
ku kira min Bokan Ukari yazo ya tamaikeni,
yagar naman jikina akeyi,
wayyo,
wayyo,
ku kirashi yazo ya taimakeni,
yayi min alkawarin bazan mutu ba,
yayi min alkawarin karashe rayuwata har kowa ya mutu ya barni..
"Mai kashewa shi ke tsoron mutuwa,
shin akwai adalci a cikin wannan?
Malam ya Mato yayi tambayar ba tare da jiran amsar kowa ba,
da sauri ya nufi dakin ya buďeshi domin a yanzu samm ya daina tausaya mata...
"Ai bai kamata wanda yake da karfin zuciyar sanadiyyar rayukan mu'imunai da dama tsoron mutuwa ba,
*JUMMA'ATU BABBAN RANA*
Ranar yin katako daga kauyen ukari zuwa Gembu,
*Ma'u yar gidan Manasir*...
Tunaninki zai iya tafiya shekaru hamsin da doriya suka wuce,
in kin manta ni bazan manta ba,
zan fara tuna miki in yaso sai ki karasa da bakinki..
Tunda ya fara maganar azababben jikin Goggo ya saki,
maganarshi tafi ciwon azaba...
"Harďejo,
Musulman kauyen Gembu,
suna Sallar Jumma'a...
ko zaki iya tuna abun da faru a ranar,
cikin dabara yace
"Faďin ainihin abin da ya faru shine kadai zai taimaki rayuwarki ki dawo kamar yadda kike da, sannan babu zancen mutuwa har sai dan kanki kinji duniyar ta isheki...
Saboda jahilci da kuma tsabar son duniya, Goggo ta fara faďin dukkan labaran da suka faru a baya,
har kawo mutuwar Atika da yunkurin kashe Papy da kuma irin ukubar da ta bawa Mamma Suwaiba, har yadda tayi ta raba Daddy da Mamma suwaiba ta hanyar asiri,
wannan confession din tayi shi ne cike da sa ran ciwon zai barta sannan bazata mutu ba,
ta sa rai bayan ta rayu zata yi asirin da zai mantar dasu komai...
*Goggo dai tazo duniya zama ne, tazo ne kawai ta karaci rayuwarta cikin asarar da lokacinta gurin yiwa wasu sihiri domin kawai gamsar da zuciyarta*....
Ajiyar Zuciya Malam Mato yayi ya kalli duk mutanen gurin da suka mutu a tsaye saboda jin rashin imanin Goggo,
"Alhamdulillah da Allah ya taimakeni ta faďi da bakinta domin inata tunanin yadda zan gamsar daku,
a lokacin da Ma'u ta sanar da yan ta'addan nan cewa akwai Musulmai a kauyen Gembu, bani da bakin magana domin na riga na ce musu ni ba musulmi bane, bayan mun shiga garin na saukesu sai na nufi can wani guri na samu maboya,
ganin irin kisan gillar da sukayi ma musulman kauyen yasani barin garin Taraba gaba dayanta saboda tsabar tsoron wata rana wannan abun zai faru dani ko wani nawa,
a kullum kwanan duniya cikin shekarun nan sai na tuno da wannan al'amarin,
rashin sanin inda zanga mai aika aikar yasani barin wa cikina komai,
da nasan a gidan nan take wallahi da kaina zan mikata ga hukuma su hukunta ta tun da sauran karfinta,
amma yanzu ko an mikata ga hukuma babu amfani domin hukuncin ubangiji ya fara tun anan duniya kafin ta riskeshi a lahira....
Wani irin kuka Baffa ya durkushe a gurin ya fara yi cikin kunan rai, shekara da shekaru yana tare da wacce ta rabashi da ahalinshi,
a harzuke bayan kukan ya lafa ya mike ya nufi inda take zaune tana yakushin jikinta ya kaiwa wuyanta shaka..
A gaggauce su Papy suka share hawayensu suka nufi gurin Baffa, dakyar suka iya rabashi da Goggo wacce take ihun ceton rai..
"Karka zama irinta Baffa,
sai ka kwashe dukkan zunubbanta,
ka barta da abunta ta girbe abun da ta shuka da hannunta..
Daddy ne ke magana cike da takaicin haďa iri da wannan zuri'a karo na ba adadi,
dole ya dinga fuskantar kalubale kala kala a cikin tashi zuri'ar...
Mummy samm ta kasa motsawa daga inda take,
juya maganganun ta dingayi a cikin kwakwalawarta,
rashin imanin mahaifiyarta har ya kai haka,
tabbas dole ta dinga ganin jarabawa kala kala,
Allah bai bata uwa ba,
wannan wacce irin uwa ce wacce sam babu kwayar halittar imani a cikin zuciyarta...
Zaburar da Goggo ta sakeyi ita ta dawo dasu daga duniyar sake saken da suka tafi,
babu wanda yayi yunkurin bin ta sai Papy da Anni,
kafin su kai inda take har ta kusa kofar gida....