← Book details Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 113

Sashe 34

Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"My Personal person ta fadi da karfi,
bai amsa ba yace "tarbiyyar musulmi ne daura video babu dankwali,
come on je ki cire shi,
dariya tayi tace "done my PP, yanzu zan cire,
ajiyar zuciya yayi yace "hope kuna nan lafiya,
amsawa tayi da cewa lafiya kalau kowa yake,
"Good yace hade da cewa ku kula sosai fa,
kunsan samarin yanzu basu da kirki,
is hardly su soku tsakani da Allah, ku kama kanku ku daina kwalliya kuyi focusing akan karatunku kinji,
gyada kai tayi tace "in shaa Allah my pp,
murmushin jindadi yayi yace "bani Nadeeyah,
saida yaji kunya da ya fada,
cire wayar yayi a kunnenshi ya kalleta hade da jin haushin kanshi,
to me zaice mata?
, sansanyar muryata yaji tana fadin "Assalamu alaikum,
"kara wayar yayi a kunnenshi yace "Alaiki salam, ya kk
, lafiya lau ina wuni ta fadi darare,
lafiya lau,
kinada abubuwa a gabanki kike kwalliya harda wani possing ayi hoto ko?,
murya na rawa tace "a'a yau ne kawai,
kuma munje saloon ne,
dadi yaji har cikin ranshi yace "to ya zama na karshe,
karatunki yanzu shi kadai zaki sa a gaba,
ko powder ki daina shafawa,
u are very ok a haka,
ki daure kiyi karatu sosai ki zama independent woman kinji ko?
Gyada kanta tayi kamar tana gabanshi tace "in shaa Allah zan kiyaye,
"yauwa kanwata take care ya fadi hade da kashe wayar ba tare da ya barta ta bashi amsa ba.......

Tun dare Daddy ya kira principal din makarantar,
da yake suna ganin girmanshi shiyasa basuyi rejecting ba suka ce gobe a zo da ita a mata interview,
godiya yayi mishi sukayi sallama, a waya ya kira Musaddiq yace gobe ya shirya ya kaisu school yayi mata registration,
amsawa yayi yace "Allah ya kaimu Daddy...

Kallo ne ya koma kan su Husna lokacin da suka fito a cikin motar, jar jallabiya Husna ta zabowa Nadeeya tace ta saka, saboda tayi bagu a makaranta,
ai kuwa sun kawo kallo,
har a registrar office duk staff din da ya shigo sai ya kalli Nadeeyah,
bayan an gama mata komai suka mata interview,
dakyar ta wuce saboda karatunsu yayi mata tsauri,
Ss3 Art 1 suka kaita saboda Art take a makarantar da ta baro..

Sallama Musaddiq yayi musu ya wuce yana jaddada musu muhimmacin karatu,
commerce class Husna take,
saida taja ta suka je class dinsu kafin teacher ya shigo,

zagayesu akayi ana tambayar Husna sunan sistern ta,
murmushi tayi kanta yayi girma tace "She is my cousin,
Nadeeyah Adam,
wow nice name suka hada baki suka fadi, *Jameelah Aja* ce tace "a sit dina zata zauna,
nan fa class din ya kaure kowa na a gurinshi zata zauna harda mazan class din,
Dariya sosai Husna tayi tace "to a Art take,
tsaki sukayi sukace 1 or 2, one ofcourse Salmah Habeeb ta fadi hade da cewa "wai halan uncle Kamal zabar kyawawa yakeyi ya kaisu art da kanshi badan suna so ba,
dariya duka class din suka kece dashi suka ce very true,
duk taron kyawawa ne a art,
halan gani yayi duk sunfi dacewa da art gidan da babu Maths,

Hango Economics teachernsu sukayi kowa ya nemi gurin zama ya nutsu,
hannunta Husna taja suka hau sama inda class dinsu yake, daukar excuse tayi gurin Uncle Tahir literature teacher tace
"new comer ce sir,
uncle Kamal yace a kawota nan class din, kuma yace a bata special treatment,
hararta yayi cikin slangs turancin shi yace go to your class,
da sauri ta fita tana dariya,

kallon Nadeeyah yayi yace "welcome, what is your Name?
Gyara baki tayi cike da kunyar kallon da yan ajin suke mata tace "Nadeeyah Adam from Fgc malali, "Good ya fadi yana kare mata kallo,
seat din Sabrinah ya kalla yaga ita kadaice bata barin kowa ya zauna,
nuni yayi mata da sit din yace "go and sit down der,
bata rai Sabrinah tayi fuska da alamar shagwaba tace "sir,
Hararta yayi ya cigaba da abin da yakeyi,
tana zama tace "sannu,
ko kallonta Sabrinah bata yi ba tace ciwo nakeyi?
Nadeeyah bata sake kulata ba ta maida hankalinta kan allo...

*Gombe state university*

9:34am
Monday 17th july,

Assalamu alaikum..

Waigowa gungun samarin sukayi suka amsa da "wa alaikum salam hade da mika mashi hannu suka gaisa,
dan Allah ina ne Acadamic planning? Hafeez ya tambaya yana gyara jakarshi,
kwatance suka mishi yayi musu godiya ya koma motarshi,
hanyar da suka nuna mishi yabi, yana zuwa gurin yaga sunan a manne,
fitowa yayi da takardunshi ya karasa kofar shiga,
layin students ya gani suna turereniya suna mika takardu, wani ya samu a gurin yace "dan Allah ina ne office din Director academic planing,
nuna mishi office din yayi ya juya ya kutsa cikin layin,

Da sallama ya shiga ya tarar da secertary dinshi,
bayan sun gaisa ya tambayeshi ko lafiya,
takardu ya mika mishi yace "nazo registration din D.E ne,
karbar takardun yayi ya duba yace
"kaje waje daga lungu zaka ga wani office ka tambayi ina Hajiya farida, ka bata,
amsan takardun yayi hade da yi mishi godiya,
yana kokarin fita daga office din yaji an murda kofar wani office dake kusa da kofar fita,
dan saurayi ne ya fito fari kyakykyawa,
kallonshi yayi ya miko mishi hannu suka gaisa,
kallon sani Hafeez yayi mishi, tunanin inda ya sanshi ya shiga yi,

"Kai Jamal, ka dauki key din motar ne,
waigowa sukayi tare da Hafeez yace "yes Papy, kai fa ka miko min,
a wannan karan ba kallan sani Hafeez yayi wa dattijon ba,
kallon kamannin da yayi da mukusancin shi yayi mishi,
Allah mai halitta,
tabbas badan wannan fari bane tass babu abinda zai hanashi cewa shi bane......

Mrs Tijjani Shattimah......
[11/03 4:41 PM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 3⃣4⃣
By *Aysha Ya'u kurah*

Har kasa Hafiz ya tsuguna ya gaida dattijon,
bai kalli inda yake ba ya amsa yana magana secretary dinshi, Mikewa Hafeez yayi har lokacin idonshi nakan dattijon,
waigowar da zaiyi idanuwansu suka sarkafu cikin na juna,
nan take wani abu ya tsarga a jikin dattijon,
bai dauke idonshi akan Hafeez ba ya karaso kusa dashi yace "your face looks familiar,
wani level kake?,
cikin girmamawa Hafeez yace "yau na fara zuwa,
nazo registration ne, "Good, ya sunanka and wane course? dattijon ya tambaya har lokacin bai fasa kallon Hafeez yana nazarin inda yasanshi ba, "sunana Hafeez Adam, daga kaduna, computer science ne sir!
kauda tunanin inda yasanshi yayi dan ya kasa tunowa,
shi dai yasan yaron ya shiga ranshi daga ganin farko,
kuma a dan fisge idonshi na yanayi da Jamal,
kafadunshi ya dafa yace "All the best, Allah yasa ka fara a sa'a, Ameen.. Hafeez ya fadi ya bishi da kallo har ya fita daga office din....

Rashin nutsuwar da bai samu ba saboda registration shiyasa bai koma gurin directorn ba,
saida yayi sati uku ya samu nutsuwa har ya fara shiga lectures, a sannan ne ya fara tunanin konawa gurin mutumin dan jin ko yana da wani dan uwa, kamannin sunyi matukar yawa, badan tsufa da haske ba, babu abinda zai hanashi cewa su ba yan biyu bane,
saidai wannan ya fishi yarinta, da haske da kuma ilimi...

Yana gama cin abinci a cafeteria ya wuce masallaci yayi sallah, yana idarwa ya kama hanyar Academic planing,
meeting ya samu suna yi sai ya fita harabar gurin dan ya jirasu, saida yayi jiran awa 3 basu gama ba sannan ne ya hakura ya tafi gida,
zuwa academic planing ya zamewa Hafeez kullum,
wata rana har yaje sau biyu duk ba sa'a,
ko ace suna meeting ko kuma ace yana office din VC..

Ranar friday karfe 11 suke da lectures din Maths method,
tun tara na safe ya shiga school ya wuce office din,
zama yayi a gurin yana jiran ganin ta inda zai bullo,
daga can nesa ya hangoshi yana tafiya sauri sauri secretary dinshi yana binshi a baya da jaka,
mikewa Hafeez yayi ya iso gurinshi ya tsugana ya gaishe shi,
dafa kanshi yayi hade da mishi alama da ya dago,
sannan ya amsa, yace "malam Hafeez har ka gama settling ko?
Cike da mamakin rike sunanshi da yayi yace "eh ranka ya dade, kullum sai nazo bana cika samun ganinka,
tafiya ya fara yi yace "Allah sarki, schedules din nawa ne are very tight, muje in baka card dina kazo gida ka sameni......

*Kaduna*

Cikin ikon Allah Nadeeyah ta fara sabawa da yan ajinsu mata,
bata saki jiki dasu a farko ba saboda gudun wulakancin masu kudi,
da taga kowa na shige mata sai ta fara sakin jiki dasu musamman *Haifa* da *Amal* su biyun nan su suka zama kawayenta,
tun da suka fahimci Sabrinah na jin haushin shigowar Nadeeyah cikinsu sai suka dauke Nadeeya a sit dinta suka maida ita gabansu,
duk jan ajin Sabrinah saboda ganin tana da kyau ta saukeshi saboda ganin yanzu duk yan ajin sun raja'a akan Nadeeyah....

" *Badariyyah Kyari* sisternki tana da kyau sosai,
Rukky Mama ta cabe da cewar bari kedai Aliya,
in muna tsaye a assembly kallonta kawai nakeyi,
na rasa cikin jinsin da ta fito, fatarta kadai abar kallo ce,
uwa uba yatsun hannu,
kamar sun sokawa Badariyya Mashi tayi saurin cewa "ba sister na bace dalla,
she is an orphan, kawota gidanmu akayi dan ta dinga tayamu aiki,
u knw Daddy is very generous, kawai yaga tunda mate dinmu ce why nt ya sata a school tunda dama ss3 zata,
she is our helper kun gane ko!!

Kallonta Rukky tayi tace "kaii amma tayi sa'a, ga kyau, gashi ta dace gidan ruko,
wallahi in tana wucewa gaban staff room malamai har leke sukeyi,
uncle Tahir ne kadai bai wannan saboda class dinshi,
shi duk yadda ake koda sabrinah bata gabanshi,
shiyasa wannan ma bata d'ad'ashi ba,
gajiya Badar tayi da jin maganganu akan Nadeeyah tayi saurin mikewa ta wuce hade da ja musu tsaki...
bayanta suka bi da sauri saboda duk yan koranta ne.....
Chapter 34 · 0% Book details