Sashe 41
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
tana fitowa idanuwanta suka sauka kan Anni,
baya taja kamar zata fadi bakinta na rawa tace,
H-an-ne.......
Mrs Tijjani Shattima.....
[18/03 8:06 AM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 3⃣9⃣
By *Aysha Ya'u kurah*
Kallon rashin sani Anni tayi mata dan bata gane fuskarta ba,
nan dai ta fadada murmushinta tace "Na'am barkanku da gida, dafatan mun sameku lafiya,
Goggo dake tsaye jikinta na rawa kamar mazari tace "lafiya lau,
matsawa tayi gefe tace ku shigo ciki,
tabarmi Mummy ta fito dasu tace "a'a Goggo bari su zauna a waje yafi iska..
Bayan sun zazzauna an gaggaisa, Goggo ta kalli Hanne kirjinta na duka uku uku tace "baki ganeni ba ko Hanne?,
gyada kai Anni tayi tace "ban ganeki ba,
gyara zama Ma'u tayi kishi ya motso mata ta fara charge ta kalli Papy tace
"wannan ce mahaifiyarka??
Eh!!
Papy ya fada yana mai jin dadin an gane mahaifiyarshi a gidan,
"TABDIJAM Goggo tace "tana kallon Anni,
Wato Hanne ke kika haifeshi,?
wannan karan mamaki yasanya Anni cewa kwarai ni na haifeshi, dana ne,
lafiya??
Idon Goggo ya rufe ta manta da yara a gurin tace
"wato dama cikin shegen da kika dinga yawo dashi a tsakanin jalingo da Gembu dama Mijina ne yayi miki shi,
kenan lokacin da nake tausayin ki in su Harira suna tsangwamarki ashe kallon sakarya kike min mijina ne ya kunsa miki,
kallon Radiya tayi tace "maza tafi shagon Gidado ki kira min Baffan ku,
kafin Radiya ta mike Baffa ya shigo gidan da sallama,
yana ganin wucewarsu ya mike a shagon Gidado hade da amso musu lemu,
Goggo sam bata basu damar amsa sallamar ba tace "yauwa gara da Allah ya kawo ka,
nuna Hanne tayi tace ka gane wannan,?
kallonta yayi yaga samm shi bai taba ganinta ba,
ita kuwa Anni kallo ta bishi dashi idonta ya ciko da kwalla tana fadin
Alhamdulillah,
Alhamdulillah,
zama Baffa yayi yace "ban santa ba,
wacece ita?
Tafa hannu Goggo tayi tace "yau ni naga Bariki,
Hannen ce baka sani ba?
Hannen gidansu Inna wuro kanwar Harira,
wacce ta kunso cikin shege aka korota daga garinsu ta dawo nan,
ashe kai ka kunsa mata,
gashi dai kamanni sun bayyana min komai,
wallahi kaji kunya, ta karasa fadi tana haki..
"innalillahi wa inna ilaihir rajiun kawai Baffa da Papy ke fada,
ganin shurun da Baffa yayi ya kara hassala Ma'u ta fara surfafa masifa da bala'i,
babu inda baya rawa a jikinta,
da dai Anni taga shuru bazai taimakesu ba tace.
"Wallahi tallahi ban taba koda magana dashi ba...
shuru Ma'u tayi tana hararar Hanne tana fadin rainin hankali, uban wa zaki rainawa hankali?
"gyara zama Anni tayi ta kalli Baffa tace "in ka yarda dani ka bani dama inyi maka bayanin komai,
idonta ta mayar kan Goggo tace "in kikaji labarin abinda ya faru, da kuma yadda ya faru ni nasan gode min zakiyi ba zargi da zagi ba,
ni ko a yau Allah ya dauki raina walhy naji dadi saboda zan cika buri na,
kullum bani da tunanin da ya wuce ta yaya zan wankewa Abdallah zuciyarshi,
ta yaya zan hada shi da mahaifinshi,
nasan duniya tana da fadi wata rana ina da yakinin Allah zai amsa min addu'ata,
sai gashi ta dalilin Hafeezu adduar da na dade ina yi Allah ya amsa...
Alheri danko ne...
Kallon su Radiya dasu Hafeez tayi tace "dan Allah ko yaran nan zasu dan bamu guri,
"babu inda zasu, Ma'u ta fadi tana tafa hannu,
kallon Jamal Mami tayi tace "dauki Ruwaidah ku tafi mota,
noke wuya tayi tace "um um,
zare mata ido Mami tayi zatayi magana Anni ta dakatar da ita,
"zo takwara,
zo kuje ku siyo min Goro kinsan kin fishi wayau naki yafi kyau,
Jiki na rawa ta mike zata wuce ta taka kafar Radiya,
da karfi ta hankada ta cikin ihun azaba saboda tsinin takalmin tace "ke makauniya ce?
baki ta bare ta fara kuka idonta kyar akan Radiya,
da sauri Hafeez ya ja hannunta suka fita yana rarrashinta,
Harara Mummy ta sakarma Radiya tace "sai kace kina yi da sa'arki,
turo baki tayi tace "mummy zafi wallahi,
"tashi ki bamu guri dalla,mummyn ta fadi a hassale,
da sauri Goggo tace "babu fa inda zata,
gyara zaman ki,
abun kunya ce suka kwaso suji kunyar su kadai,
Girgiza kai Anni tayi tace "babu komai ma,
zauna! labarin an yishi ne, ba kirkirarre bane,
kaddara ce..
Kamar yadda kika sani ni kanwar Harira ce,
mahaifina asalinshi dan Gombe ne,
mahaifiyata ce yar jalingo..
Allah ya jarabceni da soyayya da dan kanin babanmu,
mun dade tare dashi,
kullum in na fita tallan nono a gurin yake zama har ya kare, mu tafi gida..
wata rana nono na yayi kwantai, yakai ni dare,
a hanyar mu ta dawowa gida kaddara ta afka mana,
kaddarar da dan adam bai isa ya tsallake ta ba,
kaddarar dake sanya rayuwar budurwa da iyayenta cikin mawuyacin hali...
kaddarar da ta sanya Mahaifina rasa rayuwarshi...
Bayan an fahimci ina dauke da ciki,
saboda tsabar kunya irin ta fulanin "da" mahaifina ya kashe kanshi ta hanyar fadawa cikin teku, a cewarshi bazai iya fuskantar jama'a ba..
mahaifiyata da kishiyoyinta suka sani a gaba,
bani da katabus cikin kauyenmu,
ko kofi na taba babu wanda yake dauka,
haka in na fita gari an dinga darewa kenan,
shi kuma wanda yayi min cikin an nemeshi ko sama ko kasa an rasa,
daga baya ne muka samu labarin mutuwarshi,
nan fa na cire duk wani tsammani na samun mijin aure,
saboda tsabar tsana da iyaye da yanuwana suka min na fita hayyacina na kare na lalace,
mahaifiyata ma kunya ta sanyata ta rame,
saida abin ya isheta tace "in shirya in tafi jalingo gurin mahaifiyarta,
To acan ma hakan take domin kuwa saida na gwammaci zama a Gombe da zaman jalingo,
duk ranar jumma'a sai Yakumbo kakata ta turani Gembu gidan Harira saboda gudun kunyar jumma'a,
tana tsoron kar mutane su shigo su ganni,
gaba daya yan uwa sun tsane ni ta ko ina,
bani da gurin shan iska...
wata ranar jumma'a mai cike da ban alajabi da tsoratarwa,
Jumma'ar da manta ta ga yan uwan mutanen kauyen Gembu abu ne mai matukar wahala..
Tun cikin dare nake jin kaina kamar bani ba saboda yadda cikina ya dinga murda min,
a hakan Yakumbo tace in fito in wuce Gembu,
tun a hanya cikin ke murda min har al'amarin yaso fin karfina,
cikin ikon Allah cikin ya lafa min har muka shiga cikin kauyen,
a daddafe na karasa cikin kauyen nayi gamo da tashin hankalin da yasanya cikina kadawa har kafata ta gaza daukata,
ina kallonka sanda ka dauko matarka da wata mace kuna gudu,
da rarrafe na bi bayanku har nazo lungun shiga gidanku,
nan gaba daya karfina ya kare, haihuwar ta taho min gadan gadan,
Cikin ikon Allah na haifi 'yata mace,
dankwalina na cire na nadeta dashi hade da mahaifar,
koda na duba ta na dinga jijjigata na tabbatar bata raye,
anan ne nayi kuka sosai har muryata ta dashe,
ban kara sanin inda hankalina yake ba saboda zubar jinin da nakeyi..
Iska mai karfi ce ta taso a kauyen wacce kafin ruwa ya sauka saida ta dauke gidaje,
wannan iskar ita ta farkar dani nayi saurin mikewa da gawar yata na fada cikin gidan ka,
koda na shiga babu kowa a gidan sai kasar da ke tashi tana rufe ko ina na gidan,
Daki na shige da sauri,
har cikin dakin kasar ke shiga saboda iskar ba ta wasa akeyi ba,
Iskar na lafawa ruwa ya tsuge kamar da bakin kwarya,
A nan ne naji ihun jariri daga waje,
da sauri na fito na iso gurin na hango dan Mala'ikan Allah cikin zani kwance a kirjin mahaifiyarshi,
Share hawayen idonta tayi tace
"Allah shi ke raya Matacce a lokacin da yaso,
in ba Allah ba waye zai raya wanda kasa ta rufe idonshi,
ko da na dagoshi jini ne ke fita daga cikin cibiyar da ba'ayi mata yanka da kyau ba,
nan take nayi daki dashi na gyara yankan cibiyar na daureta da tsumma,
ruwan bai tsagaita ba sai can gurin magriba,
yana tsayawa na kunshe yata na mayar da ita cikin gawar da Allah ya nuna ikonsa akanta,
A tare na rufesu da kyau saboda ko yadda aka zuba kasar wata rana ruwa ka iya dago gawar saboda sam kabarin baiyi zurfi ba..
A lokacin ne na fahimci wani abu guda daya game da cikin da nayi,
wannan abu kuwa shine bak'in zare mai shara shara wanda babu mai ganinsa sai ubangiji,
wannan zaren kuwa shine zaren kaddara!
kaddarar rainon Abdallah ta nuna Baffa tace "danka, ita ta sani na dauki ciki har sanadiyar shi nazo har wannan kauyen..
Da fari a kullum ina tunanin ni kadai ce Allah baya so a duniyar nan da ya jarabceni da yin cikin shege a cewar bahaushe,
haduwata da Abdallah na fahimci dama nazo duniya ne domin shi,
koda na koma gida Yakumbo tayi tayi ta rabani dashi,
a lokacin ne na nuna musu nima ina da hakki akan dana, tunda ni na haifeshi,
babu wanda ya taba samun labarin bani na haifeshi ba,
A lokacin da na bijirewa yakumbo sai ta koreni tace in tafi gurin uwata ita bazata iya da wannan abun kunyar ba,
bani da kudi haka na goyashi saboda bashi da kayan sawa,
ga rashin karfi nawa da nashi,
Cikin ikon Allah muka samu motar zuwa Gombe,
saida muka kwana uku a hanya muna tafiya,
duk kauyen da muka tsaya anan zan roki ruwan zafi in mishi wanka,
wata baiwar Allah ce ta hada min da wani maganin da nasha har na samu karfin jikina,
sannan ta bani wanda na barbada ma cibiyarshi hade da gishiri,
koda muka isa gida nan ma akayi min caaa ana Allah wadai dani,
ban saurari kowa ba na shiga gurin mahaifiyata na roki gafararta,
nace mata zan tafi neman abun da zan rike ďa na,
Bata kalleni ba amma shashshekar kukanta shi ya tabbatar min da tana cikin tsananin damuwa,
har na kai kofa ta kirani,
dawowa nayi naga ta kwanto gefen zaninta ta fito da kudi masu yawa na furar da takeyi ta bani ba tare da ta kalleni ba,
baya taja kamar zata fadi bakinta na rawa tace,
H-an-ne.......
Mrs Tijjani Shattima.....
[18/03 8:06 AM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 3⃣9⃣
By *Aysha Ya'u kurah*
Kallon rashin sani Anni tayi mata dan bata gane fuskarta ba,
nan dai ta fadada murmushinta tace "Na'am barkanku da gida, dafatan mun sameku lafiya,
Goggo dake tsaye jikinta na rawa kamar mazari tace "lafiya lau,
matsawa tayi gefe tace ku shigo ciki,
tabarmi Mummy ta fito dasu tace "a'a Goggo bari su zauna a waje yafi iska..
Bayan sun zazzauna an gaggaisa, Goggo ta kalli Hanne kirjinta na duka uku uku tace "baki ganeni ba ko Hanne?,
gyada kai Anni tayi tace "ban ganeki ba,
gyara zama Ma'u tayi kishi ya motso mata ta fara charge ta kalli Papy tace
"wannan ce mahaifiyarka??
Eh!!
Papy ya fada yana mai jin dadin an gane mahaifiyarshi a gidan,
"TABDIJAM Goggo tace "tana kallon Anni,
Wato Hanne ke kika haifeshi,?
wannan karan mamaki yasanya Anni cewa kwarai ni na haifeshi, dana ne,
lafiya??
Idon Goggo ya rufe ta manta da yara a gurin tace
"wato dama cikin shegen da kika dinga yawo dashi a tsakanin jalingo da Gembu dama Mijina ne yayi miki shi,
kenan lokacin da nake tausayin ki in su Harira suna tsangwamarki ashe kallon sakarya kike min mijina ne ya kunsa miki,
kallon Radiya tayi tace "maza tafi shagon Gidado ki kira min Baffan ku,
kafin Radiya ta mike Baffa ya shigo gidan da sallama,
yana ganin wucewarsu ya mike a shagon Gidado hade da amso musu lemu,
Goggo sam bata basu damar amsa sallamar ba tace "yauwa gara da Allah ya kawo ka,
nuna Hanne tayi tace ka gane wannan,?
kallonta yayi yaga samm shi bai taba ganinta ba,
ita kuwa Anni kallo ta bishi dashi idonta ya ciko da kwalla tana fadin
Alhamdulillah,
Alhamdulillah,
zama Baffa yayi yace "ban santa ba,
wacece ita?
Tafa hannu Goggo tayi tace "yau ni naga Bariki,
Hannen ce baka sani ba?
Hannen gidansu Inna wuro kanwar Harira,
wacce ta kunso cikin shege aka korota daga garinsu ta dawo nan,
ashe kai ka kunsa mata,
gashi dai kamanni sun bayyana min komai,
wallahi kaji kunya, ta karasa fadi tana haki..
"innalillahi wa inna ilaihir rajiun kawai Baffa da Papy ke fada,
ganin shurun da Baffa yayi ya kara hassala Ma'u ta fara surfafa masifa da bala'i,
babu inda baya rawa a jikinta,
da dai Anni taga shuru bazai taimakesu ba tace.
"Wallahi tallahi ban taba koda magana dashi ba...
shuru Ma'u tayi tana hararar Hanne tana fadin rainin hankali, uban wa zaki rainawa hankali?
"gyara zama Anni tayi ta kalli Baffa tace "in ka yarda dani ka bani dama inyi maka bayanin komai,
idonta ta mayar kan Goggo tace "in kikaji labarin abinda ya faru, da kuma yadda ya faru ni nasan gode min zakiyi ba zargi da zagi ba,
ni ko a yau Allah ya dauki raina walhy naji dadi saboda zan cika buri na,
kullum bani da tunanin da ya wuce ta yaya zan wankewa Abdallah zuciyarshi,
ta yaya zan hada shi da mahaifinshi,
nasan duniya tana da fadi wata rana ina da yakinin Allah zai amsa min addu'ata,
sai gashi ta dalilin Hafeezu adduar da na dade ina yi Allah ya amsa...
Alheri danko ne...
Kallon su Radiya dasu Hafeez tayi tace "dan Allah ko yaran nan zasu dan bamu guri,
"babu inda zasu, Ma'u ta fadi tana tafa hannu,
kallon Jamal Mami tayi tace "dauki Ruwaidah ku tafi mota,
noke wuya tayi tace "um um,
zare mata ido Mami tayi zatayi magana Anni ta dakatar da ita,
"zo takwara,
zo kuje ku siyo min Goro kinsan kin fishi wayau naki yafi kyau,
Jiki na rawa ta mike zata wuce ta taka kafar Radiya,
da karfi ta hankada ta cikin ihun azaba saboda tsinin takalmin tace "ke makauniya ce?
baki ta bare ta fara kuka idonta kyar akan Radiya,
da sauri Hafeez ya ja hannunta suka fita yana rarrashinta,
Harara Mummy ta sakarma Radiya tace "sai kace kina yi da sa'arki,
turo baki tayi tace "mummy zafi wallahi,
"tashi ki bamu guri dalla,mummyn ta fadi a hassale,
da sauri Goggo tace "babu fa inda zata,
gyara zaman ki,
abun kunya ce suka kwaso suji kunyar su kadai,
Girgiza kai Anni tayi tace "babu komai ma,
zauna! labarin an yishi ne, ba kirkirarre bane,
kaddara ce..
Kamar yadda kika sani ni kanwar Harira ce,
mahaifina asalinshi dan Gombe ne,
mahaifiyata ce yar jalingo..
Allah ya jarabceni da soyayya da dan kanin babanmu,
mun dade tare dashi,
kullum in na fita tallan nono a gurin yake zama har ya kare, mu tafi gida..
wata rana nono na yayi kwantai, yakai ni dare,
a hanyar mu ta dawowa gida kaddara ta afka mana,
kaddarar da dan adam bai isa ya tsallake ta ba,
kaddarar dake sanya rayuwar budurwa da iyayenta cikin mawuyacin hali...
kaddarar da ta sanya Mahaifina rasa rayuwarshi...
Bayan an fahimci ina dauke da ciki,
saboda tsabar kunya irin ta fulanin "da" mahaifina ya kashe kanshi ta hanyar fadawa cikin teku, a cewarshi bazai iya fuskantar jama'a ba..
mahaifiyata da kishiyoyinta suka sani a gaba,
bani da katabus cikin kauyenmu,
ko kofi na taba babu wanda yake dauka,
haka in na fita gari an dinga darewa kenan,
shi kuma wanda yayi min cikin an nemeshi ko sama ko kasa an rasa,
daga baya ne muka samu labarin mutuwarshi,
nan fa na cire duk wani tsammani na samun mijin aure,
saboda tsabar tsana da iyaye da yanuwana suka min na fita hayyacina na kare na lalace,
mahaifiyata ma kunya ta sanyata ta rame,
saida abin ya isheta tace "in shirya in tafi jalingo gurin mahaifiyarta,
To acan ma hakan take domin kuwa saida na gwammaci zama a Gombe da zaman jalingo,
duk ranar jumma'a sai Yakumbo kakata ta turani Gembu gidan Harira saboda gudun kunyar jumma'a,
tana tsoron kar mutane su shigo su ganni,
gaba daya yan uwa sun tsane ni ta ko ina,
bani da gurin shan iska...
wata ranar jumma'a mai cike da ban alajabi da tsoratarwa,
Jumma'ar da manta ta ga yan uwan mutanen kauyen Gembu abu ne mai matukar wahala..
Tun cikin dare nake jin kaina kamar bani ba saboda yadda cikina ya dinga murda min,
a hakan Yakumbo tace in fito in wuce Gembu,
tun a hanya cikin ke murda min har al'amarin yaso fin karfina,
cikin ikon Allah cikin ya lafa min har muka shiga cikin kauyen,
a daddafe na karasa cikin kauyen nayi gamo da tashin hankalin da yasanya cikina kadawa har kafata ta gaza daukata,
ina kallonka sanda ka dauko matarka da wata mace kuna gudu,
da rarrafe na bi bayanku har nazo lungun shiga gidanku,
nan gaba daya karfina ya kare, haihuwar ta taho min gadan gadan,
Cikin ikon Allah na haifi 'yata mace,
dankwalina na cire na nadeta dashi hade da mahaifar,
koda na duba ta na dinga jijjigata na tabbatar bata raye,
anan ne nayi kuka sosai har muryata ta dashe,
ban kara sanin inda hankalina yake ba saboda zubar jinin da nakeyi..
Iska mai karfi ce ta taso a kauyen wacce kafin ruwa ya sauka saida ta dauke gidaje,
wannan iskar ita ta farkar dani nayi saurin mikewa da gawar yata na fada cikin gidan ka,
koda na shiga babu kowa a gidan sai kasar da ke tashi tana rufe ko ina na gidan,
Daki na shige da sauri,
har cikin dakin kasar ke shiga saboda iskar ba ta wasa akeyi ba,
Iskar na lafawa ruwa ya tsuge kamar da bakin kwarya,
A nan ne naji ihun jariri daga waje,
da sauri na fito na iso gurin na hango dan Mala'ikan Allah cikin zani kwance a kirjin mahaifiyarshi,
Share hawayen idonta tayi tace
"Allah shi ke raya Matacce a lokacin da yaso,
in ba Allah ba waye zai raya wanda kasa ta rufe idonshi,
ko da na dagoshi jini ne ke fita daga cikin cibiyar da ba'ayi mata yanka da kyau ba,
nan take nayi daki dashi na gyara yankan cibiyar na daureta da tsumma,
ruwan bai tsagaita ba sai can gurin magriba,
yana tsayawa na kunshe yata na mayar da ita cikin gawar da Allah ya nuna ikonsa akanta,
A tare na rufesu da kyau saboda ko yadda aka zuba kasar wata rana ruwa ka iya dago gawar saboda sam kabarin baiyi zurfi ba..
A lokacin ne na fahimci wani abu guda daya game da cikin da nayi,
wannan abu kuwa shine bak'in zare mai shara shara wanda babu mai ganinsa sai ubangiji,
wannan zaren kuwa shine zaren kaddara!
kaddarar rainon Abdallah ta nuna Baffa tace "danka, ita ta sani na dauki ciki har sanadiyar shi nazo har wannan kauyen..
Da fari a kullum ina tunanin ni kadai ce Allah baya so a duniyar nan da ya jarabceni da yin cikin shege a cewar bahaushe,
haduwata da Abdallah na fahimci dama nazo duniya ne domin shi,
koda na koma gida Yakumbo tayi tayi ta rabani dashi,
a lokacin ne na nuna musu nima ina da hakki akan dana, tunda ni na haifeshi,
babu wanda ya taba samun labarin bani na haifeshi ba,
A lokacin da na bijirewa yakumbo sai ta koreni tace in tafi gurin uwata ita bazata iya da wannan abun kunyar ba,
bani da kudi haka na goyashi saboda bashi da kayan sawa,
ga rashin karfi nawa da nashi,
Cikin ikon Allah muka samu motar zuwa Gombe,
saida muka kwana uku a hanya muna tafiya,
duk kauyen da muka tsaya anan zan roki ruwan zafi in mishi wanka,
wata baiwar Allah ce ta hada min da wani maganin da nasha har na samu karfin jikina,
sannan ta bani wanda na barbada ma cibiyarshi hade da gishiri,
koda muka isa gida nan ma akayi min caaa ana Allah wadai dani,
ban saurari kowa ba na shiga gurin mahaifiyata na roki gafararta,
nace mata zan tafi neman abun da zan rike ďa na,
Bata kalleni ba amma shashshekar kukanta shi ya tabbatar min da tana cikin tsananin damuwa,
har na kai kofa ta kirani,
dawowa nayi naga ta kwanto gefen zaninta ta fito da kudi masu yawa na furar da takeyi ta bani ba tare da ta kalleni ba,