Sashe 12
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
da sauri Nadeeyah ta kalli sama,
a firgice ta maida kanta kasa tace "waiii Mamma wannan hasken mai cutarwa ne,
bazan iya jurar kallanshi ba..
Jajircewa zakiyi Nadeeyah,
daurewa zakiyi ki fuskance shi domin bashi kadai bane,
hango wani yana fasowa a dayan gefen, duk sun kewaye taurarin dake kewaye dake da haskensu,
waigawa tayi cike da zumudi da murnar jin maganar mahaifinta,
Baba dama baka mutu ba?
kaga yadda kayi kyau kuwa,
hannuwanta ya kama yace "Tafiya ce ta kamani ta gaggawa,
kinga mahaifiyarki bata iya jure zaman, ta biyoni,
saidai dawowar mu ba mai yiwuwa bace, domin tafiyar ta din din ce,
lokacin da zakiyi wannan tafiyar baiyi ba,
yanzu lokaci ne na hakuri da jajircewa,
in kina son nasara sai kin jure,
in kina san zuciyarki tayi haske sai kinyi hakuri,
"Amma fa ba hakurin da zai cutar dake ba, cewar mamma tana murmushi tana shigewa jikin mijinta,
akwai hakuri me cutarwa ne Suwaiba,
murmushi tayi tace "akwai mana,
hakurin da kana ji kana gani a taka ka a wuce,
wannan hakurin ka iya fasa zuciya,
manzon Allah s.a.w yace "in bazaka iya hakurin abun da akayi maka ba ka rama daidai yadda akayi maka,,
"kwarai haka yake, Baba ya fadi sannan ya cigaba cewa
"ke din me nasara ce, zaki daukaka fiye da tunanin mai tunani, saidai kinsan dukkan ma'abocin daukaka yana tare da kalubale,
amma ki sani kuma kisa a ranki, a ko yaushe Allah swt yana tare dake,
karki yada Addu'a domin ita din garkuwa ce ga mu'imini...
lokacin tafiyarmu yayi,
ki kula da dukkan rayuwarki da ta yar uwarki,
sannan kiyi hakuri da dan uwanki, domin shi din mai rauni ne,
Nadeeyah tayi saurin cewa "zan biku Mamma, murmushi mai sanyin kyau sukayi mata,
suka hade baki cikin murya me kamar amsa kuwwa, sukace
"wannan tafiyar ta musamman ce, lokacin yinta a gareki baiyi ba Nadeeyah,
Tafiya suka fara yi Nadeeyah na binsu tana kuka tana fadin karku tafi ku barni,
tun tana hangensu har haske ya kara kewaye gurin,
tsayawa tayi hade da runtse ido tana kiran sunayensu hade da shashshekar kuka...
Hannun da taji kan kuncinta mai sanyin kamshi ne ya soma farkar da ita,
a hankali ta bude idonta ta saukesu kan Hinad da itama kukan takeyi..
"Sorry Nadeeyah,
kiyita karanta innalillahi wa inna ilaihir rajiun,
i know it hurts but bamu da yadda zamuyi,
addu'a itace tafi dacewa dasu a wannan lokacin,
Allahn da ya halicce su ya fimu sansu..
kawar da kai Nadeeyah tayi tana tunano hirarsu ta cikin mafarkinta,
"kunyi tafiya mai nisa Mamma,
tafiya mai dadi a gareku in shaa Allah,
sannan mai radadi a garemu,
hawayen idonta bai bar ambaliya ba ta cigaba da maganar zucin da takeyi, yanzu yaya rayuwarmu zata kasance,
shikenan bamu da wani sauran gata...
"Gatan kowa Allah ne Kanwata,
babu wani gata mai daraja, dadi, da dadadawa irin na ubangiji,
in Allah ya baiwa bawa gata, to babu wanda ya isa ya tauye ko ya kwace mishi,
mika lamarinki gurin ubangiji, kuma kiyi tawakkali kisan shi ne kadai maiyi...
saida ya kai aya Nadeeyah ta dago ta kalli gefen da yake,
tabbas zancen da takeyi a zuci ne ya fito har ya iske kunnuwanshi,
shi din ma tsaye yake idon nan nashi yayi jawur kamar gauta,
wani hawayen ya share sannan ya karaso jikin gadon da take,
zama yayi gefenta yace "ya jikin naki, runtse ido tayi ta amsa da sauki,
Allah ya baki lafiya da hakuri hade da juriya,
"Ameen yaya Musaddiq, Hinad fadi tana share mata sauran hawayen dake gefen kunnenta..
Ina Zainab take yaya Musaddiq?
Kafin Musaddiq yayi magana sukaji an murda kofar,
Hafeezu ne ya fara shigowa sai su Anty Reemah,
Hilal ne karshen shigowa shi da zainab, hannunta rike da ledojin kayan kwalama,
fuskar nan tata tayi jawur,
tana ganin Nadeeyah ta saki ledar ta karasa ta fada jikinta tana kuka,
mikewa Nadeeyah tayi a hankali sannan ta janye daga kusa da musaddiq, ta dago kan zainab tace "menene, me aka miki?
Anti Nadeeyah mamma ma ta mutu, ta tafi gurin baba,
sun dauketa sun fita da ita,
shikenan bazamu sake ganinta ba,
dariya Nadeeyah tayi tace "inji wa yace miki,
mamma bata mutu ba,
kinsan tace miki zata je Agadaz rannan ko?
Eh zainab tace tana me kallon Nadeeyah,
to can ta tafi, kina gani sun shiryata ta hau jirgi tana jin dadinta ke kuma kina nan kina kuka,
oya share hawayenki ki ji abin da mamma tace in fada miki dazu kafin ta tafi,
da sauri ta share hawayenta ta matso da kunnenta kusa da bakin Nadeeyah, rada tayi mata a kunne wanda Allah kadai yasan me tace mata, sai ko Zainab ta kyalkyace da dariya hade da rungume Nadeeyah, tace "dagaske kikeyi Anti?
Gyada kai Nadeeya tayi tace "eh,
hawayen da ta boye ne ya fara bin idanuwanta, ta kankame zainab tana zubar dasu ba tare da ta bari ta gansu ba, wayyo mutuwa.....!
@
Mrs Tijjani Shattima....!
[07/03 6:31 AM] fareedah: ●ZUMUNCINMU A YAU● 1⃣9⃣
By Aysha Ya'u Kurah
Had'a kayayyakinsu cikin jaka Nadeeyah keyi, idanuwan nan nata sai ambaliyar ruwa suke,
Hafeez ke tayata had'a kayan yana labarta mata abubuwan da suka gifta tsakaninshi da iyayensu a yan watannin da suka shude,
jan numfashi yayi kamar karamin yaro,
daga zuciya har idaniyar shi zubar ruwan hawaye sukeyi,
"yan kudaden da suka fara shigowa hannuna su suka ruda ni,
na canza abokai,
kullum bani wancan club bani wancan,
ban tsaya nan ba har sai da na koma harkar mata,
tun ina boyewa, su Baba basu sani ba har takai ga mata har gida suke biyoni,
bazan taba manta daren da zan bar gida ba,
Baba ya fito zai tafi Sallar asuba ya jiyo muryata da SAILUBA yar gidan Hinde mai tuwo,
ranar a daki na ta kwana, Koda Baba ya bude kofar, Sailuba na kwance a jikina,
duk yadda na kai ga tureta in suturta jikina ta kafe ta danneni, na kasa tabuka komai,
saida Baba ya juya, nayi karfin halin turata na mike nasa jallabiya nabi bayanshi,
Kuka na tarar dashi yana yi a tsakar gida,
a tare muka iso inda yake ni da Mamma,
ajiye butar hannunta tayi ta fara tambayarshi dalilin zubar hawayenshi,
bai kai ga yin magana ba Sailuba ta fito da daurin kirji da kayanta a hannu tana sawa tana fadin
"Zo ka sallameni Hafeezu in tafi kar a nemeni a gida,
wani irin juwa Mamma ta ji a tsakiyar kanta, bakinta da kyar yake iya furta innalillahi wa inna ilaihir rajiun, daki Baba ya jata ba tare da ya dubi inda na ke ba,
koda na biyosu ciki da sauri Baba ya dakatar dani yace
"fitar min a daki da kazantar dake jikinka,
tafi kaje ka sallameta,
ka wadata ta da duk wani nau'i na jin dadi tunda kaima ta jiyar da kai dadin,
ubangiji Allah ya shiryar dakai Ameen,
Har na iso kofar dakina ina jiyo sautin kukan mamma, Baba yana ta bata hakuri..
Da kudin da ni kaina bansan yawansu ba na sallami Sailuba,
sai na wuce nayi wanka nayi sallah,
shaidan ya dinga raya min in bar gidanmu in tafi can inda babu wanda yasanni, tunda ina da kudina inje in ci karena babu babbaka,
a haka nabi umurnin zuciyata na shirya kayana tsaff na sasu a mota,
Zainab na gani a kofar shagon Tasi, na bata dubu biyar ta kaiwa Mamma, nace ta fada musu nayi tafiya,
tun kafin ta shiga gidan na shige mota nayi gaba,
a tunanina duniyata zatayi kyau tunda babu mai samin ido,
ashe tafiyar da zata kashemin zuciya ta barni da dana sani har karshen rayuwata nayi... ya karashe maganar cikin matsanancin kuka...
Takalman Zainab Nadeeyah ta tura cikin ledar dake hannunta, wacce tun fara bata labarin ta budeta da niyyar zuba takalman,
ledar ta jike sharkaff saboda hawayen da ke sauka a kanta,
kallon Hafeez tayi tace "Yaya Allah yayi mana jarabawa mai zafin gaske,
rayuwa ce yanzu zamu fara ta wacce bamu san inda zata kaimu ba,
ka godewa Allah da yasa suka yafe maka, sannan kaji tsoron Allah,
ka nisanci duk wani aikin alfasha, kasani duk abinda zakayi yanzu za'a tada su Mamma ace su tashi suga dansu, shin irin wannan tarbiyar suka baka,
kasani yanzu babu wani wanda zai fada maka gaskiya,
rayuwa ce zakayi ta ta rashin mafadi,
kai da kanka zaka zama mafad'in kanka,
ni da zainab kuma duk inda zamuje na tabbatar bazamu rasa mai kwaba mana ba, kaga mummy yanzu ta canza,
matsalata daya itace "Bad----- shigowar Hinad cikin dakin ya katseta, ta kallesu tace "Nadeeyah Mummy tace kuyi sauri,
hawaye ta share ta dauki karamar jakar, Hafeez ya dauki babbar suka fito sukayi waje,
loda kayan sukayi a motar Hafeez, sannan kowa ya shiga mota,
Hinad da Nadeeyah motar Hafeez suka shiga,
makota suka kewaye su Nadeeya anata musu fatan alkhairi,
Tasi ya leko ta windon motar, ya miko mata ledar lolli pop idonshi cike da kwalla yace "ki ajiyewa Zainab, Allah ya hadaku da alkhairi Nadeeyah,
Wani kukan ta fashe dashi na tuno memories dinsu na lokacin da dukkan iyayenta suna da rai,
da irin kara kainin da sukayi tsakanin gida da shagon Tasi,
Tasi ya bada gudunmuwa mai karfi a rayuwarsu, bai taba kazawa gurin tallafa musu da bashi da kuma kyauta ba,
kallonshi tayi yana share hawaye tace "mun gode Tasi Allah ya saka maka da gidan aljanna....
Islamiyyar su Zainab suka biya dan daukota,
motar Mahmoud suka tarar a kofar makarantar,
kafin suyi parking suka hango Musaddiq rike da hannunta sun fito daga ciki,
baya ya bude mata suka shige, Mahmoud yaja motar suka wuce,
Bayansu Hafeez yabi, zuciyarshi ta dan rage zafi da fargaba saboda yasan in shaa Allahu Musaddiq da mahaifinshi bazasu bar kannenshi cikin garari ba.....
A katafaran gidan "Alhaji Mukhtar Kyari dukka motocin sukayi parking,
a firgice ta maida kanta kasa tace "waiii Mamma wannan hasken mai cutarwa ne,
bazan iya jurar kallanshi ba..
Jajircewa zakiyi Nadeeyah,
daurewa zakiyi ki fuskance shi domin bashi kadai bane,
hango wani yana fasowa a dayan gefen, duk sun kewaye taurarin dake kewaye dake da haskensu,
waigawa tayi cike da zumudi da murnar jin maganar mahaifinta,
Baba dama baka mutu ba?
kaga yadda kayi kyau kuwa,
hannuwanta ya kama yace "Tafiya ce ta kamani ta gaggawa,
kinga mahaifiyarki bata iya jure zaman, ta biyoni,
saidai dawowar mu ba mai yiwuwa bace, domin tafiyar ta din din ce,
lokacin da zakiyi wannan tafiyar baiyi ba,
yanzu lokaci ne na hakuri da jajircewa,
in kina son nasara sai kin jure,
in kina san zuciyarki tayi haske sai kinyi hakuri,
"Amma fa ba hakurin da zai cutar dake ba, cewar mamma tana murmushi tana shigewa jikin mijinta,
akwai hakuri me cutarwa ne Suwaiba,
murmushi tayi tace "akwai mana,
hakurin da kana ji kana gani a taka ka a wuce,
wannan hakurin ka iya fasa zuciya,
manzon Allah s.a.w yace "in bazaka iya hakurin abun da akayi maka ba ka rama daidai yadda akayi maka,,
"kwarai haka yake, Baba ya fadi sannan ya cigaba cewa
"ke din me nasara ce, zaki daukaka fiye da tunanin mai tunani, saidai kinsan dukkan ma'abocin daukaka yana tare da kalubale,
amma ki sani kuma kisa a ranki, a ko yaushe Allah swt yana tare dake,
karki yada Addu'a domin ita din garkuwa ce ga mu'imini...
lokacin tafiyarmu yayi,
ki kula da dukkan rayuwarki da ta yar uwarki,
sannan kiyi hakuri da dan uwanki, domin shi din mai rauni ne,
Nadeeyah tayi saurin cewa "zan biku Mamma, murmushi mai sanyin kyau sukayi mata,
suka hade baki cikin murya me kamar amsa kuwwa, sukace
"wannan tafiyar ta musamman ce, lokacin yinta a gareki baiyi ba Nadeeyah,
Tafiya suka fara yi Nadeeyah na binsu tana kuka tana fadin karku tafi ku barni,
tun tana hangensu har haske ya kara kewaye gurin,
tsayawa tayi hade da runtse ido tana kiran sunayensu hade da shashshekar kuka...
Hannun da taji kan kuncinta mai sanyin kamshi ne ya soma farkar da ita,
a hankali ta bude idonta ta saukesu kan Hinad da itama kukan takeyi..
"Sorry Nadeeyah,
kiyita karanta innalillahi wa inna ilaihir rajiun,
i know it hurts but bamu da yadda zamuyi,
addu'a itace tafi dacewa dasu a wannan lokacin,
Allahn da ya halicce su ya fimu sansu..
kawar da kai Nadeeyah tayi tana tunano hirarsu ta cikin mafarkinta,
"kunyi tafiya mai nisa Mamma,
tafiya mai dadi a gareku in shaa Allah,
sannan mai radadi a garemu,
hawayen idonta bai bar ambaliya ba ta cigaba da maganar zucin da takeyi, yanzu yaya rayuwarmu zata kasance,
shikenan bamu da wani sauran gata...
"Gatan kowa Allah ne Kanwata,
babu wani gata mai daraja, dadi, da dadadawa irin na ubangiji,
in Allah ya baiwa bawa gata, to babu wanda ya isa ya tauye ko ya kwace mishi,
mika lamarinki gurin ubangiji, kuma kiyi tawakkali kisan shi ne kadai maiyi...
saida ya kai aya Nadeeyah ta dago ta kalli gefen da yake,
tabbas zancen da takeyi a zuci ne ya fito har ya iske kunnuwanshi,
shi din ma tsaye yake idon nan nashi yayi jawur kamar gauta,
wani hawayen ya share sannan ya karaso jikin gadon da take,
zama yayi gefenta yace "ya jikin naki, runtse ido tayi ta amsa da sauki,
Allah ya baki lafiya da hakuri hade da juriya,
"Ameen yaya Musaddiq, Hinad fadi tana share mata sauran hawayen dake gefen kunnenta..
Ina Zainab take yaya Musaddiq?
Kafin Musaddiq yayi magana sukaji an murda kofar,
Hafeezu ne ya fara shigowa sai su Anty Reemah,
Hilal ne karshen shigowa shi da zainab, hannunta rike da ledojin kayan kwalama,
fuskar nan tata tayi jawur,
tana ganin Nadeeyah ta saki ledar ta karasa ta fada jikinta tana kuka,
mikewa Nadeeyah tayi a hankali sannan ta janye daga kusa da musaddiq, ta dago kan zainab tace "menene, me aka miki?
Anti Nadeeyah mamma ma ta mutu, ta tafi gurin baba,
sun dauketa sun fita da ita,
shikenan bazamu sake ganinta ba,
dariya Nadeeyah tayi tace "inji wa yace miki,
mamma bata mutu ba,
kinsan tace miki zata je Agadaz rannan ko?
Eh zainab tace tana me kallon Nadeeyah,
to can ta tafi, kina gani sun shiryata ta hau jirgi tana jin dadinta ke kuma kina nan kina kuka,
oya share hawayenki ki ji abin da mamma tace in fada miki dazu kafin ta tafi,
da sauri ta share hawayenta ta matso da kunnenta kusa da bakin Nadeeyah, rada tayi mata a kunne wanda Allah kadai yasan me tace mata, sai ko Zainab ta kyalkyace da dariya hade da rungume Nadeeyah, tace "dagaske kikeyi Anti?
Gyada kai Nadeeya tayi tace "eh,
hawayen da ta boye ne ya fara bin idanuwanta, ta kankame zainab tana zubar dasu ba tare da ta bari ta gansu ba, wayyo mutuwa.....!
@
Mrs Tijjani Shattima....!
[07/03 6:31 AM] fareedah: ●ZUMUNCINMU A YAU● 1⃣9⃣
By Aysha Ya'u Kurah
Had'a kayayyakinsu cikin jaka Nadeeyah keyi, idanuwan nan nata sai ambaliyar ruwa suke,
Hafeez ke tayata had'a kayan yana labarta mata abubuwan da suka gifta tsakaninshi da iyayensu a yan watannin da suka shude,
jan numfashi yayi kamar karamin yaro,
daga zuciya har idaniyar shi zubar ruwan hawaye sukeyi,
"yan kudaden da suka fara shigowa hannuna su suka ruda ni,
na canza abokai,
kullum bani wancan club bani wancan,
ban tsaya nan ba har sai da na koma harkar mata,
tun ina boyewa, su Baba basu sani ba har takai ga mata har gida suke biyoni,
bazan taba manta daren da zan bar gida ba,
Baba ya fito zai tafi Sallar asuba ya jiyo muryata da SAILUBA yar gidan Hinde mai tuwo,
ranar a daki na ta kwana, Koda Baba ya bude kofar, Sailuba na kwance a jikina,
duk yadda na kai ga tureta in suturta jikina ta kafe ta danneni, na kasa tabuka komai,
saida Baba ya juya, nayi karfin halin turata na mike nasa jallabiya nabi bayanshi,
Kuka na tarar dashi yana yi a tsakar gida,
a tare muka iso inda yake ni da Mamma,
ajiye butar hannunta tayi ta fara tambayarshi dalilin zubar hawayenshi,
bai kai ga yin magana ba Sailuba ta fito da daurin kirji da kayanta a hannu tana sawa tana fadin
"Zo ka sallameni Hafeezu in tafi kar a nemeni a gida,
wani irin juwa Mamma ta ji a tsakiyar kanta, bakinta da kyar yake iya furta innalillahi wa inna ilaihir rajiun, daki Baba ya jata ba tare da ya dubi inda na ke ba,
koda na biyosu ciki da sauri Baba ya dakatar dani yace
"fitar min a daki da kazantar dake jikinka,
tafi kaje ka sallameta,
ka wadata ta da duk wani nau'i na jin dadi tunda kaima ta jiyar da kai dadin,
ubangiji Allah ya shiryar dakai Ameen,
Har na iso kofar dakina ina jiyo sautin kukan mamma, Baba yana ta bata hakuri..
Da kudin da ni kaina bansan yawansu ba na sallami Sailuba,
sai na wuce nayi wanka nayi sallah,
shaidan ya dinga raya min in bar gidanmu in tafi can inda babu wanda yasanni, tunda ina da kudina inje in ci karena babu babbaka,
a haka nabi umurnin zuciyata na shirya kayana tsaff na sasu a mota,
Zainab na gani a kofar shagon Tasi, na bata dubu biyar ta kaiwa Mamma, nace ta fada musu nayi tafiya,
tun kafin ta shiga gidan na shige mota nayi gaba,
a tunanina duniyata zatayi kyau tunda babu mai samin ido,
ashe tafiyar da zata kashemin zuciya ta barni da dana sani har karshen rayuwata nayi... ya karashe maganar cikin matsanancin kuka...
Takalman Zainab Nadeeyah ta tura cikin ledar dake hannunta, wacce tun fara bata labarin ta budeta da niyyar zuba takalman,
ledar ta jike sharkaff saboda hawayen da ke sauka a kanta,
kallon Hafeez tayi tace "Yaya Allah yayi mana jarabawa mai zafin gaske,
rayuwa ce yanzu zamu fara ta wacce bamu san inda zata kaimu ba,
ka godewa Allah da yasa suka yafe maka, sannan kaji tsoron Allah,
ka nisanci duk wani aikin alfasha, kasani duk abinda zakayi yanzu za'a tada su Mamma ace su tashi suga dansu, shin irin wannan tarbiyar suka baka,
kasani yanzu babu wani wanda zai fada maka gaskiya,
rayuwa ce zakayi ta ta rashin mafadi,
kai da kanka zaka zama mafad'in kanka,
ni da zainab kuma duk inda zamuje na tabbatar bazamu rasa mai kwaba mana ba, kaga mummy yanzu ta canza,
matsalata daya itace "Bad----- shigowar Hinad cikin dakin ya katseta, ta kallesu tace "Nadeeyah Mummy tace kuyi sauri,
hawaye ta share ta dauki karamar jakar, Hafeez ya dauki babbar suka fito sukayi waje,
loda kayan sukayi a motar Hafeez, sannan kowa ya shiga mota,
Hinad da Nadeeyah motar Hafeez suka shiga,
makota suka kewaye su Nadeeya anata musu fatan alkhairi,
Tasi ya leko ta windon motar, ya miko mata ledar lolli pop idonshi cike da kwalla yace "ki ajiyewa Zainab, Allah ya hadaku da alkhairi Nadeeyah,
Wani kukan ta fashe dashi na tuno memories dinsu na lokacin da dukkan iyayenta suna da rai,
da irin kara kainin da sukayi tsakanin gida da shagon Tasi,
Tasi ya bada gudunmuwa mai karfi a rayuwarsu, bai taba kazawa gurin tallafa musu da bashi da kuma kyauta ba,
kallonshi tayi yana share hawaye tace "mun gode Tasi Allah ya saka maka da gidan aljanna....
Islamiyyar su Zainab suka biya dan daukota,
motar Mahmoud suka tarar a kofar makarantar,
kafin suyi parking suka hango Musaddiq rike da hannunta sun fito daga ciki,
baya ya bude mata suka shige, Mahmoud yaja motar suka wuce,
Bayansu Hafeez yabi, zuciyarshi ta dan rage zafi da fargaba saboda yasan in shaa Allahu Musaddiq da mahaifinshi bazasu bar kannenshi cikin garari ba.....
A katafaran gidan "Alhaji Mukhtar Kyari dukka motocin sukayi parking,