Sashe 26
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
wani kukan ne ya kufce mata na tuno saurayin da tayi arangama dashi a bikin Nafisa jiya mai cike da barkwanci da halin kirki,
a zuciyarta tana takaicin yadda yayi mata nisa ta ko wani irin bangare saboda matsayin shi,
daki taja suwaiba suka shige ta bar Goggo nata banbamin bala'inta,
itama tana takaicin bakin jinin da yaranta suke dashi,
babu irin maganin da batayi musu ba dan su samu mashin shini amma a banza,
to ita kuwa ta yaya zata yarda ta bar suwaiba ta kula samari alhali yaranta duk ba mashin shini, masifar ta cigaba dayi kamar zautacciya zuciyarta na mata zafin balbalin wuta.....
Albishirinki Ma'u!!!
Kai yau cikin farin ciki nake wallahi,
Goro ta fadi tana zuba mishi ruwa a kofi,
baibi takan ruwan ba ya kwala kiran suwaiba,
da sauri ta fito yace "akwai bako a waje kira Yayarki kuje ta rakaki, kuma kar ku dade,
cike da faduwar gaba Ma'u tace "baka ce min komai ba kuma kace yara su fita,
yanzu sai aga yara sun fita zance kai ba abin kunyar ka bane,
"shiyasa nace Zainabu ta raka ta ai, saboda idon mutane,
zuciyar ma'u kamar zata fito tace "to meye albishir din,
gyara zama yayi yace "kinajin labarin Alhaji Garba Kyari mai fata ko?, gyada kai Ma'u tayi kirjinta na tsananta bugawa,
yace "to danshi ne yaga suwaiba yake so,
kuma da aure, nace yaje ya turo magabatanshi mu tsayar da maganar aure,
wallahi Ma'u bakiji dadin da nakeji ba,
ko ba komai zan fara aurar wa, mutanen unguwa zasu bar zundena,
yake ma'u ta shiga yi tana fadin madallah Allah ya sanya alheri, Ameen.. Baffa yace ya mike ya wuce daki zuciyarshi wasai bai ko lura da yanayin ma'u ba,
shidai a yadda yakeji a ranshi, yasan suwaiba ta gama samun gatan duniya saidai kuma ta roki lahira....
Tun da suka fito Bingel tayi tozali da Mukhtar cikin kayanshi riga da wando fela,
gashin nan Afro ya tajeshi ya mike sosai, hankalinta yayi kololuwar tashi,
shine,
shine wanda ta ganshi a gidan Nafisa,
karasowa yayi gurin kafin su iso yace "barka da fitowa sahibar ruhina,
ya ilahi, suwaiba kamar zata nutse ta damki hannun yayarta hade da rufe fuskarta cikin hijab,
no, no, no,
wannan kunyar cutar dani zatayi,
kiyi hakuri ki dago kanki ki kalleni,
sakin hannun Bingel tayi ta ruga cikin gida da gudu ta barsu a waje da Bingel da tayi tsaye tana kallonshi kamar mutum mutumi,
Hannu yasa yayi kasss a fuskarta yace "ina wuni yar uwarmu,
firgigit tayi tace "ni ya kamata in fara gaisar dakai,
murmushi yayi yace "kuma sai kika barta ta gudu baki rike ta ba,
dariya tayi tace "kasan yarinya ce, kunya gareta,
amma bari in tayata tadin,
cikin nutsuwa ta dinga tambayarshi halayarshi da abubuwan daya kamata ta sani,
sun dade suna hira yana fada mata yadda yake ji a cikin rashi game da kanwarta,
da zai tafi ya bukaci ta kira mishi ita su yi sallama,
sallama tayi mishi ta wuce gida ta iske suwaiba a zaure tace "jeki kiyi sallama dashi, ko so kikeyi yayi fushi,
dakyar ta fito ta tsaya nesa dashi tace "ina wuni,
jingina yayi jikin stalet dinshi yace "bazan amsa ba,
ashe ma dai ni dodo ne ban sani ba,
rufe fuskarta ta sakeyi tace a'a kayi hakuri,
murmushi yayi yace to nayi, ya bude gaban motar ya dauko leda yace "gashi inji mamanki tace wai a kawo wa yarta,
dakyar ta karbi ledar ta ruga cikin gida da gudu,
murmushin shaukin samun farar mace kamila yayi sannan ya shiga mota ya tada ya wuce....
Bayan zuwan magabatan Mukhtar aka saka ranar aure sati biyu,
babu irin hidimar da baya ma Baffa saboda so da kaunar da yake yi ma suwaiba,
ita kuwa Bingel ramewa ta soma yi saboda tunanin mukhtar da ta sanya kanta ciki,
bangaren Ma'u kuma sai hada tuggunta takeyi wanda zai hana auren,
gori kuwa babu wanda bata sha daga makota,
da abun ya isheta ta zauna wani dare ta dinga rusar kuka, Halima da itama kishin suwaiba ya dameta ta zauna tana tayata kukan,
a haka suwaiba da ta dawo gurin mukhtar ta samesu,
kudin da ya bata ta fito dashi ta mikawa Ma'u tace "Goggo gashi yace in kawo miki kudin walima,
amsa tayi ta ajiye a gefe,
cike da fargaba tace "Goggo me ya sameki,
rungumar munafurci Ma'u tayi mata tace "Suwaiba ya zanyi da raina,
ya zanyi da gorin mutane,
yanzu kina karamar kanwar yayarki ace kinyi aure ita bata yi ba,
kinsan dole abun ya dameni,
dole ne in shiga cikin kunci da takaici saboda nasan babu wanda zai aureta yanzu, matso da ita ta kuma yi tace
"kinsan dai ni na haifeku dukkanku ko? Gyada kai Suwaiba tayi tace "eh, to yar albarka ina umurtarki da ki janye auren nan akanki ki barwa yayarki,
nasan Allah zai dubi abin alherin da kikayi ya baki wanda ya fishi,
jiki na rawa suwaiba tace "Goggo, dan Allah kiyi hakuri,
wallahi ina sonshi,
kuma shim--- ya isheni,
yanzu duk halaccin da Bingel tayi miki tun kina yarinya har kawo yanzu baki gani ba,
duk irin kaunar da ta nuna miki bazaki dubashi ki sadaukar mata da mijin da zaki aura ba,
kuka ne ya kufcewa suwaiba tace "hakkinta ne Goggo,
Hakkinta ne a matsayinta na yayata ta kula dani kuma ta sadaukar da komai nata a gareni,
wallahi da zan iya da na rabu dashi na bar mata shi amma bazan iya---- wani wawan mari Ma'u ta kai mata,
tace "lallai rashin kunyarki ta tumbatsa,
a gabana kike cewa kina son namiji,
lallai ďan da baka haifa ba dole ya nuna shi ba naka bane,
dammmmm....
suwaiba taji a kirjinta,
kalaman Goggo suka sa zuciyarta ta fara yawo a cikin ma'ajiyinta........
Mrs Tijjani Shattima
[05/03 11:10 PM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* 2⃣9⃣
By *Aysha Ya'u Kurah*
*_Duniya kurkukun mu'imuni, kuma Aljannar kafiri, akwai mutanen da Allah swt yake Halittarsu a cikin duniyar nan ba domin suji dadi ba, sai dai domin rayuwakansu su zamto izina ga wadanda sukazo domin zamanta na din din, mai hankali shi kadai yasan duniya ba gurin jin dadi bane, lahira itace matabbata, sannan akwai tarin tanadi da Allah yayi wa bayinshi masu hakuri, tanadin Allah shine tanadi Allah ya sa mu dace,_*
*RABUWA DA MASOYI*
Mikewa tayi ta isa gabanta tace "Goggo, dan Allah karki ce bake kika haifeni ba,
Kukan Munafurci Ma'u ta saki tace "Suwaiba yau kin sani na fada miki abinda ban taba tunanin fadin shi ba,
yau kin kaini makura har na fito miki da *SIRRIN BOYE*
kuka ne ya kufce ma Suwaiba tace "wacece mahaifiyata?
, a ina take?,
nan take shaukin son taga mahaifiyarta yazo cikin zuciyarta,
rungemeta Ma'u tayi sosai tace "Tambayar bata da amfani tunda bata raye,
ni nan ni na raine ki tun kina jarinta da taimakon yayarki,
munsha gwargwarmayar rayuwa gurin baki tarbiyya,
musamman yayar taki da kike yunkurin k'in sadaukar mata da soyayyarki,
cikin kuka suwaiba tace "innalillahi wa inna ilaihir rajiun, kara kankameta Ma'u tayi tace "duk abin da kika ga na miki a baya bawai dan bana sanki bane, nayi shi ne dan samar miki tarbiyya mai kyau da amfani,
kiyi hakuri,
kiyi hakuri ki bar mata,
"labarin karya ta shirya mata akan mahaifiyarta sannan ta karashe da fadin irin kular da zainab din tayi mata,
kukan bai fasa zubowa a idonta ba tace "Allah ya jikan mahaifiyata Goggo, Ameen Ma'u ta fadi sannan tace "nasan zaki bar ma yar uwarki mijin da zaki aura ko? Nasan zuciyar zinari gareki,
girgiza kai Suwaiba tayi tace a'a Goggo,
yaudara ce wannan,
bazan iya hakuri da shi ba,
domin kuwa Allah sai ya tambayeni,
yasa rai da aurena kuma kawai sai in ce mishi ya auri yayata,
hakan bazai yiwu ba,
tana karashe fadi hade da tashi ta fita zuciyarta na tariyo mata irin ukubar da tasha a hannun Goggo,
ba tun yau take tunanin cewa ba Goggo bace ta haifeta,
gashi yau sanadiyyar Mukhtar an warware mata komai,
hawayen idonta ta share dan tasan in shaa Allahu ta kusa daina zubda su,
tasan Mukhtar zai zame mata komai da ta rasa a rayuwa..
Dakinsu ta shiga jiki a sanyaye,
a zaune ta tarar da zainab da ta gama sauraron duk abinda suke cewa,
tafarfasa zuciyarta takeyi saboda yadda ta dauka Suwaiba zata iya barin mata komai take bukata a rayuwa,
lallai a yanzu ne ta fahimci cewa uwa daya ya wuce wasa,
tayi imanin da Leemah ce zata yarda ta barta Mukhtar dan kar ta kunyata,
wata irin tsanar Suwaiba ce ta darsu a zuciyar zainab wacce dama ta dade ana mata aikenta, sai yanzu shaidan ya samar mata mazauni a zuciyarta,
barka da hutawa yaya, suwaiba ta fadi tana cire hijab dinta,
uhmmm!!
kawai taji tace sannan ta mike kafarta a kan gado,
gabanta ne ya fadi dan bata saba ganin hakan a gurin yar uwarta ba,
gefen gadon taje ta tsuguna tace "yaya ko na miki wani abu ne,
juya mata baya tayi tace "karki dameni suwaiba,
kaina ke ciwo,
nan take idonta ya ciko da kwalla ta mike ta fita kofar dakin,
kuka sosai ta zauna tana yi, zuciyarta sai kai kawo takeyi akan maganar da Goggo tayi mata,
sam bata damu da sanin cewa ba ita ta haifeta ba, dan ta dade da sanin uwar da ta haifeka baza tayi maka irin wannan tsanar ba,
abin kawai da ya daga hankalinta shine rashin sanin uwarta da kuma rashin adduar da bata samu daga gareta a matsayin sadaka a kabarinta..
yanzu kuma babban tashin hankalinta bai wuce na rashin walwalar da ta gani a gurin yar uwarta mai kaunarta ba,
tana wannan tunanin taji Ma'u tazo ta wuce cikin dakin...
a zuciyarta tana takaicin yadda yayi mata nisa ta ko wani irin bangare saboda matsayin shi,
daki taja suwaiba suka shige ta bar Goggo nata banbamin bala'inta,
itama tana takaicin bakin jinin da yaranta suke dashi,
babu irin maganin da batayi musu ba dan su samu mashin shini amma a banza,
to ita kuwa ta yaya zata yarda ta bar suwaiba ta kula samari alhali yaranta duk ba mashin shini, masifar ta cigaba dayi kamar zautacciya zuciyarta na mata zafin balbalin wuta.....
Albishirinki Ma'u!!!
Kai yau cikin farin ciki nake wallahi,
Goro ta fadi tana zuba mishi ruwa a kofi,
baibi takan ruwan ba ya kwala kiran suwaiba,
da sauri ta fito yace "akwai bako a waje kira Yayarki kuje ta rakaki, kuma kar ku dade,
cike da faduwar gaba Ma'u tace "baka ce min komai ba kuma kace yara su fita,
yanzu sai aga yara sun fita zance kai ba abin kunyar ka bane,
"shiyasa nace Zainabu ta raka ta ai, saboda idon mutane,
zuciyar ma'u kamar zata fito tace "to meye albishir din,
gyara zama yayi yace "kinajin labarin Alhaji Garba Kyari mai fata ko?, gyada kai Ma'u tayi kirjinta na tsananta bugawa,
yace "to danshi ne yaga suwaiba yake so,
kuma da aure, nace yaje ya turo magabatanshi mu tsayar da maganar aure,
wallahi Ma'u bakiji dadin da nakeji ba,
ko ba komai zan fara aurar wa, mutanen unguwa zasu bar zundena,
yake ma'u ta shiga yi tana fadin madallah Allah ya sanya alheri, Ameen.. Baffa yace ya mike ya wuce daki zuciyarshi wasai bai ko lura da yanayin ma'u ba,
shidai a yadda yakeji a ranshi, yasan suwaiba ta gama samun gatan duniya saidai kuma ta roki lahira....
Tun da suka fito Bingel tayi tozali da Mukhtar cikin kayanshi riga da wando fela,
gashin nan Afro ya tajeshi ya mike sosai, hankalinta yayi kololuwar tashi,
shine,
shine wanda ta ganshi a gidan Nafisa,
karasowa yayi gurin kafin su iso yace "barka da fitowa sahibar ruhina,
ya ilahi, suwaiba kamar zata nutse ta damki hannun yayarta hade da rufe fuskarta cikin hijab,
no, no, no,
wannan kunyar cutar dani zatayi,
kiyi hakuri ki dago kanki ki kalleni,
sakin hannun Bingel tayi ta ruga cikin gida da gudu ta barsu a waje da Bingel da tayi tsaye tana kallonshi kamar mutum mutumi,
Hannu yasa yayi kasss a fuskarta yace "ina wuni yar uwarmu,
firgigit tayi tace "ni ya kamata in fara gaisar dakai,
murmushi yayi yace "kuma sai kika barta ta gudu baki rike ta ba,
dariya tayi tace "kasan yarinya ce, kunya gareta,
amma bari in tayata tadin,
cikin nutsuwa ta dinga tambayarshi halayarshi da abubuwan daya kamata ta sani,
sun dade suna hira yana fada mata yadda yake ji a cikin rashi game da kanwarta,
da zai tafi ya bukaci ta kira mishi ita su yi sallama,
sallama tayi mishi ta wuce gida ta iske suwaiba a zaure tace "jeki kiyi sallama dashi, ko so kikeyi yayi fushi,
dakyar ta fito ta tsaya nesa dashi tace "ina wuni,
jingina yayi jikin stalet dinshi yace "bazan amsa ba,
ashe ma dai ni dodo ne ban sani ba,
rufe fuskarta ta sakeyi tace a'a kayi hakuri,
murmushi yayi yace to nayi, ya bude gaban motar ya dauko leda yace "gashi inji mamanki tace wai a kawo wa yarta,
dakyar ta karbi ledar ta ruga cikin gida da gudu,
murmushin shaukin samun farar mace kamila yayi sannan ya shiga mota ya tada ya wuce....
Bayan zuwan magabatan Mukhtar aka saka ranar aure sati biyu,
babu irin hidimar da baya ma Baffa saboda so da kaunar da yake yi ma suwaiba,
ita kuwa Bingel ramewa ta soma yi saboda tunanin mukhtar da ta sanya kanta ciki,
bangaren Ma'u kuma sai hada tuggunta takeyi wanda zai hana auren,
gori kuwa babu wanda bata sha daga makota,
da abun ya isheta ta zauna wani dare ta dinga rusar kuka, Halima da itama kishin suwaiba ya dameta ta zauna tana tayata kukan,
a haka suwaiba da ta dawo gurin mukhtar ta samesu,
kudin da ya bata ta fito dashi ta mikawa Ma'u tace "Goggo gashi yace in kawo miki kudin walima,
amsa tayi ta ajiye a gefe,
cike da fargaba tace "Goggo me ya sameki,
rungumar munafurci Ma'u tayi mata tace "Suwaiba ya zanyi da raina,
ya zanyi da gorin mutane,
yanzu kina karamar kanwar yayarki ace kinyi aure ita bata yi ba,
kinsan dole abun ya dameni,
dole ne in shiga cikin kunci da takaici saboda nasan babu wanda zai aureta yanzu, matso da ita ta kuma yi tace
"kinsan dai ni na haifeku dukkanku ko? Gyada kai Suwaiba tayi tace "eh, to yar albarka ina umurtarki da ki janye auren nan akanki ki barwa yayarki,
nasan Allah zai dubi abin alherin da kikayi ya baki wanda ya fishi,
jiki na rawa suwaiba tace "Goggo, dan Allah kiyi hakuri,
wallahi ina sonshi,
kuma shim--- ya isheni,
yanzu duk halaccin da Bingel tayi miki tun kina yarinya har kawo yanzu baki gani ba,
duk irin kaunar da ta nuna miki bazaki dubashi ki sadaukar mata da mijin da zaki aura ba,
kuka ne ya kufcewa suwaiba tace "hakkinta ne Goggo,
Hakkinta ne a matsayinta na yayata ta kula dani kuma ta sadaukar da komai nata a gareni,
wallahi da zan iya da na rabu dashi na bar mata shi amma bazan iya---- wani wawan mari Ma'u ta kai mata,
tace "lallai rashin kunyarki ta tumbatsa,
a gabana kike cewa kina son namiji,
lallai ďan da baka haifa ba dole ya nuna shi ba naka bane,
dammmmm....
suwaiba taji a kirjinta,
kalaman Goggo suka sa zuciyarta ta fara yawo a cikin ma'ajiyinta........
Mrs Tijjani Shattima
[05/03 11:10 PM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* 2⃣9⃣
By *Aysha Ya'u Kurah*
*_Duniya kurkukun mu'imuni, kuma Aljannar kafiri, akwai mutanen da Allah swt yake Halittarsu a cikin duniyar nan ba domin suji dadi ba, sai dai domin rayuwakansu su zamto izina ga wadanda sukazo domin zamanta na din din, mai hankali shi kadai yasan duniya ba gurin jin dadi bane, lahira itace matabbata, sannan akwai tarin tanadi da Allah yayi wa bayinshi masu hakuri, tanadin Allah shine tanadi Allah ya sa mu dace,_*
*RABUWA DA MASOYI*
Mikewa tayi ta isa gabanta tace "Goggo, dan Allah karki ce bake kika haifeni ba,
Kukan Munafurci Ma'u ta saki tace "Suwaiba yau kin sani na fada miki abinda ban taba tunanin fadin shi ba,
yau kin kaini makura har na fito miki da *SIRRIN BOYE*
kuka ne ya kufce ma Suwaiba tace "wacece mahaifiyata?
, a ina take?,
nan take shaukin son taga mahaifiyarta yazo cikin zuciyarta,
rungemeta Ma'u tayi sosai tace "Tambayar bata da amfani tunda bata raye,
ni nan ni na raine ki tun kina jarinta da taimakon yayarki,
munsha gwargwarmayar rayuwa gurin baki tarbiyya,
musamman yayar taki da kike yunkurin k'in sadaukar mata da soyayyarki,
cikin kuka suwaiba tace "innalillahi wa inna ilaihir rajiun, kara kankameta Ma'u tayi tace "duk abin da kika ga na miki a baya bawai dan bana sanki bane, nayi shi ne dan samar miki tarbiyya mai kyau da amfani,
kiyi hakuri,
kiyi hakuri ki bar mata,
"labarin karya ta shirya mata akan mahaifiyarta sannan ta karashe da fadin irin kular da zainab din tayi mata,
kukan bai fasa zubowa a idonta ba tace "Allah ya jikan mahaifiyata Goggo, Ameen Ma'u ta fadi sannan tace "nasan zaki bar ma yar uwarki mijin da zaki aura ko? Nasan zuciyar zinari gareki,
girgiza kai Suwaiba tayi tace a'a Goggo,
yaudara ce wannan,
bazan iya hakuri da shi ba,
domin kuwa Allah sai ya tambayeni,
yasa rai da aurena kuma kawai sai in ce mishi ya auri yayata,
hakan bazai yiwu ba,
tana karashe fadi hade da tashi ta fita zuciyarta na tariyo mata irin ukubar da tasha a hannun Goggo,
ba tun yau take tunanin cewa ba Goggo bace ta haifeta,
gashi yau sanadiyyar Mukhtar an warware mata komai,
hawayen idonta ta share dan tasan in shaa Allahu ta kusa daina zubda su,
tasan Mukhtar zai zame mata komai da ta rasa a rayuwa..
Dakinsu ta shiga jiki a sanyaye,
a zaune ta tarar da zainab da ta gama sauraron duk abinda suke cewa,
tafarfasa zuciyarta takeyi saboda yadda ta dauka Suwaiba zata iya barin mata komai take bukata a rayuwa,
lallai a yanzu ne ta fahimci cewa uwa daya ya wuce wasa,
tayi imanin da Leemah ce zata yarda ta barta Mukhtar dan kar ta kunyata,
wata irin tsanar Suwaiba ce ta darsu a zuciyar zainab wacce dama ta dade ana mata aikenta, sai yanzu shaidan ya samar mata mazauni a zuciyarta,
barka da hutawa yaya, suwaiba ta fadi tana cire hijab dinta,
uhmmm!!
kawai taji tace sannan ta mike kafarta a kan gado,
gabanta ne ya fadi dan bata saba ganin hakan a gurin yar uwarta ba,
gefen gadon taje ta tsuguna tace "yaya ko na miki wani abu ne,
juya mata baya tayi tace "karki dameni suwaiba,
kaina ke ciwo,
nan take idonta ya ciko da kwalla ta mike ta fita kofar dakin,
kuka sosai ta zauna tana yi, zuciyarta sai kai kawo takeyi akan maganar da Goggo tayi mata,
sam bata damu da sanin cewa ba ita ta haifeta ba, dan ta dade da sanin uwar da ta haifeka baza tayi maka irin wannan tsanar ba,
abin kawai da ya daga hankalinta shine rashin sanin uwarta da kuma rashin adduar da bata samu daga gareta a matsayin sadaka a kabarinta..
yanzu kuma babban tashin hankalinta bai wuce na rashin walwalar da ta gani a gurin yar uwarta mai kaunarta ba,
tana wannan tunanin taji Ma'u tazo ta wuce cikin dakin...