Sashe 76
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"ki kama jikinki Nadeeyah,
ki sa ruwan zafi da gishiri ki zauna a ciki,
sannan kisha tea mai zafi ki hada da paracetamol,
kina yin hakan zakiji sauki,
Allah ya kara lafiya,
karki raga mishi ki bashi wahala kamar yadda ya baki kinji ko,
Murmushin karfin hali Nadeeyah tayi tace
"nagode Anty,
ki gaida min su Hinad, "zasuji my sister,
ki kula sosai da mijinki da kanki, yanzu ku biyun nan kune sirrin juna,
ku kare ma kanku mutunci,
in abu ya dameki ki sameshi ki fada mishi,
ku tattala rayuwarku ke da shi,
Allah ya baku zaman lafiya, "Ameen Anty nagode sosai,
"bakomai dear,
a tashi a kama jiki, sai na jiki,
bata jira amsarta ba ta kashe wayar, ta cigaba da ayyukan gida....
Taimaka mata yayi ta koma bayin sannan ya fito ya sanya jallabiya ya fita da sauri dan nemo magunguna da abun karyawa,
ko kallon inda su Raudha suke baiyi ba,
hakan ba karamin dugunzumasu yayi ba suka mike suka nufi dakin da Nadeeyar take..
Jin karan ruwa ya sa su bude bayin a isgilance,
yadda ruwan ke shiganta yasata lumshe ido tana jin wani dadi na ratsata,
jin muryar Raudha da tayi babu zato shi ya sanyata bude kumburarrun idanuwanta,
kallon da suke mata ne ya sa cikinta kartawa ta fara rawar baki tana fadin
"ina kwananku,
"Lafiya kalau karuwar karshen zamani,
yadda maganar ta fito babu control ya sanya Nadeeyah jin wani irin bakin cikin da bata taba ji a kalamansu ba,
sunsha zaginta da kalamai marasa daďi amma wannan shine zagi mafi muni da taba cin karo dashi daga garesu,
maida kwallar idonta tayi ta dauke kanta a kansu,
Nan fa suka cigaba da zaginta suna aibata ta kamar wadanda sukeyi da sa'arsu,
kalamansu na batanci yana matukar sosa mata rai,
amma haka nan ta danne ta maida hawayenta haďe da fitowa ta dauki towel ta nade jikinta dashi saboda girmanshi,
bata sake kallon inda suke ba tayi hanyar fita daga bayin a dan hanzarce duk da tana jin zafin jikinta,
ta kama kofar kenan zata murda Raudha ta janyota haďe da dauke fuskarta da mari,
"Dan ubanki mu zaki mayar mahaukata,
mu zaki bawa banza ajiya,
ke har kin isa muna miki magana ki sanya kafarki kiyi waje saboda tsabar raini,
cike da masifa Radiya ta karbe da cewa
"kinga laifin yar matsiyata marasa asali,
Allah kadai yasan daga inda ubanta ya fito har muka haďa jibi da matsiyata irin su masu siffar munafukai,
wallahi tallahi in bakiyi dalilin da little ya sakeki ba sai mun sanya bakin ciki ya zama ajalinki,
ki fara counting days dinki, dan zuwan Badar da Faida bazai taba zama abu mai dadi a gareki ba,
shegiya yar iska,
mai sakin jiki gurin namiji a daren farko,
"kukan da Nadeeyah takeyi a wannan lokacin mai sauti ne, dan kalamansu yafi mari ciwo a gareta,
kalmar rashin asali da ake yawan fadinta a garesu yana matukar taba mata zuciya,
gaba daya ji tayi ta tsani zaman duniyan ma,
da Allah zai dauki ranta a lokacin da kowa ya huta da kwasarma kanshi zunubi akanta,
har suka gama zagi da aibata ta bata dago kai ta dubesu ba kuma bata fasa kukan da takeyi ba,
da suka gaji sai suka dungure mata kai da karfi haďe furta wani mugun zagi ga matattun iyayenta,
nan kofar bayin ta durkushe tana kuka mai sosa rai...
A gigice ya ajiye kayan da ya shigo dasu ya nufi bayin a hanzarce,
da sauri ya ďago ta kamar yar baby ya nufi cikin dakin da ita, duk tunaninshi ciwon ne ke damunta,
ajiyeta yayi duk ya ruďe yace
"bari in dauko miki riga muje asibiti,
bazan iya jure ganin kukan nan ba,
girgiza mishi kai tayi murya a dashe tace
"Naji sauki,
bana jin ciwon komai,
"to meyasa ki kuka?, ya tambaya cike da damuwa haďe da kwantar da kanshi kan hannunta da ya dau zafi sosai,
"Dan Allah yaya Musaddiq ka sakeni!!!
Yadda yaji maganar kamar an soka mishi mashi ya sanyashi ďagowa ya kalli cikin idonta da yayi jawur,
a hankali ya mike ya zauna sosai kusa da ita haďe da dagota itama ta zauna,
"Kiyi hakuri,
nasan na miki laifi sosai,
na wahalar dake kuma na saki kuka,
bazan kara yi miki komai ba in shaa Allah,
"dan Allah karki kara yin maganar rabuwar mu,
plsss...
ya karashe yana mai shafo gefen fuskarta,
tausayi sosai ya bata tayi saurin kauda kanta gefe,
bata da karfin gwiwar fada mishi dalilinta na san rabuwarsu,
yan uwanshi da mahaifiyarshi basa kaunar auren nan,
da zaiji ta tata da sun rabu ko hankulansu zai kwanta,
hannu yasa ya share mata hawaye ndake gangaro mata yace
"komai zaiyi daidai kinji,
bari in baki breakfast sai ki sha magani kiyi bacci.......
Ajiyar zuciya Marakisiyya tayi bayan ta gama sauraron labarin Badar,
ta tausaya mata matuka na ganin ta rabu da abin da take so lokaci kalilan kuma shi yana can yana jin dadinshi da wata,
nan ta tambayi Badar tana son ta taimaketa ne ta koma gida, ko kuwa so takeyi ta zauna anan ta koya mata sihirin da ta koya a gurinsu wanda zai sanyata tayi gaggawar rabasu,
zuciya marar kashi,
Badariyya bata dubi halin da take ciki ba tayi saurin cewa tana son koyon sihirin,
dariya Marakisiyya tayi a ranta tace
"dama so nakeyi ki koya mu hadu mu biyu mu tada Rugar gaba dayanta sannan mu nemi hanyar garuruwanmu,
a fili kuma ce mata tayi
"an gama,
wasu guraye ta fiddo daga jikinta ta mikawa Badar tace ta rufe idonta,
tana rufe idonta ta fara ganin kanta cikin wani sururin guri mai tsananin ban tsoro,
nan fa ta dada runtseshi haďe da kankame Marakisiyya tana ihu sosai,
bakinta Marakisiyya ta toshe dan sam bata so asan abun da takeyi,
sai da sukayi kusan minti 30 a haka sannan Marakisiyya ta kwace gurayen,
Wuri wuri Badar tayi da idanuwanta saboda tsananin tsoro,
"Kin tsorata ko?
Gyaďa kai kawai tayi tana fitar da numfashin wahala,
Wata dariyar Marakisiyya ta sake yi tace
"Lokacin jin tsoro ya wuce, nan ta kwance wata leda ta cigaba da cewa
"dafi kasar nan ki ayyana abu a ranki,
zaki ga duk abinda kike yana dawo miki kamar a mafarki, (tayi mata haka ne dan ta kara zura jiki da ita ta)..
*HUSNA*
ce ta faďo mata a rai wanda a sonta rayuwar su Musaddiq taso fara gani,
tana runtse idanuwanta komai na Husnah ya fara yi mata yawo kamar a film,
"Zaune ta gansu a kayataccen parlonsu Husnah na zuba ma Hafeez shagwaba yana rarrashinta,
komai na gidan su madaidaici gunin sha'awa,
babu abin da yafi girgizata ya sanyata cikin bakin kishi kamar ganin yadda fuskar Hafeez ke mata kwarjini da kuma girma kamar wani sarki mai daraja,
Saboda sabon shiga ce cikin sihirin shi ya hanata gano muhimmin abun dake tattare da Hafeez,
amma tabbas taga alamu na sarauta mai girma a tare dashi....
Saida ta gama duba lafiyar kowa taga duk suna harkarsu ba tare da sun damu da bacewarta ba,
Sai ta koma kan wanda take mammako da tsoron duba nasu,
aiko tayi mugun gamo,
domin kuwa yadda ta gansu a manne da juna ya 'ballo magani yana bata cike da rarrashi haďe da kwantar da ita a jikinshi ba karamin kai ganinta kasa yayi ba,
kankancewa idanuwanta sukayi haďe da yin jawur kamar gauta,
nan tayi saurin cire hannunta a kasar sihirin da Marakisiyya ta bata,
mikewa tayi tana safa da marwah haďe da cin alwashin rabasu kuma ta kashe Nadeeyar gaba daya,
Wannan shiga gonarta da Nadeeyah tayi wallahi sai tayi paying da rayuwarta,
Cikin kwarewa Marakisiyya ta koya mata duk wasu nau'i na tsafi haďe da bata wasu abubuwan da zata sha tayi wanka dasu,
"Hatsabibanci Marakisiyya ya sata koyon duk abubuwan a gidan,
ko ina kewayawa takeyi tana koyo haďe da haďa su da kanta,
duk yadda aka kai ga tsoron manyan gidan Marakisiyya bata wannan domin ga da ga zata zagesu tass,
shiyasa aka koma sa mata bulala a jiki,
ta zame musu karfen kafa,
basa iyawa da ita,
Tun ranar da taga Badariyya ta shin shino barinta gidan da taimakon Badariyya,
shiyasa tayi saurin shigar mata da bukatarta kafin ma a samu wata a gidan ta shige mata....
Mrs Tijjani Shattimah....
[20/04 4:18 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 6⃣0⃣
By *Aysha Ya'u kurah*
Cikin shashshekar kuka take tambayar doctorn abin da ke damun ďanta,
yanayin ruďewar da take ciki ya sanya doctorn dawowa kujerar kusa da ita,
"Calm down Ma'am,
"ba wani serious abu bane,
kawai damuwa ce da rashin cin abinci ya sanya shi zama weak, but with time zai samu sauki in ya kiyaye,
ko da baya san cin abinci atleast ya dinga ci ko kadan ne at the right time,
sannan ya daina damuwa ko yaya take,
thank Goodness bai taba zuciyarshi ba,
but yaso yayi affecting dinta,
plss ya kiyaye sosai cos life is very precious...
Wasu zafafan hawaye ne suka biyo ta gefen idonshi bayan ya gama sauraron abin da doctorn ya faďi
"Life is nothing without Nadeeyah,
ya Allah ka sassauta min..
Hannu Anty Saude tasa ta share mishi hawayen itama ta share nata sannan tayi ma doctorn godiya ta kuma yi mishi alkawarin kiyaye duk abinda yace mata,
har bakin kofa ta rakashi sannan ta wuce kitchen rai a bace,
Wani maganin kwari mai karfin gaske ta dauko haďe da juice ta dawo kusa da Taheer ta zauna, yana kallonta ta ďure maganin a ciki,
a hankali ya mike yana tambayarta abun da zatayi dashi,
ko kallon inda yake batayi ba ta daga juice din zata kaishi bakinta,
Wani irin karfi yaji a jikinshi haďe kabe juice din a hannunta, baki na rawa yace
"Are u out of ur senses,
poison ne fa,
so kikeyi ki kashe kanki?
ki sa ruwan zafi da gishiri ki zauna a ciki,
sannan kisha tea mai zafi ki hada da paracetamol,
kina yin hakan zakiji sauki,
Allah ya kara lafiya,
karki raga mishi ki bashi wahala kamar yadda ya baki kinji ko,
Murmushin karfin hali Nadeeyah tayi tace
"nagode Anty,
ki gaida min su Hinad, "zasuji my sister,
ki kula sosai da mijinki da kanki, yanzu ku biyun nan kune sirrin juna,
ku kare ma kanku mutunci,
in abu ya dameki ki sameshi ki fada mishi,
ku tattala rayuwarku ke da shi,
Allah ya baku zaman lafiya, "Ameen Anty nagode sosai,
"bakomai dear,
a tashi a kama jiki, sai na jiki,
bata jira amsarta ba ta kashe wayar, ta cigaba da ayyukan gida....
Taimaka mata yayi ta koma bayin sannan ya fito ya sanya jallabiya ya fita da sauri dan nemo magunguna da abun karyawa,
ko kallon inda su Raudha suke baiyi ba,
hakan ba karamin dugunzumasu yayi ba suka mike suka nufi dakin da Nadeeyar take..
Jin karan ruwa ya sa su bude bayin a isgilance,
yadda ruwan ke shiganta yasata lumshe ido tana jin wani dadi na ratsata,
jin muryar Raudha da tayi babu zato shi ya sanyata bude kumburarrun idanuwanta,
kallon da suke mata ne ya sa cikinta kartawa ta fara rawar baki tana fadin
"ina kwananku,
"Lafiya kalau karuwar karshen zamani,
yadda maganar ta fito babu control ya sanya Nadeeyah jin wani irin bakin cikin da bata taba ji a kalamansu ba,
sunsha zaginta da kalamai marasa daďi amma wannan shine zagi mafi muni da taba cin karo dashi daga garesu,
maida kwallar idonta tayi ta dauke kanta a kansu,
Nan fa suka cigaba da zaginta suna aibata ta kamar wadanda sukeyi da sa'arsu,
kalamansu na batanci yana matukar sosa mata rai,
amma haka nan ta danne ta maida hawayenta haďe da fitowa ta dauki towel ta nade jikinta dashi saboda girmanshi,
bata sake kallon inda suke ba tayi hanyar fita daga bayin a dan hanzarce duk da tana jin zafin jikinta,
ta kama kofar kenan zata murda Raudha ta janyota haďe da dauke fuskarta da mari,
"Dan ubanki mu zaki mayar mahaukata,
mu zaki bawa banza ajiya,
ke har kin isa muna miki magana ki sanya kafarki kiyi waje saboda tsabar raini,
cike da masifa Radiya ta karbe da cewa
"kinga laifin yar matsiyata marasa asali,
Allah kadai yasan daga inda ubanta ya fito har muka haďa jibi da matsiyata irin su masu siffar munafukai,
wallahi tallahi in bakiyi dalilin da little ya sakeki ba sai mun sanya bakin ciki ya zama ajalinki,
ki fara counting days dinki, dan zuwan Badar da Faida bazai taba zama abu mai dadi a gareki ba,
shegiya yar iska,
mai sakin jiki gurin namiji a daren farko,
"kukan da Nadeeyah takeyi a wannan lokacin mai sauti ne, dan kalamansu yafi mari ciwo a gareta,
kalmar rashin asali da ake yawan fadinta a garesu yana matukar taba mata zuciya,
gaba daya ji tayi ta tsani zaman duniyan ma,
da Allah zai dauki ranta a lokacin da kowa ya huta da kwasarma kanshi zunubi akanta,
har suka gama zagi da aibata ta bata dago kai ta dubesu ba kuma bata fasa kukan da takeyi ba,
da suka gaji sai suka dungure mata kai da karfi haďe furta wani mugun zagi ga matattun iyayenta,
nan kofar bayin ta durkushe tana kuka mai sosa rai...
A gigice ya ajiye kayan da ya shigo dasu ya nufi bayin a hanzarce,
da sauri ya ďago ta kamar yar baby ya nufi cikin dakin da ita, duk tunaninshi ciwon ne ke damunta,
ajiyeta yayi duk ya ruďe yace
"bari in dauko miki riga muje asibiti,
bazan iya jure ganin kukan nan ba,
girgiza mishi kai tayi murya a dashe tace
"Naji sauki,
bana jin ciwon komai,
"to meyasa ki kuka?, ya tambaya cike da damuwa haďe da kwantar da kanshi kan hannunta da ya dau zafi sosai,
"Dan Allah yaya Musaddiq ka sakeni!!!
Yadda yaji maganar kamar an soka mishi mashi ya sanyashi ďagowa ya kalli cikin idonta da yayi jawur,
a hankali ya mike ya zauna sosai kusa da ita haďe da dagota itama ta zauna,
"Kiyi hakuri,
nasan na miki laifi sosai,
na wahalar dake kuma na saki kuka,
bazan kara yi miki komai ba in shaa Allah,
"dan Allah karki kara yin maganar rabuwar mu,
plsss...
ya karashe yana mai shafo gefen fuskarta,
tausayi sosai ya bata tayi saurin kauda kanta gefe,
bata da karfin gwiwar fada mishi dalilinta na san rabuwarsu,
yan uwanshi da mahaifiyarshi basa kaunar auren nan,
da zaiji ta tata da sun rabu ko hankulansu zai kwanta,
hannu yasa ya share mata hawaye ndake gangaro mata yace
"komai zaiyi daidai kinji,
bari in baki breakfast sai ki sha magani kiyi bacci.......
Ajiyar zuciya Marakisiyya tayi bayan ta gama sauraron labarin Badar,
ta tausaya mata matuka na ganin ta rabu da abin da take so lokaci kalilan kuma shi yana can yana jin dadinshi da wata,
nan ta tambayi Badar tana son ta taimaketa ne ta koma gida, ko kuwa so takeyi ta zauna anan ta koya mata sihirin da ta koya a gurinsu wanda zai sanyata tayi gaggawar rabasu,
zuciya marar kashi,
Badariyya bata dubi halin da take ciki ba tayi saurin cewa tana son koyon sihirin,
dariya Marakisiyya tayi a ranta tace
"dama so nakeyi ki koya mu hadu mu biyu mu tada Rugar gaba dayanta sannan mu nemi hanyar garuruwanmu,
a fili kuma ce mata tayi
"an gama,
wasu guraye ta fiddo daga jikinta ta mikawa Badar tace ta rufe idonta,
tana rufe idonta ta fara ganin kanta cikin wani sururin guri mai tsananin ban tsoro,
nan fa ta dada runtseshi haďe da kankame Marakisiyya tana ihu sosai,
bakinta Marakisiyya ta toshe dan sam bata so asan abun da takeyi,
sai da sukayi kusan minti 30 a haka sannan Marakisiyya ta kwace gurayen,
Wuri wuri Badar tayi da idanuwanta saboda tsananin tsoro,
"Kin tsorata ko?
Gyaďa kai kawai tayi tana fitar da numfashin wahala,
Wata dariyar Marakisiyya ta sake yi tace
"Lokacin jin tsoro ya wuce, nan ta kwance wata leda ta cigaba da cewa
"dafi kasar nan ki ayyana abu a ranki,
zaki ga duk abinda kike yana dawo miki kamar a mafarki, (tayi mata haka ne dan ta kara zura jiki da ita ta)..
*HUSNA*
ce ta faďo mata a rai wanda a sonta rayuwar su Musaddiq taso fara gani,
tana runtse idanuwanta komai na Husnah ya fara yi mata yawo kamar a film,
"Zaune ta gansu a kayataccen parlonsu Husnah na zuba ma Hafeez shagwaba yana rarrashinta,
komai na gidan su madaidaici gunin sha'awa,
babu abin da yafi girgizata ya sanyata cikin bakin kishi kamar ganin yadda fuskar Hafeez ke mata kwarjini da kuma girma kamar wani sarki mai daraja,
Saboda sabon shiga ce cikin sihirin shi ya hanata gano muhimmin abun dake tattare da Hafeez,
amma tabbas taga alamu na sarauta mai girma a tare dashi....
Saida ta gama duba lafiyar kowa taga duk suna harkarsu ba tare da sun damu da bacewarta ba,
Sai ta koma kan wanda take mammako da tsoron duba nasu,
aiko tayi mugun gamo,
domin kuwa yadda ta gansu a manne da juna ya 'ballo magani yana bata cike da rarrashi haďe da kwantar da ita a jikinshi ba karamin kai ganinta kasa yayi ba,
kankancewa idanuwanta sukayi haďe da yin jawur kamar gauta,
nan tayi saurin cire hannunta a kasar sihirin da Marakisiyya ta bata,
mikewa tayi tana safa da marwah haďe da cin alwashin rabasu kuma ta kashe Nadeeyar gaba daya,
Wannan shiga gonarta da Nadeeyah tayi wallahi sai tayi paying da rayuwarta,
Cikin kwarewa Marakisiyya ta koya mata duk wasu nau'i na tsafi haďe da bata wasu abubuwan da zata sha tayi wanka dasu,
"Hatsabibanci Marakisiyya ya sata koyon duk abubuwan a gidan,
ko ina kewayawa takeyi tana koyo haďe da haďa su da kanta,
duk yadda aka kai ga tsoron manyan gidan Marakisiyya bata wannan domin ga da ga zata zagesu tass,
shiyasa aka koma sa mata bulala a jiki,
ta zame musu karfen kafa,
basa iyawa da ita,
Tun ranar da taga Badariyya ta shin shino barinta gidan da taimakon Badariyya,
shiyasa tayi saurin shigar mata da bukatarta kafin ma a samu wata a gidan ta shige mata....
Mrs Tijjani Shattimah....
[20/04 4:18 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 6⃣0⃣
By *Aysha Ya'u kurah*
Cikin shashshekar kuka take tambayar doctorn abin da ke damun ďanta,
yanayin ruďewar da take ciki ya sanya doctorn dawowa kujerar kusa da ita,
"Calm down Ma'am,
"ba wani serious abu bane,
kawai damuwa ce da rashin cin abinci ya sanya shi zama weak, but with time zai samu sauki in ya kiyaye,
ko da baya san cin abinci atleast ya dinga ci ko kadan ne at the right time,
sannan ya daina damuwa ko yaya take,
thank Goodness bai taba zuciyarshi ba,
but yaso yayi affecting dinta,
plss ya kiyaye sosai cos life is very precious...
Wasu zafafan hawaye ne suka biyo ta gefen idonshi bayan ya gama sauraron abin da doctorn ya faďi
"Life is nothing without Nadeeyah,
ya Allah ka sassauta min..
Hannu Anty Saude tasa ta share mishi hawayen itama ta share nata sannan tayi ma doctorn godiya ta kuma yi mishi alkawarin kiyaye duk abinda yace mata,
har bakin kofa ta rakashi sannan ta wuce kitchen rai a bace,
Wani maganin kwari mai karfin gaske ta dauko haďe da juice ta dawo kusa da Taheer ta zauna, yana kallonta ta ďure maganin a ciki,
a hankali ya mike yana tambayarta abun da zatayi dashi,
ko kallon inda yake batayi ba ta daga juice din zata kaishi bakinta,
Wani irin karfi yaji a jikinshi haďe kabe juice din a hannunta, baki na rawa yace
"Are u out of ur senses,
poison ne fa,
so kikeyi ki kashe kanki?