Sashe 66
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Daddy dan Allah ka aura min Nadeeyah,
wallahi ina santa sosai,
"Bakin cikin kiran Sunan Suwaiba da Daddy yayi da kuma na kalaman Musaddiq su suka hadu suka dugunzuma zuciyar Mummy ta sakar mishi wata irin kazamtaciyar ashariya,
kallo daya Daddy yayi mata tayi saurin dauke kai idanuwanta sunyi jaa saboda bacin rai,
Maida hankalinshi gurin danshi yayi Zuciyarshi fess saboda dama abin da yake ma danshi addu'a kenan,
"ka nemi soyayyarta? Daddy ya tambayeshi cikin sakin fuska,
"Eh Daddy, ita ma tana sona,
"Karya kakeyi wallahi,
inaji tana cewa bata sanka,
Yadda Mummy tayi maganar ya sanya Daddy dauke kai dan dariya ta kusa kufce mishi,
jiya bata barshi ya runtsa ba saboda labarin Faida yar gidan *Hon Danjuma Diriss*,
ta matukar cin burin bikin,
shi kuwa a gurinshi sam bayasan danshi yayi auren
*MATAUL HAYAT*,
irin su Nadeeya ya dade yana fata,
sai gashi Allah ya kawo mishi cikin sauki,
waya ya daga ya kira number Husnah yace suzo tare da Nadeeyah,
Mummy najin haka ta dauko wayarta ta tura text din gargadi zuwa ga Nadeeyah,
A lokacin da ta tura text din a lokacin Nadeeyah da Husnah sun kusa taka step din karshe.....
Cikin hikima Daddy yayi musu Nasiha ya nuna musu muhimmancin aure at early age,
sannan ya kalli Nadeeyah yace
"Nadeeyah kina da wanda kike so? Aure zan muku ke da Husnah...
A kunyace taja hijab dinta ta kasa hada ido dashi,
ya za'ayi ta iya furta bata san danshi na cikinshi,
Daddy,
Hilal,
Anty Reemah,
Musaddiq,
Anty Raly,
uwa uba Husnah da bata banbanta kanta da ita,
duk a cikin zuriar mutumin dake gabanta yana tambayarta ko tana san danshi,
ta ina zata iya butulce mishi,
a cikin jerin da ta lissafo babu wanda bai taka rawar gani cikin rayuwarta ba,
kuma Daddy ne ya samar dasu,
dago kai tayi suka hada ido da Mummy ta harareta hade girgiza mata kai,
dauke kanta tayi da sauri ta kalli Daddy dake sake jefo mata tambayar,
gyada kanta tayi a hankali alamar eh,
wanene shi?
Dan Musaddiq yazo min da zancenki,
in wani kike so shikenan sai sawun giwa ya taka na rakumi,
wani irin girma ya kara a idonta ta kasa bashi amsa,
"Ko Musaddiq din kike so?
Hannun Husnah ta rike sosai ta kasa dago ido ta kalleshi bare ta bashi amsa,
sau uku yana tambayarta tana yin shuru,
dariya yayi yace su tashi tafi,
Nadeeyah har tana tuntube da kofa tayi saurin fita,
Maida kallonshi gurin Musaddiq yayi yace
"To Malam ka shirya ma aure?
nawa ka tara daga albashinka,
nidai kasan ba ruwana nima da kaina na auri matata ya karashe cikin zolayar dukkansu biyun,
Ganin ya saki fuska yasa Mummy zama a kasan kafarshi,
"Dan Allah Daddy ka rufa min asiri,
bai kalleta ba yace
"Allah ne mai rufawa Zainabu,
me ya faru?
Hawayen bakin ciki ta fara yi tace "Yanzu kai farin cikinka ne danka guda daya tiloo ya kare anan,
tsakani da Allah duk yadda manyan abokanka ke miko ya'yansu mata gurinka domin shi, sai kuma suga ya kare a gurin yar Mai gadi,
yadda ta fadi abun ya soki Daddy Matuka,
nan da nan fuskarshi ta sauya yace
"akan Nadeeyah zan iya bata miki rai wallahi,
idan kika sake kiranta da yar mai gadi a matsayinta na jininki wallahi hukuncin da zan miki ba mai dadi bane,
cikin bacin rai ta mike tace
"ba jinina bace,
uwarta ce kadai jinina,
kai kasan asalinsu ne,
wa yasani ma ko ubanta barawo ne ya shigo cikinmu aka bashi aure,
wallahi bazan yarda in hada jini da marasa asali in samu bara gurbi cikin zuri'ata da zanyi tunkaho da ita ba,
"wallahi bazata sabu ba,
ai nima ina da hakki akan shi,
saboda haka wallahi indai ni na haifeshi bai isa ya auri Nadeeyah ba,
Sam Daddy bashi da saurin hannu amma tabbas a lokacin yayi niyyar dauke fuskar Mummy da mari,
a hankali yace
"ke kika haifeshi,
ke kuma nike iko dake,
wallahi tallahi in har kikayi abun da auren nan yaki yiwuwa sai kin bar min gidana,
kinga sai kowa ya nuna ikonshi,
Asali kuma Nadeeyah bata da wanda ya fini,
a yanzu na zama asalin Nadeeyah,
ni ne ubanta,
ni ne danginta da komai nata,
sai ki je maiduguri ki binciki Asalin Alh Garba kyari mai fata,
kallon Musaddiq yayi yace ka tashi kaje ka fara shiri daga bangarenka,
ni a bangarena bani da matsala...
jiki a sanyaye Musaddiq ya mike ya fita daga dakin,
bai taba tunanin zai samu wannan matsalar ba,
gashi kuma har ga Allah yana son Nadeeyah bazai iya rabuwa da ita ba,
ga kuma Mummy zata yi mishi karan tsaye cikin rayuwarshi,
tunane tunane ya dinga yi ya rasa mafita ya dauki wayarshi dan kiran Hilal,
a kashe wayar take dan haka ya kwanta yanata sakar da bata da karshe....
Mummy kuwa tana fita dakinta ta wuce cike da bakin ciki ta daga waya ta kira Radiya da Raudha da ta dawo gida weekend tace su kira Raliya suzo su sameta a gidan Goggo,
jin yadda muryarta ke rawa suka san ba lafiya ba,
ko wacce hankali tashe ta shirya tafiya gidan Goggo...
"Radiya ina zaki da sassafe?,
ko abun karyawa bakiyi ma su Umma ba kuma kinsan ba ita kadai bace,
shekeke ta kalleshi tace
"ni ma uwata ke nema na,
ko bani da ikon amsa kiran,
su tashi su daura da kansu tunda dai suna da hannu,
shikenan ni bani da sukuni saboda umma tazo,
a'a wallahi bazai yiwu ba,
Raees babban danta ne ya shigo yace
"Mama wai inji Umma tace ki kawo mata ruwan zafi zata sha magani,
wani dogon tsaki taja tace
"maza jeka gurin Gyatum kace ta kai mata,
hijab ta dauko tasa tana kunkunin da tun zuwansu gidan takeyinshi,
Mikewa mijinta yayi ya kira kanwarshi Haleesah yace "tazo tayi ma Su umma abinci,
sam baya jin dadin abin da Radiya kema yan uwanshi dashi kanshi,
hakuri kawai yakeyi saboda darajar mahaifinta,
yana shiga kitchen ya tarar da wata yar budurwa wacce shekarunta bai wuce sha tara ba. tana tsaye tana taya gyatum aiki,
Da sauri gyatum ta gaisheshi ya amsa yana kallon yarinyar,
itama tsugunawa tayi har kasa ta gaisheshi,
kamanninta da gyatum shi ya tabbatar mishi yarta ce,
saidai wannan din bak'inta mai kyau ne,
da dara daran ido farare tass ga kyawun diri,
har zai fita yace
"Gyatum wannan yarki ce?
Murmushi tayi tace "eh Alhj,
auta ta ce,
a gurin kanwata take a jos,
a can take karatu,
yanzu ma tazo hutu ne tazo tayani aiki,
gyada kanshi yayi yace
"Dan Allah ku taimakeni ku hada ma su Umma abun karyawa,
in san samu ne ma su samu tuwon laushi,
da sauri gyatum ta mike tace
"har sai ka roka,
Bar wanke wanken nan Fatima ki fara hada kayan karyawa,
Cike da jin dadi ya fita dan ko abincin baiyi dadi ba yasan zai fita kunyar mahaifiyarshi da kannenta...
Cikin kwarewa Fatima tayi miyar kukar da taji daddawa da dagargajajjen naman kaza, sannan ta tafasa kifi kadan ta sa citta da karumfani da tafarnuwa ta dakesu tsaf ta juye a cikin miyar,
nan gida ya kaure da kamshi, tana gamawa suka shirya komai cikin cooler gyatum ta dama musu kunun gyada ta fito da garin kosai ta kwaba tasa kwai da albasa ta soyashi gunin dadi,
manyan Coolers gyatum ta zuba abincin aka kai musu sannan ta zuba a kananan coolers ta ajiye wa mai gidan a dining,
saboda farin cikin ganin tuwon malmala biyu Umma ta cinye,
cike da jin dadi Haleesa ta kalleta tace
"yau Umma taci abinda take so, san samu kullum da safe da dare a dunga miki tuwo,
to hakan bazai yiwu ba,
hidimar Maman Raees tafi karfinta,
harara Indo kanwar Umma ta jefawa Haleesa tace
"yau da tayi kasheta aikin yayi,
Dariya Haleesa tayi tace
"waya fada miki ita tayi,
ita bata gidan ma,
mai aikin gidan ce tayi,
a daidai lokacin fatima ta shigo kwashe kayan abincin,
albarka suka shiga sa mata har ta gama ta fita,
umma dai da ido ta bita,
a kullum tana ma danta adduar samun mace ta gari ba mai kyale kyale irin Radiya ba,
yanzu din ma bazata fasa ba,
ganin da tayi wa Fatima na farko taji ta shiga ranta,
saidai bazata tilasta shi ya nemeta ba,
za dai ta cigaba da addua,
dan tabbas danta bashi da mace a gidanshi......
*Wai ina Hajiya Goggo Ma'u ne*
Bangaren Goggo kuwa tunda Anni ta tare kullum cikin kunan zuci take,
tayi asirin,
tayi tsafin duk a banza saboda yin auren Baffa ma kadai karyewar alkadari ne,
ga yawan abinci sadaka da Anni keyi kusan kullum domin nema musu tsira ranar Gobe kiyama,
Tunda Goggo taga asirin nata yaki aiki saidai suyi ta cin kudinta sai ta hakura ta fara kunno wutar tashin hankali da masifa a gidan,
idan Allah yasa ranar a dakin Anni Baffa zai kwana tofa babu bacci,
dan ta dinga dukan kofar da muciya kenan,
abun ba karamin damun Baffa yakeyi ba,
Anni ke hanashi magana ta nusar dashi yanzu tsufa yazo,
ba lokacin sa'insa bane,
lokacin da zamu koma ga Allah ne,
haka zasu mike suyi ta Sallah har ta gaji ta koma daki tana zage zage kamar wata yarinya,
Yau ma kamar Kullum Anni na tsakar gida ita da mai aikinta suna girkin sadaka ,
Shinkafa ce da wake sai lettuce da su tumatur,
suna gamawa aka fara zubashi a farantai ana fita dasu waje almajirai na rige rigen karba,
makota masu karamin karfi suma suka shigo da robobinsu aka zuba musu,
sunyi nisa sosai gurin rabo Goggo ta fito da bokitin fenti karami, fitsari ne a ciki ya kai rabi,
nan ta doshi katuwar tukunyar ta antaya fitsarin a ciki,
Da kyar Anni ta iya danne bacin ranta dan ta harzuka matuka,
rufe tukunyar tayi tace
"Harira, ki kira almajirai su kwashe abincin nan su kai ma dabbobi yau ranar tasu ce,
tana kaiwa nan tayi hanyar dakinta,
gabanta Goggo tasha ta dinga dura mata zagi,
ita dai Anni dariya kawai takeyi tana fadin nagode,
wallahi ina santa sosai,
"Bakin cikin kiran Sunan Suwaiba da Daddy yayi da kuma na kalaman Musaddiq su suka hadu suka dugunzuma zuciyar Mummy ta sakar mishi wata irin kazamtaciyar ashariya,
kallo daya Daddy yayi mata tayi saurin dauke kai idanuwanta sunyi jaa saboda bacin rai,
Maida hankalinshi gurin danshi yayi Zuciyarshi fess saboda dama abin da yake ma danshi addu'a kenan,
"ka nemi soyayyarta? Daddy ya tambayeshi cikin sakin fuska,
"Eh Daddy, ita ma tana sona,
"Karya kakeyi wallahi,
inaji tana cewa bata sanka,
Yadda Mummy tayi maganar ya sanya Daddy dauke kai dan dariya ta kusa kufce mishi,
jiya bata barshi ya runtsa ba saboda labarin Faida yar gidan *Hon Danjuma Diriss*,
ta matukar cin burin bikin,
shi kuwa a gurinshi sam bayasan danshi yayi auren
*MATAUL HAYAT*,
irin su Nadeeya ya dade yana fata,
sai gashi Allah ya kawo mishi cikin sauki,
waya ya daga ya kira number Husnah yace suzo tare da Nadeeyah,
Mummy najin haka ta dauko wayarta ta tura text din gargadi zuwa ga Nadeeyah,
A lokacin da ta tura text din a lokacin Nadeeyah da Husnah sun kusa taka step din karshe.....
Cikin hikima Daddy yayi musu Nasiha ya nuna musu muhimmancin aure at early age,
sannan ya kalli Nadeeyah yace
"Nadeeyah kina da wanda kike so? Aure zan muku ke da Husnah...
A kunyace taja hijab dinta ta kasa hada ido dashi,
ya za'ayi ta iya furta bata san danshi na cikinshi,
Daddy,
Hilal,
Anty Reemah,
Musaddiq,
Anty Raly,
uwa uba Husnah da bata banbanta kanta da ita,
duk a cikin zuriar mutumin dake gabanta yana tambayarta ko tana san danshi,
ta ina zata iya butulce mishi,
a cikin jerin da ta lissafo babu wanda bai taka rawar gani cikin rayuwarta ba,
kuma Daddy ne ya samar dasu,
dago kai tayi suka hada ido da Mummy ta harareta hade girgiza mata kai,
dauke kanta tayi da sauri ta kalli Daddy dake sake jefo mata tambayar,
gyada kanta tayi a hankali alamar eh,
wanene shi?
Dan Musaddiq yazo min da zancenki,
in wani kike so shikenan sai sawun giwa ya taka na rakumi,
wani irin girma ya kara a idonta ta kasa bashi amsa,
"Ko Musaddiq din kike so?
Hannun Husnah ta rike sosai ta kasa dago ido ta kalleshi bare ta bashi amsa,
sau uku yana tambayarta tana yin shuru,
dariya yayi yace su tashi tafi,
Nadeeyah har tana tuntube da kofa tayi saurin fita,
Maida kallonshi gurin Musaddiq yayi yace
"To Malam ka shirya ma aure?
nawa ka tara daga albashinka,
nidai kasan ba ruwana nima da kaina na auri matata ya karashe cikin zolayar dukkansu biyun,
Ganin ya saki fuska yasa Mummy zama a kasan kafarshi,
"Dan Allah Daddy ka rufa min asiri,
bai kalleta ba yace
"Allah ne mai rufawa Zainabu,
me ya faru?
Hawayen bakin ciki ta fara yi tace "Yanzu kai farin cikinka ne danka guda daya tiloo ya kare anan,
tsakani da Allah duk yadda manyan abokanka ke miko ya'yansu mata gurinka domin shi, sai kuma suga ya kare a gurin yar Mai gadi,
yadda ta fadi abun ya soki Daddy Matuka,
nan da nan fuskarshi ta sauya yace
"akan Nadeeyah zan iya bata miki rai wallahi,
idan kika sake kiranta da yar mai gadi a matsayinta na jininki wallahi hukuncin da zan miki ba mai dadi bane,
cikin bacin rai ta mike tace
"ba jinina bace,
uwarta ce kadai jinina,
kai kasan asalinsu ne,
wa yasani ma ko ubanta barawo ne ya shigo cikinmu aka bashi aure,
wallahi bazan yarda in hada jini da marasa asali in samu bara gurbi cikin zuri'ata da zanyi tunkaho da ita ba,
"wallahi bazata sabu ba,
ai nima ina da hakki akan shi,
saboda haka wallahi indai ni na haifeshi bai isa ya auri Nadeeyah ba,
Sam Daddy bashi da saurin hannu amma tabbas a lokacin yayi niyyar dauke fuskar Mummy da mari,
a hankali yace
"ke kika haifeshi,
ke kuma nike iko dake,
wallahi tallahi in har kikayi abun da auren nan yaki yiwuwa sai kin bar min gidana,
kinga sai kowa ya nuna ikonshi,
Asali kuma Nadeeyah bata da wanda ya fini,
a yanzu na zama asalin Nadeeyah,
ni ne ubanta,
ni ne danginta da komai nata,
sai ki je maiduguri ki binciki Asalin Alh Garba kyari mai fata,
kallon Musaddiq yayi yace ka tashi kaje ka fara shiri daga bangarenka,
ni a bangarena bani da matsala...
jiki a sanyaye Musaddiq ya mike ya fita daga dakin,
bai taba tunanin zai samu wannan matsalar ba,
gashi kuma har ga Allah yana son Nadeeyah bazai iya rabuwa da ita ba,
ga kuma Mummy zata yi mishi karan tsaye cikin rayuwarshi,
tunane tunane ya dinga yi ya rasa mafita ya dauki wayarshi dan kiran Hilal,
a kashe wayar take dan haka ya kwanta yanata sakar da bata da karshe....
Mummy kuwa tana fita dakinta ta wuce cike da bakin ciki ta daga waya ta kira Radiya da Raudha da ta dawo gida weekend tace su kira Raliya suzo su sameta a gidan Goggo,
jin yadda muryarta ke rawa suka san ba lafiya ba,
ko wacce hankali tashe ta shirya tafiya gidan Goggo...
"Radiya ina zaki da sassafe?,
ko abun karyawa bakiyi ma su Umma ba kuma kinsan ba ita kadai bace,
shekeke ta kalleshi tace
"ni ma uwata ke nema na,
ko bani da ikon amsa kiran,
su tashi su daura da kansu tunda dai suna da hannu,
shikenan ni bani da sukuni saboda umma tazo,
a'a wallahi bazai yiwu ba,
Raees babban danta ne ya shigo yace
"Mama wai inji Umma tace ki kawo mata ruwan zafi zata sha magani,
wani dogon tsaki taja tace
"maza jeka gurin Gyatum kace ta kai mata,
hijab ta dauko tasa tana kunkunin da tun zuwansu gidan takeyinshi,
Mikewa mijinta yayi ya kira kanwarshi Haleesah yace "tazo tayi ma Su umma abinci,
sam baya jin dadin abin da Radiya kema yan uwanshi dashi kanshi,
hakuri kawai yakeyi saboda darajar mahaifinta,
yana shiga kitchen ya tarar da wata yar budurwa wacce shekarunta bai wuce sha tara ba. tana tsaye tana taya gyatum aiki,
Da sauri gyatum ta gaisheshi ya amsa yana kallon yarinyar,
itama tsugunawa tayi har kasa ta gaisheshi,
kamanninta da gyatum shi ya tabbatar mishi yarta ce,
saidai wannan din bak'inta mai kyau ne,
da dara daran ido farare tass ga kyawun diri,
har zai fita yace
"Gyatum wannan yarki ce?
Murmushi tayi tace "eh Alhj,
auta ta ce,
a gurin kanwata take a jos,
a can take karatu,
yanzu ma tazo hutu ne tazo tayani aiki,
gyada kanshi yayi yace
"Dan Allah ku taimakeni ku hada ma su Umma abun karyawa,
in san samu ne ma su samu tuwon laushi,
da sauri gyatum ta mike tace
"har sai ka roka,
Bar wanke wanken nan Fatima ki fara hada kayan karyawa,
Cike da jin dadi ya fita dan ko abincin baiyi dadi ba yasan zai fita kunyar mahaifiyarshi da kannenta...
Cikin kwarewa Fatima tayi miyar kukar da taji daddawa da dagargajajjen naman kaza, sannan ta tafasa kifi kadan ta sa citta da karumfani da tafarnuwa ta dakesu tsaf ta juye a cikin miyar,
nan gida ya kaure da kamshi, tana gamawa suka shirya komai cikin cooler gyatum ta dama musu kunun gyada ta fito da garin kosai ta kwaba tasa kwai da albasa ta soyashi gunin dadi,
manyan Coolers gyatum ta zuba abincin aka kai musu sannan ta zuba a kananan coolers ta ajiye wa mai gidan a dining,
saboda farin cikin ganin tuwon malmala biyu Umma ta cinye,
cike da jin dadi Haleesa ta kalleta tace
"yau Umma taci abinda take so, san samu kullum da safe da dare a dunga miki tuwo,
to hakan bazai yiwu ba,
hidimar Maman Raees tafi karfinta,
harara Indo kanwar Umma ta jefawa Haleesa tace
"yau da tayi kasheta aikin yayi,
Dariya Haleesa tayi tace
"waya fada miki ita tayi,
ita bata gidan ma,
mai aikin gidan ce tayi,
a daidai lokacin fatima ta shigo kwashe kayan abincin,
albarka suka shiga sa mata har ta gama ta fita,
umma dai da ido ta bita,
a kullum tana ma danta adduar samun mace ta gari ba mai kyale kyale irin Radiya ba,
yanzu din ma bazata fasa ba,
ganin da tayi wa Fatima na farko taji ta shiga ranta,
saidai bazata tilasta shi ya nemeta ba,
za dai ta cigaba da addua,
dan tabbas danta bashi da mace a gidanshi......
*Wai ina Hajiya Goggo Ma'u ne*
Bangaren Goggo kuwa tunda Anni ta tare kullum cikin kunan zuci take,
tayi asirin,
tayi tsafin duk a banza saboda yin auren Baffa ma kadai karyewar alkadari ne,
ga yawan abinci sadaka da Anni keyi kusan kullum domin nema musu tsira ranar Gobe kiyama,
Tunda Goggo taga asirin nata yaki aiki saidai suyi ta cin kudinta sai ta hakura ta fara kunno wutar tashin hankali da masifa a gidan,
idan Allah yasa ranar a dakin Anni Baffa zai kwana tofa babu bacci,
dan ta dinga dukan kofar da muciya kenan,
abun ba karamin damun Baffa yakeyi ba,
Anni ke hanashi magana ta nusar dashi yanzu tsufa yazo,
ba lokacin sa'insa bane,
lokacin da zamu koma ga Allah ne,
haka zasu mike suyi ta Sallah har ta gaji ta koma daki tana zage zage kamar wata yarinya,
Yau ma kamar Kullum Anni na tsakar gida ita da mai aikinta suna girkin sadaka ,
Shinkafa ce da wake sai lettuce da su tumatur,
suna gamawa aka fara zubashi a farantai ana fita dasu waje almajirai na rige rigen karba,
makota masu karamin karfi suma suka shigo da robobinsu aka zuba musu,
sunyi nisa sosai gurin rabo Goggo ta fito da bokitin fenti karami, fitsari ne a ciki ya kai rabi,
nan ta doshi katuwar tukunyar ta antaya fitsarin a ciki,
Da kyar Anni ta iya danne bacin ranta dan ta harzuka matuka,
rufe tukunyar tayi tace
"Harira, ki kira almajirai su kwashe abincin nan su kai ma dabbobi yau ranar tasu ce,
tana kaiwa nan tayi hanyar dakinta,
gabanta Goggo tasha ta dinga dura mata zagi,
ita dai Anni dariya kawai takeyi tana fadin nagode,