Sashe 4
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
kullum cikin bakin cikin halin danta takeyi wanda Sam bai biyo halinta dana ubanshi ba,
da ya tashi sai ya dauko halin mamanta har ya damata ya shanye saidai shi Sam bashi da neman suna kuma komai zaiyi sai yanada hujja...
Ruwa musaddiq ya bata tasha yace "kiyi hakuri anty kin so ki bata ranki ne,
kinsan halin Hilal, babu mai iya canza shi sai Allah,
kuma kin San duk abin da zaiyi akan gaskiya yakeyi he is open,
baya barin abu a ranshi,
dole ya koyi barin abu a ranshi musaddiq, Reema ta fadi tana mai ajiye kofin da ta sha ruwa,!
meye amfanin duk abun da akayi ma mutum yace sai ya rama,
wani lokacin ma ba dashi akeyi ba sai ya sako kanshi saboda shi baya gudun bakin duni--
kwanciyar da taji anyi a bayanta ne ya hanata karasawa,
kamshin turaren da taji ne ya sanar da ita ko waye,
Kara tamke fuskarta tayi hade da Jan tsaki,
cikin muryarshi ta yan gayun yaran hutu yace
"ki daina gudun bakin duniya Momma na,
in dai duniya muke son mu burge to lallai munada aiki babba a gaban mu,
"chapter closed",
am so sorry for hurting you mum,
wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarta hade da kara kaunar dan nata,
duk iya inda yakai da zuciyarshi ya tsani bacin ranta,
baya daukar mintina sai yasan hanyar da yabi ya wanke zuciyarta,
dariyar farin ciki musaddiq yayi "yace komai ya wuce ''aunty momma!! ,
murmushi tayi hade jan kunnuwansu,
zama sukayi suka sata a tsakiya suna mata hira kamar babu wani abu na bacin rai daya gifta a tsakanin su,,
karar da wayarta tayi ne ya katse musu hirar,
zaro ido tayi ta mike tana fadin ya ilahi hade da daukar wayar, sorry Rally shaff na mance da ku,
daga dayan bangaren Rally tace ai na Lura da hakan, gashi har mun gama komai,
cikin farin ciki Anty reema tace kinyi komai simple dai ko, kinsan komai namu very simple muke yinshi,
saima kin gani anty, abin sai ya burge ki ta fadi tana gyara balloons din da sukayi kasa kasa, ok thank u babe,
gamu nan Zuwa,
juyowa tayi tace kuje ku shirya ku raka ni wani guri,
Hilal da ya riga ya harbo su yace ni a shirye nake mum,
bata kalleshi ba ta kamo hannun Musaddiq sukayi daki,
a cikin sababbin kayan da ta siyo mishi ta zaba mishi tace ya saka ta fita ta bashi guri,
saida ya dau minti goma yana shiryawa,
jar riga ya saka mai matukar kyau da deep blue wando, ya taje kwantaccen gashin shi, kyawun bakar fatarshi mai sanyi ya kara bayyana, hatta madubin da ya kalla yasan babu karya shi din mai kyau ne matuka,,
fitowa yayi cikin takunshi na nima na fara girma,
kallon kauna anty reema ta bishi dashi tana fadin wowwww kanina,
babu kamarka a wannan zamanin,
gaskiya kayan nan sun karbe ka,
sajenshi ta shafa tace "Allah ya nuna min aurenka dole in zauna da matar saboda kar ta cutar min da kai,
Hilal ya ajiye cup din coffee yana dariya yace saboda kinsan uncle din nawa is nt brave ko,
zanci ub-- toshe mata baki yayi da sauri hade da rungumeta yana dariya harda kyakyatawa,
tureshi tayi tace "wallahi yaron nan ya rainani sosai,
zanyi maganin ka,
dariya suka saki Hilal ya dauko keyn mota Kan centre table yace oya mu wuce,
Anty reema ta kalleshi Sama da kasa tace da wannan wandon zaka fita,,,
pls mum karki fara muje kawai ya fadi yana wani narkewa,
hmmm kawai tace ta kama hannun musaddiq suka fita Zuwa gurin Mota.....
Mrs Tijjani Shattima.....!
[04/12 09:44] Meela Adeel: 7⃣
°ZUMUNCINMU A YAU °
By Aysha Ya'u Kurah
Mamma duba min kiga kwabin yayi haka,
mamma dake kashingide ta dan mike ta kalli kwanon madarar da Nadiya ta kwaba,
hannu tasa ta dan taba ta gutsuri kadan tasa a bakinta,
"mmmm gaskiya yayi dadi kuma yayi danko ta fadi tana lumshe ido alamar santi duk dan ta kara ma diyarta kwarin gwiwa,
murmushin Jindadi Nadiya tayi ta ajiye a kan tabarma ta shiga kitchen ta dauko leda da kwalbar da zata murza madarar,
Cikin nutsuwa take murzawa tana yanka su kanana tana sawa cikin wata tsaftatacciyar robar sweet da ta amso a shagon Tasi makocinsu,
hira sukeyi cikin jindadi mamma na taya ta kirga wadanda ta yanka, saida suka gama tsaf, Nadiya ta kalli mamma tace
"Mamma in rokeki wani abu,
mamma ta karashe rufe robar tuwon madara tace fadi kanki tsaye yar albarka,
Dan Allah Mamma kiyi hakuri ki daina yin "wankau" ban taba Jin zafin masu yi min gorin kina wankau ba sai yau da Nafi'un Baba Atika yayi min a shagon Tasi,
wai masu wanke daudar wasu bazasu taba yin arziki ba,
Dan Allah mamma ki daina, in shaa Allahu wannan karamar sana'ar da muka fara zata dinga rufa mana asiri da dan abun da baba da yaya hafiz zasu samo,
tunda ta fara maganar idon mamma ya ciko da kwalla,
kauda kanta tayi ta dan share da gefen zani tace
"Nadiya wanki baya kawo talauci duk canfin hausawa ne,
saidai zan daina saboda in karfafa gwiwar ki tunda hakan kika bukata,
sannan zamu hada da ruwan kankara saboda yayi karanci a unguwar nan,
wani farin ciki ne ya lullube Nadiya tace "alhamdulillah" nagode mamma,
bari inje in kaiwa Tasi dan yace ina gamawa in kawo mishi,
gyada kai mamma tayi tace "a kai da bismilla Allah yasa mishi albarka, Ameen Nadiya tace tana kiciniyar sa hijab dinta,
karo tayi da samari biyu suna kutso kansu gidan hade da sallama,
da sauri taja da baya ta kame jikin bango saboda irin kallon da Hilal yake yi mata,
tsaki yaja hade da kakkabe kayan jikinshi ya wuce,
kanta a kasa ta gaida musaddiq ta raba ta gefenshi ta wuce,
binta yayi da kallo zuciyarshi a karye,
Allah kadai yasan irin tausaya musun da yakeyi, yarinya karama tasan wahalhalun rayuwa,
muryar Anty Reemah ya jiyo tana tambayarta inda zata,
sunne kai tayi tace "zanje shago ne in kai tuwon Madara,
Hinad ta kalli hannunta tace "wow dan sammin, budewa ta fara kokarin yi Anty Reemah tace "kyaleta kinji na nawa ne duka,
cike da Jin kunya tace
"na dari takwas da hamsin ne, sai na dari ribar Mai shago,
Anty Reemah tayi murmushi tace duka dari tara da hamsin kenan ko,
girgiza kai Nadiya tayi tace ki bani dari takwas kawai, dubu daya ta zaro a Jakarta tace to gashi ki dauki dari takwas na tuwon Madara canjin ki siyo takalmi ki cire wannan hadi da Bautan kinji yar kasuwa,
rufe fuskarta tayi tana dariya tace nagode sosai Allah ya saka da alkhairi,
Ameen anty Reemah tace ta mikewa Hinad tuwon madarar suka karasa cikin gidan tare da Musaddiq,,
Hilal suka tarar a tsaye mamma na mishi hira yana fadin umm in na a'a ne yace um um,
mamma na ganin su ta karaso tana musu oyoyo,
a dadduma suka zauna ta kawo musu ruwa,
duk ta rasa inda zata sa ranta saboda dadin yau nata yazo inda take,
me za'a dafa muku tayi ta fada kamar zata fado kansu saboda murna,
Anty Reemah tace wallhy a koshe muke mamma daga gurin partyn Musaddiq muke nace bari mu biyo mu gaisheki mu kuma yi miki sallama dan inaga jibi zan koma,
Ayya mamma ta fadi tana Mai zaunawa kusa da ita, har zaki koma Antyn Yara,
Reemah tace eh zamu koma tare da musaddiq na sama mishi makaranta a can,,
Allah sarki musaddiq zaka bamu kewa ashe, to Allah yasa ka je ka fara a sa'a,
Ameen musaddiq yace yana Sosa keya,
da sauri ta dawo gidan da sabon silifas a kafarta da ledar madara da suga,
ajiyewa tayi a kofar kitchen tace sannunku,
mamma ta kalleta kallon tuhuma tace a Ina kika samo sabon takalmi? ,
canji ta ciro a cikin aljihunta ta mika ma mamma tace Anty ce ta siye duka ta kuma bani kudin takalmi,
shine dan sakarci baki shigo kin fada min ba mamma ta fadi rai a bace,
Anty Reemah tace "kiyi hakuri mamma ni nace tayi sauri ta siyo takalmi,
mamma tayi murmushi tace to mun gode fa Allah ya saka da alkhairi, Ameen anty Reemah tace tana kallon Nadiya da ke rabe tana wasa da hijabinta,
ni ko mamma wace makaranta Nadiya ke Zuwa?
Mamma ta yi murmushi tace ta zana jarabawar aji shida zata cigaba da makarantar gaba in shaa Allah,
to ai mamma naga har an kusa gama third term wace makaranta kuke neman mata? ,
mamma ta kalli gefen da Nadiya take tace makarantar kwana ta Queen Amina dake kakuri,
to har yanzu bata samu bane? Reemah ta tambaya cike da damuwa,
muna ta kokarin har hada abin da zata tafi dashi ne mamma ta fadi cike da Jin kunya,
Anty Reemah tayi ajiyar zuciya tace mamma karatun diya mace nada matukar amfani,
Dan Allah Kar ayi wasa da ita first term din nan da za mu shiga,
ki bar batun queen Amina,
zan ma abban Hilal magana zai sa a bata admission a fgc malali in shaa Allah,
sannan ki turo min hafiz inason ganinshi gobe kafin muje gidan Baffa,
Kasa rufe baki mamma tayi saboda murna,
share hawayen farin ciki ta shiga yi tana kallon Nadiya dake ta dariya,
kai gaskiya nagode Antyn yara, Allah ya biyaki da aljanna, nagode sosai,
anty Reemah ta mike tana fadin haba mamma me akayi ai duk daya ne,
Dan Allah ki daina min godiya,
Godiya ta zama dole Reemah mamma ta fadi tana rike baki, kedai kawai Allah shine zai saka miki,
Ameen anty Reemah tace ta fito da dubu biyar a jaka ta bawa Nadiya tace wannan na auta ne in ta tashi kice mata gashi inji ni kinji,
Nadiya ta karba ta shiga godiya hade da bayyana kyawawan hakoranta,
har gurin Mota suka raka su suna ta godiya kamar bakin su zai tsinke, musaddiq mamma ta kalla tace "me kake so in kawo maka ka tafi dashi? , murmushi yayi yace koma meye mamma nagode,
mamma tace to an gama dan albarka..
da ya tashi sai ya dauko halin mamanta har ya damata ya shanye saidai shi Sam bashi da neman suna kuma komai zaiyi sai yanada hujja...
Ruwa musaddiq ya bata tasha yace "kiyi hakuri anty kin so ki bata ranki ne,
kinsan halin Hilal, babu mai iya canza shi sai Allah,
kuma kin San duk abin da zaiyi akan gaskiya yakeyi he is open,
baya barin abu a ranshi,
dole ya koyi barin abu a ranshi musaddiq, Reema ta fadi tana mai ajiye kofin da ta sha ruwa,!
meye amfanin duk abun da akayi ma mutum yace sai ya rama,
wani lokacin ma ba dashi akeyi ba sai ya sako kanshi saboda shi baya gudun bakin duni--
kwanciyar da taji anyi a bayanta ne ya hanata karasawa,
kamshin turaren da taji ne ya sanar da ita ko waye,
Kara tamke fuskarta tayi hade da Jan tsaki,
cikin muryarshi ta yan gayun yaran hutu yace
"ki daina gudun bakin duniya Momma na,
in dai duniya muke son mu burge to lallai munada aiki babba a gaban mu,
"chapter closed",
am so sorry for hurting you mum,
wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarta hade da kara kaunar dan nata,
duk iya inda yakai da zuciyarshi ya tsani bacin ranta,
baya daukar mintina sai yasan hanyar da yabi ya wanke zuciyarta,
dariyar farin ciki musaddiq yayi "yace komai ya wuce ''aunty momma!! ,
murmushi tayi hade jan kunnuwansu,
zama sukayi suka sata a tsakiya suna mata hira kamar babu wani abu na bacin rai daya gifta a tsakanin su,,
karar da wayarta tayi ne ya katse musu hirar,
zaro ido tayi ta mike tana fadin ya ilahi hade da daukar wayar, sorry Rally shaff na mance da ku,
daga dayan bangaren Rally tace ai na Lura da hakan, gashi har mun gama komai,
cikin farin ciki Anty reema tace kinyi komai simple dai ko, kinsan komai namu very simple muke yinshi,
saima kin gani anty, abin sai ya burge ki ta fadi tana gyara balloons din da sukayi kasa kasa, ok thank u babe,
gamu nan Zuwa,
juyowa tayi tace kuje ku shirya ku raka ni wani guri,
Hilal da ya riga ya harbo su yace ni a shirye nake mum,
bata kalleshi ba ta kamo hannun Musaddiq sukayi daki,
a cikin sababbin kayan da ta siyo mishi ta zaba mishi tace ya saka ta fita ta bashi guri,
saida ya dau minti goma yana shiryawa,
jar riga ya saka mai matukar kyau da deep blue wando, ya taje kwantaccen gashin shi, kyawun bakar fatarshi mai sanyi ya kara bayyana, hatta madubin da ya kalla yasan babu karya shi din mai kyau ne matuka,,
fitowa yayi cikin takunshi na nima na fara girma,
kallon kauna anty reema ta bishi dashi tana fadin wowwww kanina,
babu kamarka a wannan zamanin,
gaskiya kayan nan sun karbe ka,
sajenshi ta shafa tace "Allah ya nuna min aurenka dole in zauna da matar saboda kar ta cutar min da kai,
Hilal ya ajiye cup din coffee yana dariya yace saboda kinsan uncle din nawa is nt brave ko,
zanci ub-- toshe mata baki yayi da sauri hade da rungumeta yana dariya harda kyakyatawa,
tureshi tayi tace "wallahi yaron nan ya rainani sosai,
zanyi maganin ka,
dariya suka saki Hilal ya dauko keyn mota Kan centre table yace oya mu wuce,
Anty reema ta kalleshi Sama da kasa tace da wannan wandon zaka fita,,,
pls mum karki fara muje kawai ya fadi yana wani narkewa,
hmmm kawai tace ta kama hannun musaddiq suka fita Zuwa gurin Mota.....
Mrs Tijjani Shattima.....!
[04/12 09:44] Meela Adeel: 7⃣
°ZUMUNCINMU A YAU °
By Aysha Ya'u Kurah
Mamma duba min kiga kwabin yayi haka,
mamma dake kashingide ta dan mike ta kalli kwanon madarar da Nadiya ta kwaba,
hannu tasa ta dan taba ta gutsuri kadan tasa a bakinta,
"mmmm gaskiya yayi dadi kuma yayi danko ta fadi tana lumshe ido alamar santi duk dan ta kara ma diyarta kwarin gwiwa,
murmushin Jindadi Nadiya tayi ta ajiye a kan tabarma ta shiga kitchen ta dauko leda da kwalbar da zata murza madarar,
Cikin nutsuwa take murzawa tana yanka su kanana tana sawa cikin wata tsaftatacciyar robar sweet da ta amso a shagon Tasi makocinsu,
hira sukeyi cikin jindadi mamma na taya ta kirga wadanda ta yanka, saida suka gama tsaf, Nadiya ta kalli mamma tace
"Mamma in rokeki wani abu,
mamma ta karashe rufe robar tuwon madara tace fadi kanki tsaye yar albarka,
Dan Allah Mamma kiyi hakuri ki daina yin "wankau" ban taba Jin zafin masu yi min gorin kina wankau ba sai yau da Nafi'un Baba Atika yayi min a shagon Tasi,
wai masu wanke daudar wasu bazasu taba yin arziki ba,
Dan Allah mamma ki daina, in shaa Allahu wannan karamar sana'ar da muka fara zata dinga rufa mana asiri da dan abun da baba da yaya hafiz zasu samo,
tunda ta fara maganar idon mamma ya ciko da kwalla,
kauda kanta tayi ta dan share da gefen zani tace
"Nadiya wanki baya kawo talauci duk canfin hausawa ne,
saidai zan daina saboda in karfafa gwiwar ki tunda hakan kika bukata,
sannan zamu hada da ruwan kankara saboda yayi karanci a unguwar nan,
wani farin ciki ne ya lullube Nadiya tace "alhamdulillah" nagode mamma,
bari inje in kaiwa Tasi dan yace ina gamawa in kawo mishi,
gyada kai mamma tayi tace "a kai da bismilla Allah yasa mishi albarka, Ameen Nadiya tace tana kiciniyar sa hijab dinta,
karo tayi da samari biyu suna kutso kansu gidan hade da sallama,
da sauri taja da baya ta kame jikin bango saboda irin kallon da Hilal yake yi mata,
tsaki yaja hade da kakkabe kayan jikinshi ya wuce,
kanta a kasa ta gaida musaddiq ta raba ta gefenshi ta wuce,
binta yayi da kallo zuciyarshi a karye,
Allah kadai yasan irin tausaya musun da yakeyi, yarinya karama tasan wahalhalun rayuwa,
muryar Anty Reemah ya jiyo tana tambayarta inda zata,
sunne kai tayi tace "zanje shago ne in kai tuwon Madara,
Hinad ta kalli hannunta tace "wow dan sammin, budewa ta fara kokarin yi Anty Reemah tace "kyaleta kinji na nawa ne duka,
cike da Jin kunya tace
"na dari takwas da hamsin ne, sai na dari ribar Mai shago,
Anty Reemah tayi murmushi tace duka dari tara da hamsin kenan ko,
girgiza kai Nadiya tayi tace ki bani dari takwas kawai, dubu daya ta zaro a Jakarta tace to gashi ki dauki dari takwas na tuwon Madara canjin ki siyo takalmi ki cire wannan hadi da Bautan kinji yar kasuwa,
rufe fuskarta tayi tana dariya tace nagode sosai Allah ya saka da alkhairi,
Ameen anty Reemah tace ta mikewa Hinad tuwon madarar suka karasa cikin gidan tare da Musaddiq,,
Hilal suka tarar a tsaye mamma na mishi hira yana fadin umm in na a'a ne yace um um,
mamma na ganin su ta karaso tana musu oyoyo,
a dadduma suka zauna ta kawo musu ruwa,
duk ta rasa inda zata sa ranta saboda dadin yau nata yazo inda take,
me za'a dafa muku tayi ta fada kamar zata fado kansu saboda murna,
Anty Reemah tace wallhy a koshe muke mamma daga gurin partyn Musaddiq muke nace bari mu biyo mu gaisheki mu kuma yi miki sallama dan inaga jibi zan koma,
Ayya mamma ta fadi tana Mai zaunawa kusa da ita, har zaki koma Antyn Yara,
Reemah tace eh zamu koma tare da musaddiq na sama mishi makaranta a can,,
Allah sarki musaddiq zaka bamu kewa ashe, to Allah yasa ka je ka fara a sa'a,
Ameen musaddiq yace yana Sosa keya,
da sauri ta dawo gidan da sabon silifas a kafarta da ledar madara da suga,
ajiyewa tayi a kofar kitchen tace sannunku,
mamma ta kalleta kallon tuhuma tace a Ina kika samo sabon takalmi? ,
canji ta ciro a cikin aljihunta ta mika ma mamma tace Anty ce ta siye duka ta kuma bani kudin takalmi,
shine dan sakarci baki shigo kin fada min ba mamma ta fadi rai a bace,
Anty Reemah tace "kiyi hakuri mamma ni nace tayi sauri ta siyo takalmi,
mamma tayi murmushi tace to mun gode fa Allah ya saka da alkhairi, Ameen anty Reemah tace tana kallon Nadiya da ke rabe tana wasa da hijabinta,
ni ko mamma wace makaranta Nadiya ke Zuwa?
Mamma ta yi murmushi tace ta zana jarabawar aji shida zata cigaba da makarantar gaba in shaa Allah,
to ai mamma naga har an kusa gama third term wace makaranta kuke neman mata? ,
mamma ta kalli gefen da Nadiya take tace makarantar kwana ta Queen Amina dake kakuri,
to har yanzu bata samu bane? Reemah ta tambaya cike da damuwa,
muna ta kokarin har hada abin da zata tafi dashi ne mamma ta fadi cike da Jin kunya,
Anty Reemah tayi ajiyar zuciya tace mamma karatun diya mace nada matukar amfani,
Dan Allah Kar ayi wasa da ita first term din nan da za mu shiga,
ki bar batun queen Amina,
zan ma abban Hilal magana zai sa a bata admission a fgc malali in shaa Allah,
sannan ki turo min hafiz inason ganinshi gobe kafin muje gidan Baffa,
Kasa rufe baki mamma tayi saboda murna,
share hawayen farin ciki ta shiga yi tana kallon Nadiya dake ta dariya,
kai gaskiya nagode Antyn yara, Allah ya biyaki da aljanna, nagode sosai,
anty Reemah ta mike tana fadin haba mamma me akayi ai duk daya ne,
Dan Allah ki daina min godiya,
Godiya ta zama dole Reemah mamma ta fadi tana rike baki, kedai kawai Allah shine zai saka miki,
Ameen anty Reemah tace ta fito da dubu biyar a jaka ta bawa Nadiya tace wannan na auta ne in ta tashi kice mata gashi inji ni kinji,
Nadiya ta karba ta shiga godiya hade da bayyana kyawawan hakoranta,
har gurin Mota suka raka su suna ta godiya kamar bakin su zai tsinke, musaddiq mamma ta kalla tace "me kake so in kawo maka ka tafi dashi? , murmushi yayi yace koma meye mamma nagode,
mamma tace to an gama dan albarka..