Sashe 112
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
jin har minti uku baiyi magana ba yasata juyawa dan ganin halin da yake ciki,
wannan karan a juye yake idanuwan nan a rufe wani sabon bacci ne ma yayi gaba dashi wanda daga gani kasan yana cikin mayen magani ne,
da sauri ta murďa kofar ta fita saboda kwalla da taji ta taru a idonta,
wannan wacce iriyar zazzafar jarabawa ce,
ya Allah ka kawo mana mafita baki dayanmu dan alfarmar annabi Muhammad s.a.w.....
Gidan Alhaji Mukhtar ya zama tamkar gidan zaman makoki, kamar babu wata hidima da za'ayi a cikinsa nan da kwana biyu,
Anty Reemah dasu Raudha sune kadai ke hidimarsu bisa ga umurnin Daddy,
sai kuma Mummy da a yanzu takan samu shigowa duba jikin Musaddiq,
duk da bata samun koda gaisawa da Daddy hakan yayi mata daďi tunda ya yafe mata kuma ya yafewa 'yayanshi yana sakar musu yanzu,
a yanzu bata da burin da ya wuce taga rayuwar Musaddiq ta inganta,
ta rasa kalmar da zata roki Nadeeyah dashi ta yarda da auren ďanta wanda ta zama sila a rabuwarsu,
gashi abun da tayi yayi sanadiyyar sanya shi cikin tsakiyar rayuwa da mutuwa...
A yau ma kamar kullum bayan ta gama gyara ďakin Goggo inda take kwana ta shirya tsaff dan tafiya dubo Musaddiq sannan ta zauna ayi kamun Nadeeyah da ita,
tana rufe kofa ta jiyo muryar Badariyya wacce a yanzu Yareemah Suhail ke fitowa da ita ya kawo ta har gida tun dawowar Nadeeyah,,
kwancen kayan da su Husna suka bata shi ta sanya tayi kyau abunta, sannan su suwidi suma sunyi kyansu dan a yanzu suna samun sake da kuma abinci wanda duk tazo sai yan uwa sun sai mata,
"A'a Badariyyah kece a gidan, to juya muje ki duba jikin Musaddiq daga nan ki jira ayi kamun Nadeeyah dake,
cike da damuwa ta juya suka fita suna tattauna damuwar da Musaddiq din ke ciki a sanadinsu, Badariyya a cikin ranta ta dau alwashin kebewa da Nadeeyah ta faďa mata abubuwan da tayi wanda ya rabasu, babu mamaki taji tausayinshi in tasan baya cikin hayyacinsa sanda yayi sakin....
Bayan ta gama sauraron kalaman Badariyya wanda takeyinsu cike da nadama tace
"Badariyya abun da kukayi bai isa ya raba mu ba,
tunda kika ga mun rabu to tabbas Allah ya rubuta rabuwar tamu ne a lokacin,
sannan a yanzu in na ki uncle Taheer shi munsan halin da zai shiga,
dan Allah ku fahimceni,
ni kadai nasan halin da nake ciki, ku tayani addu'a nasan komai zai daidaita da yardar Allah...
Share hawaye Badariyya tayi tace "Zamu tayaki, Allah yasa hakan shine mafi alkhairi....
Karfe huďu da yan mintuna Nadeeyah ta shirya cikin wani lace mai kyau da tsada cikin kayan da Taheer ya dinka mata, Anty Raly ke tsaye a kanta tana gyara mata kwalliyarta haďe da yi mata ďauri,
wata farar alkyabba mai adon yellow ta dauko ta daura mata a kanta wanda hakan ya sake fitar da kayatuwar da amaryar tayi, jan lallen da akayi mata ya rinu sosai ya koma dark maroon hakan ba karamin sake fitar da suffar yatsunta yayi ba,
zaunar da ita Anty Raly tayi tana jiyo sautin maganganu yan biki daga waje,,
Cike da masifa take shirya su Nour tana daka musu tsawar su tsaya ko ta zanesu,
a hankali Nadeeyah ta janyo hannun Abee tace
"Kawo in shiryashi Husna,
"Barshi.. kadai ta faďi haďe da janyo hannunshi ta sa mishi irin kayan dake jikin Hafeez,
oya a je ayi wasa, banda barna da bata jiki,
mikewa tayi da niyyar shiga bayi Nadeeyah ta riko hannunta,
"Husnah nasan ni mai laif---
Lokaci na kurewa Nadeeyah,
baki da laifin komai kaddararmu ce tazo a haka,
na kasa dai jin saukin zuciyata ne shiyasa har yanzun kika ganni haka,
with time in shaa Allah komai zai daidaita,
Husnah ta katseta fuskar nan murtuke tamkar wacce akayi ma mutuwa..
ganin Nadeeyah na kokarin sake magana yasata zame hannunta daga cikin nata ta faďa bayi,
wani irin kuka ne yazo musu a tare mai cin rai,
saida sukaci suka koshi sannan Husnah tayi wanka ta fito ta shirya da sauri sauri tayi waje....
Sai biyar da kusan rabi dangin Taheer suka zo sa lallen amarya, sai da suka biya kawayen amarya wacce Amal ce kaďai sai Raliya da ta shiga cikin zancen,
turaruka masu kamshin gaske suka karar a jikinta sauran yan uwansu na Agadez wadanda suka ji dadin ganin Nadeeyah da Hafeez suna rangaďa guďa,
kwaryar nono wacce suka kawo gidan kanta ta kai hamsin,
banda sauran gararrakin arziki da suka kawo,
sunci sun sha a gidan sosai dan komai nasu daban aka ware musu,
sai bayan Isha'i motocin da suka kawosu suka maida su....
A daddafe Musaddiq ya amsa gaisuwar Taheer wanda ke tsaye rike da danshi cikin tsadajjiyar shadda iri ďaya,
lallaba Junior ya shiga yi bayan ya fuskanci irin fushin da yakeyi dashi,
sannan kuma dan ya daukewa kanshi damuwar da ke cinshi tun kwana uku baya,
wani mugun tari yaji Musaddiq nayi wanda ya sanyashi sakin hannun Junior ya isa gareshi haďe da dauko ruwa yana faďin sannu, ga ruwa kasha,
runtse ido Musaddiq yayi haďe da kauda fuskarshi gefe,
ya riga ya gama yanke duk wani hukuncin da ya dace,
yasani a yanzu ganin gobe a gareshi nada matukar wahala, a yanzu ya sadaukar da komai yasan Nadeeyah da ďanshi bazasu taba yin kunci ba tunda suna tare da nagartaccen mutum irin Taheer wanda a haďuwarka dashi ta farko zata tabbatar da hakan komin kinka dashi,
dafe kanshi yayi da hannayenshi biyu saboda hawayen dake zubo mishi babu kakkautawa,
Mikewa Taheer yayi dukkan lakar jikinshi a sake ya kama hannun Junior suka sauka kasa,
a hanyar da zai sadasu da kofar fita ya haďu da Hilal da ya dawo daga rakiyar abokansu,
shima duk ya fukace ya fita hayyacinshi kamar shine mai ciwon,
"A'a yallabai har kun fito,
ya faďi yana mika mishi hannu,
"Eh dare nayi,
Allah ya bashi lafiya,
"Ameen Hilal ya amsa haďe cewa sai da safe mun gode,
"Allah ya tashemu lafiya Taheer yace yana mai saka kafarshi a waje,
A gurin motarshi suka tsaya ya kira number Nadeeyah wacce ke kan dadduma tana zubda kwallar da ta zame mata jiki,
a hankali ta ďauka cikin nuna bata cikin damuwa tace
"Uncle kun wuce ne?
"No muna waje,
muna san ganinki ne ya faďi wani ďaci na tokare makogaronshi,
Kara sassauta murya tayi tace "Gobe ne fa, daga gobe bazan sake barin gefenka ba, har sai ka gaji da ganina,
kayi hakuri plss,
Lumshe idanuwanshi yayi haďe da kallon sama a zuciyarshi yana rokon ubangiji sassauci akan wannan jarabawar,
*Tayi min tsauri da yawa* ya faďi ba tare da yasan ta fito ba, yana mai kwantar da kanshi kan murfin motar,
"Gani nan zuwa Uncle, in dai rashin ganina yayi maka tsauri, bakayi deserving shan wahala akaina ba,
bata jira amsarshi ba ta kashe wayar ta mike haďe da ninke dardumar tayi waje....
Duk abin nan da sukeyi a kunnen Raudha wacce ta fashe da kukan Nadama,
gashi dukkaninsu na suffering daga mugun halinsu,
babu wanda ya tsira,
shiyasa akace Sharri dan aike ne, in ka aikashi dawowa yakeyi ya shafi wanda bai nan sanda kayi aiken,
tayi nadama matuka a yanzu da itama bata ga tsuntsu,
domin ko ďuriyar 'yayanta bata ji, har gara Radiya ta roki Shamsu ta waya yayi mata alkawarin yana dawowa italy zaizo su sasanta,
ita fa, babu waya daga Abbati bare har tasan ko har yanzu yana nan da ragowar soyayyarta a cikin ranshi,
Addu'a ta shiga yi ba kakkautawa tana faďawa Allah damuwarta haďe da neman afuwarshi.....
Cike da kulawa ya kalleta yace "Kuka ko?
Wa ya sa kanwata kuka har ya koďar min da idanuwanta?
Rufe fuskarta tayi da hijab kukan da ke tokare a wuyanta ya fito da karfinshi,
barinta yayi tayi ma'ishi sannan yace
"Me kike so?
Tell me ko me kike so zanyi miki in dai zai saki daina zubar hawaye kullum,
Junior ya faďa min bakya cin abinci,
bakya kula dashi,
har ihu kike mishi,
tell me ur problem,
i promise to solve it for u komin wahalarshi...
Hannunshi ta riko a hankali tace "With u my problems are always solved,
bani da wata matsala Uncle, thanks for always being dere for me....
Sanya hannun yayi ya share mata hawayenta shima duk gabban jikinshi a karye suke a zuciyarshi yace
"I will also solve this for u, sadaukarwa a soyayya wani abu ne,
i will make sure u get wat u want,
a fili kuma cewa yayi ta kwantar da hankalinta zai cigaba da solving ko wace irin matsala tata har ranar da kasa zata rufe idonshi..
kwantar da fuskarta tayi kan tafukan hannunshi wasu sabbin hawayen na zuba a kansu..
"Bari in tashi Junior yazo yaga shagwabar da baya yi Mamma nayi,
abin kunya ya faďi cike da zolaya yana girgiza kai,
Dariya tayi sosai tace
"Kai ka koya min, leka cikin motar tayi ta hangoshi kwance ya mike yana bacci,
"ya kamata ku tafi gida,
plss uncle kuyi bacci gobe kasan zakasha wahala sosai,
"Ai bakinki ne wahala,
ke zanma wannan faďan,
kuma ki tabbatar kinci abinci yanzu kafin ki kwanta,
inason gobe in ganki kinyi kiba kamar Husnah kina jina ko,
Buďe baki tayi tana dariya tace "sai dai in kamoka,
ko kuma------
Ihun da suka jiyo a cikin gidan ne yasata katse maganar da tayi niyya,
tabbas wannan muryar Hilal ce sai kuma ta Husna da ta biyo baya,
da sauri ya rufe kofar suka ruga ciki da gudu..
Ganin daukacin yan gidan sun nufi dakin da Musaddiq yake yasasu nufar ďakin suma,
a tare suka iso ciki da Daddy,
abin da suka tarar ne tada hankalinsu,
Hilal ne ke kokawar kwace kwalbar hannun Musaddiq ya kasa saboda wani irin karfi da ya karu wa Musaddiq,
sannan kuma girman ba ďaya ba, duk sauran yan uwanshi dake gurin sunyi yunkurin karba ya hanasu,
wannan karan a juye yake idanuwan nan a rufe wani sabon bacci ne ma yayi gaba dashi wanda daga gani kasan yana cikin mayen magani ne,
da sauri ta murďa kofar ta fita saboda kwalla da taji ta taru a idonta,
wannan wacce iriyar zazzafar jarabawa ce,
ya Allah ka kawo mana mafita baki dayanmu dan alfarmar annabi Muhammad s.a.w.....
Gidan Alhaji Mukhtar ya zama tamkar gidan zaman makoki, kamar babu wata hidima da za'ayi a cikinsa nan da kwana biyu,
Anty Reemah dasu Raudha sune kadai ke hidimarsu bisa ga umurnin Daddy,
sai kuma Mummy da a yanzu takan samu shigowa duba jikin Musaddiq,
duk da bata samun koda gaisawa da Daddy hakan yayi mata daďi tunda ya yafe mata kuma ya yafewa 'yayanshi yana sakar musu yanzu,
a yanzu bata da burin da ya wuce taga rayuwar Musaddiq ta inganta,
ta rasa kalmar da zata roki Nadeeyah dashi ta yarda da auren ďanta wanda ta zama sila a rabuwarsu,
gashi abun da tayi yayi sanadiyyar sanya shi cikin tsakiyar rayuwa da mutuwa...
A yau ma kamar kullum bayan ta gama gyara ďakin Goggo inda take kwana ta shirya tsaff dan tafiya dubo Musaddiq sannan ta zauna ayi kamun Nadeeyah da ita,
tana rufe kofa ta jiyo muryar Badariyya wacce a yanzu Yareemah Suhail ke fitowa da ita ya kawo ta har gida tun dawowar Nadeeyah,,
kwancen kayan da su Husna suka bata shi ta sanya tayi kyau abunta, sannan su suwidi suma sunyi kyansu dan a yanzu suna samun sake da kuma abinci wanda duk tazo sai yan uwa sun sai mata,
"A'a Badariyyah kece a gidan, to juya muje ki duba jikin Musaddiq daga nan ki jira ayi kamun Nadeeyah dake,
cike da damuwa ta juya suka fita suna tattauna damuwar da Musaddiq din ke ciki a sanadinsu, Badariyya a cikin ranta ta dau alwashin kebewa da Nadeeyah ta faďa mata abubuwan da tayi wanda ya rabasu, babu mamaki taji tausayinshi in tasan baya cikin hayyacinsa sanda yayi sakin....
Bayan ta gama sauraron kalaman Badariyya wanda takeyinsu cike da nadama tace
"Badariyya abun da kukayi bai isa ya raba mu ba,
tunda kika ga mun rabu to tabbas Allah ya rubuta rabuwar tamu ne a lokacin,
sannan a yanzu in na ki uncle Taheer shi munsan halin da zai shiga,
dan Allah ku fahimceni,
ni kadai nasan halin da nake ciki, ku tayani addu'a nasan komai zai daidaita da yardar Allah...
Share hawaye Badariyya tayi tace "Zamu tayaki, Allah yasa hakan shine mafi alkhairi....
Karfe huďu da yan mintuna Nadeeyah ta shirya cikin wani lace mai kyau da tsada cikin kayan da Taheer ya dinka mata, Anty Raly ke tsaye a kanta tana gyara mata kwalliyarta haďe da yi mata ďauri,
wata farar alkyabba mai adon yellow ta dauko ta daura mata a kanta wanda hakan ya sake fitar da kayatuwar da amaryar tayi, jan lallen da akayi mata ya rinu sosai ya koma dark maroon hakan ba karamin sake fitar da suffar yatsunta yayi ba,
zaunar da ita Anty Raly tayi tana jiyo sautin maganganu yan biki daga waje,,
Cike da masifa take shirya su Nour tana daka musu tsawar su tsaya ko ta zanesu,
a hankali Nadeeyah ta janyo hannun Abee tace
"Kawo in shiryashi Husna,
"Barshi.. kadai ta faďi haďe da janyo hannunshi ta sa mishi irin kayan dake jikin Hafeez,
oya a je ayi wasa, banda barna da bata jiki,
mikewa tayi da niyyar shiga bayi Nadeeyah ta riko hannunta,
"Husnah nasan ni mai laif---
Lokaci na kurewa Nadeeyah,
baki da laifin komai kaddararmu ce tazo a haka,
na kasa dai jin saukin zuciyata ne shiyasa har yanzun kika ganni haka,
with time in shaa Allah komai zai daidaita,
Husnah ta katseta fuskar nan murtuke tamkar wacce akayi ma mutuwa..
ganin Nadeeyah na kokarin sake magana yasata zame hannunta daga cikin nata ta faďa bayi,
wani irin kuka ne yazo musu a tare mai cin rai,
saida sukaci suka koshi sannan Husnah tayi wanka ta fito ta shirya da sauri sauri tayi waje....
Sai biyar da kusan rabi dangin Taheer suka zo sa lallen amarya, sai da suka biya kawayen amarya wacce Amal ce kaďai sai Raliya da ta shiga cikin zancen,
turaruka masu kamshin gaske suka karar a jikinta sauran yan uwansu na Agadez wadanda suka ji dadin ganin Nadeeyah da Hafeez suna rangaďa guďa,
kwaryar nono wacce suka kawo gidan kanta ta kai hamsin,
banda sauran gararrakin arziki da suka kawo,
sunci sun sha a gidan sosai dan komai nasu daban aka ware musu,
sai bayan Isha'i motocin da suka kawosu suka maida su....
A daddafe Musaddiq ya amsa gaisuwar Taheer wanda ke tsaye rike da danshi cikin tsadajjiyar shadda iri ďaya,
lallaba Junior ya shiga yi bayan ya fuskanci irin fushin da yakeyi dashi,
sannan kuma dan ya daukewa kanshi damuwar da ke cinshi tun kwana uku baya,
wani mugun tari yaji Musaddiq nayi wanda ya sanyashi sakin hannun Junior ya isa gareshi haďe da dauko ruwa yana faďin sannu, ga ruwa kasha,
runtse ido Musaddiq yayi haďe da kauda fuskarshi gefe,
ya riga ya gama yanke duk wani hukuncin da ya dace,
yasani a yanzu ganin gobe a gareshi nada matukar wahala, a yanzu ya sadaukar da komai yasan Nadeeyah da ďanshi bazasu taba yin kunci ba tunda suna tare da nagartaccen mutum irin Taheer wanda a haďuwarka dashi ta farko zata tabbatar da hakan komin kinka dashi,
dafe kanshi yayi da hannayenshi biyu saboda hawayen dake zubo mishi babu kakkautawa,
Mikewa Taheer yayi dukkan lakar jikinshi a sake ya kama hannun Junior suka sauka kasa,
a hanyar da zai sadasu da kofar fita ya haďu da Hilal da ya dawo daga rakiyar abokansu,
shima duk ya fukace ya fita hayyacinshi kamar shine mai ciwon,
"A'a yallabai har kun fito,
ya faďi yana mika mishi hannu,
"Eh dare nayi,
Allah ya bashi lafiya,
"Ameen Hilal ya amsa haďe cewa sai da safe mun gode,
"Allah ya tashemu lafiya Taheer yace yana mai saka kafarshi a waje,
A gurin motarshi suka tsaya ya kira number Nadeeyah wacce ke kan dadduma tana zubda kwallar da ta zame mata jiki,
a hankali ta ďauka cikin nuna bata cikin damuwa tace
"Uncle kun wuce ne?
"No muna waje,
muna san ganinki ne ya faďi wani ďaci na tokare makogaronshi,
Kara sassauta murya tayi tace "Gobe ne fa, daga gobe bazan sake barin gefenka ba, har sai ka gaji da ganina,
kayi hakuri plss,
Lumshe idanuwanshi yayi haďe da kallon sama a zuciyarshi yana rokon ubangiji sassauci akan wannan jarabawar,
*Tayi min tsauri da yawa* ya faďi ba tare da yasan ta fito ba, yana mai kwantar da kanshi kan murfin motar,
"Gani nan zuwa Uncle, in dai rashin ganina yayi maka tsauri, bakayi deserving shan wahala akaina ba,
bata jira amsarshi ba ta kashe wayar ta mike haďe da ninke dardumar tayi waje....
Duk abin nan da sukeyi a kunnen Raudha wacce ta fashe da kukan Nadama,
gashi dukkaninsu na suffering daga mugun halinsu,
babu wanda ya tsira,
shiyasa akace Sharri dan aike ne, in ka aikashi dawowa yakeyi ya shafi wanda bai nan sanda kayi aiken,
tayi nadama matuka a yanzu da itama bata ga tsuntsu,
domin ko ďuriyar 'yayanta bata ji, har gara Radiya ta roki Shamsu ta waya yayi mata alkawarin yana dawowa italy zaizo su sasanta,
ita fa, babu waya daga Abbati bare har tasan ko har yanzu yana nan da ragowar soyayyarta a cikin ranshi,
Addu'a ta shiga yi ba kakkautawa tana faďawa Allah damuwarta haďe da neman afuwarshi.....
Cike da kulawa ya kalleta yace "Kuka ko?
Wa ya sa kanwata kuka har ya koďar min da idanuwanta?
Rufe fuskarta tayi da hijab kukan da ke tokare a wuyanta ya fito da karfinshi,
barinta yayi tayi ma'ishi sannan yace
"Me kike so?
Tell me ko me kike so zanyi miki in dai zai saki daina zubar hawaye kullum,
Junior ya faďa min bakya cin abinci,
bakya kula dashi,
har ihu kike mishi,
tell me ur problem,
i promise to solve it for u komin wahalarshi...
Hannunshi ta riko a hankali tace "With u my problems are always solved,
bani da wata matsala Uncle, thanks for always being dere for me....
Sanya hannun yayi ya share mata hawayenta shima duk gabban jikinshi a karye suke a zuciyarshi yace
"I will also solve this for u, sadaukarwa a soyayya wani abu ne,
i will make sure u get wat u want,
a fili kuma cewa yayi ta kwantar da hankalinta zai cigaba da solving ko wace irin matsala tata har ranar da kasa zata rufe idonshi..
kwantar da fuskarta tayi kan tafukan hannunshi wasu sabbin hawayen na zuba a kansu..
"Bari in tashi Junior yazo yaga shagwabar da baya yi Mamma nayi,
abin kunya ya faďi cike da zolaya yana girgiza kai,
Dariya tayi sosai tace
"Kai ka koya min, leka cikin motar tayi ta hangoshi kwance ya mike yana bacci,
"ya kamata ku tafi gida,
plss uncle kuyi bacci gobe kasan zakasha wahala sosai,
"Ai bakinki ne wahala,
ke zanma wannan faďan,
kuma ki tabbatar kinci abinci yanzu kafin ki kwanta,
inason gobe in ganki kinyi kiba kamar Husnah kina jina ko,
Buďe baki tayi tana dariya tace "sai dai in kamoka,
ko kuma------
Ihun da suka jiyo a cikin gidan ne yasata katse maganar da tayi niyya,
tabbas wannan muryar Hilal ce sai kuma ta Husna da ta biyo baya,
da sauri ya rufe kofar suka ruga ciki da gudu..
Ganin daukacin yan gidan sun nufi dakin da Musaddiq yake yasasu nufar ďakin suma,
a tare suka iso ciki da Daddy,
abin da suka tarar ne tada hankalinsu,
Hilal ne ke kokawar kwace kwalbar hannun Musaddiq ya kasa saboda wani irin karfi da ya karu wa Musaddiq,
sannan kuma girman ba ďaya ba, duk sauran yan uwanshi dake gurin sunyi yunkurin karba ya hanasu,