Sashe 14
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sallama Daddy yayi ya karaso gurinsu cikin kunan rai,
zuciyarshi nata juya kalamansu,
lallai ya yarjewa kanshi duk zumuncin da ake samun tsaiko ko rashin jituwa a cikinshi daga tushe abin ke farawa,
duniya ina zaki damu, wannan shi ake kira da Zumuncin zamani,
tun ranar farko da ya fara ziyartar gidan da niyyar neman aure yasan akwai matsala a cikin zuri'ar,
ko gurin bashi auren yasan cewa suwaiba bata da galihu,
da tana da galihu da----- bismillah zauna mana Alhaji, "Goggo ta katse mishi zancen zucin da ya tafi na tunanin abubuwan da suka faru shekaru da dama,
zama yayi fuskar nan babu yabo ba fallasa,
a lokacin duk sauran yan yaran suka karaso,
Dakin ya musu kadan, amma haka suka rab'a suka zazzauna,
hankalinsu suka mayar gurin Baffa dan jin abin da yasa ya tarasu,
Da bismilla ya fara,
kowa ya shiga nutsuwarshi dan duk tunaninsu maganar da zai fada ta dattaku ce,
sai da ya fara jajantawa su Nadeeyah akan zazzafar rashin da sukayi,
sannan ya cigaba da cewa wannan mutuwar duk ta shafemu kuma ta taba mu fiye da tunanin me tunani,
Abun da yasa na taraku anan ba komai bane sai dan in fada muku na yanke shawarar yadda zamuyi da Nadeeyah da Zainab,
Kallon gefen da Hafeezu yake yayi yace "kai Hafeezu, kana da yarinyar da kake so?
Girgiza kai Hafeez yayi cikin rashin fahimta,
Baffa ya cigaba da cewa "to na baka nan da wata daya ka nemo yarinyar da zaka aura domin ta zo ta rike maka kannenka,
wani irin kallo mummy ta yi ma Baffa,
a lokacin in ranta yayi dubu to duk sun baci saboda a tunaninta Baffa ne zai rikesu Nadeeyah saboda sune suka fi cancanta da rikesu din,
maganar da Baffa ya cigaba dayi ne ta katse ta,
"abinda yasa nace haka, saboda kaga rabaku zai iya zama matsala,
duk inda kuka je bazaku ji dadin zama ba saboda kun saba da junanku, ku kadai kun isa ku debewa kanku kewar rashin iyayenku,
Goggo ta amshe da cewa kwarai kuwa, kuma kai Hafeezu hankalinka zai fi kwanciya in kasan kannenka na gurin ka,
fatanmu dai Allah yasa a samu mace ta gari,
Duk cikar gurin babu wanda maganarsu tayi mishi dadi,
har shi Baffa din bayan gama maganar saida yayi ajiyar zuciya sannan ya cigaba da zubda hawayen zuciya,
Anty Reemah ta bude baki zatayi magana Daddy ya rigata,
"kwarai kuwa Goggo shawararki tayi kuma na gamsu da ita dari bisa dari,
Musaddiq da Hilal na jin furucin Daddy wanda ya zama shine na karshe da ya rage suji me zaice, zuciyoyinsu suka tsinke a tare,
nan take kwalla ta taru a idon musaddiq da ya kalli gefen Nadeeyah da Hafeez yaga dukkaninsu kukan rashin gata sukeyi,
kallon bakin Daddy yayi da ya cigaba da cewa
"ba sai Hafeezu ya fita neman aure ba, ni nan zan bashi mata wacce nasan bazata cutar da kannenshi ba, Ya kalli Baffa da yayi kasake yana sauraronshi yace "ina son hada auren HAFEEZU da HUSNA.....
Kamar saukar aradu haka Goggo taji zancen, zaro ido tayi cike da firgici tace wace Husnan,
" *Husnah Mukhtar Kyari*,
Daddy ya fadi da gadara saboda yasan shi kadai keda iko da ita,,
Nawa Husnan take muntari, Goggo ta fadi tana share gumin daya fara tsatsasafowa a goshinta,
Daddy yace "Ita da Nadeeyah shekarunsu daya,
in har zamu iya barin Nadeeya ta rike kanta da zainab me zai hana mu hada auren da Husna sai su zauna su rike kansu gaba daya, jinin ai daya ne, babu wani bare ko Baffa,
wani irin murmushi Hilal yayi da karfi yace "You are the best grandpa..
Anty Reemah da ta harbo jirgin mahaifinta tayi saurin amsheshi da fadin "hakan shine daidai Daddy,
kaga basai ma an shigo da bare ba, kuma Husna ma ai ba yarinya bace, muma muna kamarta aka daura mana aure,
Allah ubangiji ya inganta wannan hadin...
sai dai ya inganta uwarki Goggo ta fadi ba tare da tasan ta danno ashar ba,
Kowa a gurin ya gimtse dariyarshi saboda sunsan yadda Goggo ke son Husna da Badariyya,
barin Husna ma son ta na musamman ne a ranta,
kullum hango Husna take cikin villar rahamaniya,
bazai yiwu ta bari rayuwar Husna ta kare a gurin wadannan masu kashin mindirikin ba,
Haukar gangan ta fara yi musu harda kuka wai Daddy yayi mata Gadara da diyarshi,
cikin sanyin murya Daddy yace "Goggo ba gadara bane, ai naga duk jikokin ne, tsatso daya suka fito, basu da wani banbanci,
cikin ficewar hayyaci tace "Allah ya kyauta wadannan masu kashin tsiyan su fito a tsatson---- da sauri mummy ta mike ta rufe mata baki tayi mata ihun da bata san ta mata shi ba,
itama a nata bangaren ko sama da kasa zasu hade bazata bar autarta ta auri Hafeez ba,
dan ta kawo karshen rigimar tayi kasa da murya mai alamar kuka tana matso hawaye tace "Rike su Nadeeyah bazai taba zame min matsala ba, basu da kowa sai ni, nice uwa kuma ubansu,
dangin mahaifinsu suna nesa damu "Aagadaz" ba nan kusa bane bare muce zamu tura wani nashi yazo,
durkusawa tayi gaban Daddy tace "dan Allah in bazaka damu ba zan rike yaran nan a gidanka,
ajiyar zuciya Daddy yayi cike da farin ciki yace "Babu wani matsala ai d'a duk na kowa ne, bare kuma yaran nan jininki ne,
Baffa farin ciki cike fal a zuciyarshi yace "Nagode nagode Alhaji Allah ya saka da alkhairi,
"babu komai Daddy ya fadi yana kallon Goggo dake zabga mishi harara,
zuciyarta cike take famm saboda bata san jinin suwaiba ya rabi kowa nata, bata ankara ba taji muryar Anty Reemah na cewa
"Mummy dan Allah ku bani daya daga cikinsu in tafi da ita, nima in samu ladan rikon maraya,,
Goggo ta kara hassala ta figi hijabinta a kan gado tace "ki je cikin kabari ki fito da Suwaiba da *ATIKA* ki hada duk ki tafi dasu.....
Banda Mummy da Baffa da suka san wacece Atika, babu wanda a cikinsu yasan wacece Atika??
Sunan Atika ya shiga yawo a kunnuwan dukkan yaran dake gurin.......WACECE ATIKA???? Shine tambayar da zuciyoyin mazauna gurin ke yi.......!
Mrs Tijjani Shattima......
[07/03 6:31 AM] fareedah: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 2⃣2⃣
By *Aysha Ya'u Kurah*
Share zufa Goggo tayi cike da tashin hankali tace "To Allah ya kaimu, sai kunzo,
Ajiyar zuciya Mummy tayi tace "to Goggo, amma bakya ganin fadin sirrin zai iya kawo karshen zama na da Muntari,
"Ko kusa, Goggo ta fadi cike da dakiya tace "in ya rabu dake ina zai kai yaran da kika haifa mishi, ai zancen rabuwa babu shi, domin kuwa yanzu girma ya kamaku, ki kwantar da hankalinki ni nasan abun da zanyi.....
Ajiye wayar Goggo tayi ta shiga safa da marwa a cikin dakinta,
Gumin dake tsatstsafowa a fuskarta bai tsaya ba duk ko da irin sanyin fankar dake kad'awa a dakin,
jiki na rawa ta haye can saman gadonta mai rumfa dakyar tana numfarfashi, ta mika hannu tayi ta dauko wani akushi,
bude cikin shi tayi ta zuraa mishi idonuwanta duk jikinta a sanyaye kamar wacce aka tsinkewa lakka,
nan take tunaninta ya tafi can shekaru da dama da suka wuce...
Shekarun da Allah subhanahu wa ta'ala ya arawa Goggo su,
Shekaru masu cike da abubuwan al'ajabi wadanda aka shafe tunaninsu a doron kasa...
"sau tari Allah na arawa mutane lokaci ko zasu samu su gyara abubuwan da sukeyi marasa kyau,
amma ita Goggo a gareta gani takeyi cancantarta ne yasa har yanzu Allah bai mata komai ba, saboda yasan irin gwagwarmayar da tasha ....
*********TARABA 1969*********
Kauyen *GEMBU* dake Karkashin karamar hukumar *SARDAUNA* a cikin jahar TARABA,
Babban kauye ne wanda yake cike da fulani arna da kuma tsirarun musulmai,
Irin arnan da babu abinda sukeyi a rayuwarsu sai kiwo da noma,
mazan su da matansu,
Hatta abin da zasu ci ma su suke noma shi da kansu,
Kauye ne inda babu wanda ya damu da addini bare har sukai ga assasa shi, "walau Addinin kirista ko na musulunci"
kowa harkar gabanshi yakeyi, da yawansu saboda rashin addini basu dauki kowacce irin mugunta a bakin komai ba, komai suke aikatawa a garin su a ganinsu dai dai ne......
Ihun shanaye ne kawai ke fitowa daga cikin wagegen bukkar gidan JAURO,
Samarin dake zaune a kofar gidan kowa ya fara gyara zaman jarkarshi dan sun san yanzu za'a fara kiran layi..
Cike da gadara ya ajiye jarkarshi a gaban ta kowa, ya koma jikin gidan yana sakuce hakorinshi..
Shuru sauran mutanen sukayi saboda tsoronshi da sukeji,
Cike da damuwa saurayin da ke zaune tun safe a gaba ya daga jarkarshi a kasa,
ya kuma ga in yayi shuru to fa za'a cuce shi,
Mikewa yayi cikin sanyi ya fara magana da gurbatacciyar hausarshi ta kabilun fulani
"Tun asuba nake nan,
kayi hakuri can tsauni zan kai madara kaga da nisa banasan dare yayi mana,
bude idoo saurayin yayi cike da gatsali yace "amma kai bako ne anan ko?
gyada kai saurayin yayi yace "eh a can tsaunin Mambila nake,
nazo siyan madara ne akwai bakin da suka zo daga Cameroon zasu tafi anjima da maraice kuma suna son madara irin ta gidan jauro, shine nazo siya, kayi hakuri a bamu, tare muke da yar su gata can a zaune duk ta gaji,
Dago kai saurayin me suna SHAHO yayi ya kalli gurin bishiyar da saurayin ya nuna mishi,
kyakyawar budurwa ya hango zaune a gefen bishiyar fuskarta da alamun gajiya,
da ganinta kasan ba yar nigeria bace,
jikinta rufe yake ruff da bakar riga har kanta,
sandar dake hannunshi ya ajiye yace "a zuba maka in ma jarkar da ka kawo sun kai goma,
kanshi ya fara kakkabewa ya fara nufar inda budurwar take,
Da sauri saurayin ya taro shi yace "ina zaka je?
Yarinyar nan bata jin hausa haka fulatanci, larabci kadai take ji, kayi hakuri muyi abinda ya kawo mu, mu tafi mu bar muku garinku,
zuciyarshi nata juya kalamansu,
lallai ya yarjewa kanshi duk zumuncin da ake samun tsaiko ko rashin jituwa a cikinshi daga tushe abin ke farawa,
duniya ina zaki damu, wannan shi ake kira da Zumuncin zamani,
tun ranar farko da ya fara ziyartar gidan da niyyar neman aure yasan akwai matsala a cikin zuri'ar,
ko gurin bashi auren yasan cewa suwaiba bata da galihu,
da tana da galihu da----- bismillah zauna mana Alhaji, "Goggo ta katse mishi zancen zucin da ya tafi na tunanin abubuwan da suka faru shekaru da dama,
zama yayi fuskar nan babu yabo ba fallasa,
a lokacin duk sauran yan yaran suka karaso,
Dakin ya musu kadan, amma haka suka rab'a suka zazzauna,
hankalinsu suka mayar gurin Baffa dan jin abin da yasa ya tarasu,
Da bismilla ya fara,
kowa ya shiga nutsuwarshi dan duk tunaninsu maganar da zai fada ta dattaku ce,
sai da ya fara jajantawa su Nadeeyah akan zazzafar rashin da sukayi,
sannan ya cigaba da cewa wannan mutuwar duk ta shafemu kuma ta taba mu fiye da tunanin me tunani,
Abun da yasa na taraku anan ba komai bane sai dan in fada muku na yanke shawarar yadda zamuyi da Nadeeyah da Zainab,
Kallon gefen da Hafeezu yake yayi yace "kai Hafeezu, kana da yarinyar da kake so?
Girgiza kai Hafeez yayi cikin rashin fahimta,
Baffa ya cigaba da cewa "to na baka nan da wata daya ka nemo yarinyar da zaka aura domin ta zo ta rike maka kannenka,
wani irin kallo mummy ta yi ma Baffa,
a lokacin in ranta yayi dubu to duk sun baci saboda a tunaninta Baffa ne zai rikesu Nadeeyah saboda sune suka fi cancanta da rikesu din,
maganar da Baffa ya cigaba dayi ne ta katse ta,
"abinda yasa nace haka, saboda kaga rabaku zai iya zama matsala,
duk inda kuka je bazaku ji dadin zama ba saboda kun saba da junanku, ku kadai kun isa ku debewa kanku kewar rashin iyayenku,
Goggo ta amshe da cewa kwarai kuwa, kuma kai Hafeezu hankalinka zai fi kwanciya in kasan kannenka na gurin ka,
fatanmu dai Allah yasa a samu mace ta gari,
Duk cikar gurin babu wanda maganarsu tayi mishi dadi,
har shi Baffa din bayan gama maganar saida yayi ajiyar zuciya sannan ya cigaba da zubda hawayen zuciya,
Anty Reemah ta bude baki zatayi magana Daddy ya rigata,
"kwarai kuwa Goggo shawararki tayi kuma na gamsu da ita dari bisa dari,
Musaddiq da Hilal na jin furucin Daddy wanda ya zama shine na karshe da ya rage suji me zaice, zuciyoyinsu suka tsinke a tare,
nan take kwalla ta taru a idon musaddiq da ya kalli gefen Nadeeyah da Hafeez yaga dukkaninsu kukan rashin gata sukeyi,
kallon bakin Daddy yayi da ya cigaba da cewa
"ba sai Hafeezu ya fita neman aure ba, ni nan zan bashi mata wacce nasan bazata cutar da kannenshi ba, Ya kalli Baffa da yayi kasake yana sauraronshi yace "ina son hada auren HAFEEZU da HUSNA.....
Kamar saukar aradu haka Goggo taji zancen, zaro ido tayi cike da firgici tace wace Husnan,
" *Husnah Mukhtar Kyari*,
Daddy ya fadi da gadara saboda yasan shi kadai keda iko da ita,,
Nawa Husnan take muntari, Goggo ta fadi tana share gumin daya fara tsatsasafowa a goshinta,
Daddy yace "Ita da Nadeeyah shekarunsu daya,
in har zamu iya barin Nadeeya ta rike kanta da zainab me zai hana mu hada auren da Husna sai su zauna su rike kansu gaba daya, jinin ai daya ne, babu wani bare ko Baffa,
wani irin murmushi Hilal yayi da karfi yace "You are the best grandpa..
Anty Reemah da ta harbo jirgin mahaifinta tayi saurin amsheshi da fadin "hakan shine daidai Daddy,
kaga basai ma an shigo da bare ba, kuma Husna ma ai ba yarinya bace, muma muna kamarta aka daura mana aure,
Allah ubangiji ya inganta wannan hadin...
sai dai ya inganta uwarki Goggo ta fadi ba tare da tasan ta danno ashar ba,
Kowa a gurin ya gimtse dariyarshi saboda sunsan yadda Goggo ke son Husna da Badariyya,
barin Husna ma son ta na musamman ne a ranta,
kullum hango Husna take cikin villar rahamaniya,
bazai yiwu ta bari rayuwar Husna ta kare a gurin wadannan masu kashin mindirikin ba,
Haukar gangan ta fara yi musu harda kuka wai Daddy yayi mata Gadara da diyarshi,
cikin sanyin murya Daddy yace "Goggo ba gadara bane, ai naga duk jikokin ne, tsatso daya suka fito, basu da wani banbanci,
cikin ficewar hayyaci tace "Allah ya kyauta wadannan masu kashin tsiyan su fito a tsatson---- da sauri mummy ta mike ta rufe mata baki tayi mata ihun da bata san ta mata shi ba,
itama a nata bangaren ko sama da kasa zasu hade bazata bar autarta ta auri Hafeez ba,
dan ta kawo karshen rigimar tayi kasa da murya mai alamar kuka tana matso hawaye tace "Rike su Nadeeyah bazai taba zame min matsala ba, basu da kowa sai ni, nice uwa kuma ubansu,
dangin mahaifinsu suna nesa damu "Aagadaz" ba nan kusa bane bare muce zamu tura wani nashi yazo,
durkusawa tayi gaban Daddy tace "dan Allah in bazaka damu ba zan rike yaran nan a gidanka,
ajiyar zuciya Daddy yayi cike da farin ciki yace "Babu wani matsala ai d'a duk na kowa ne, bare kuma yaran nan jininki ne,
Baffa farin ciki cike fal a zuciyarshi yace "Nagode nagode Alhaji Allah ya saka da alkhairi,
"babu komai Daddy ya fadi yana kallon Goggo dake zabga mishi harara,
zuciyarta cike take famm saboda bata san jinin suwaiba ya rabi kowa nata, bata ankara ba taji muryar Anty Reemah na cewa
"Mummy dan Allah ku bani daya daga cikinsu in tafi da ita, nima in samu ladan rikon maraya,,
Goggo ta kara hassala ta figi hijabinta a kan gado tace "ki je cikin kabari ki fito da Suwaiba da *ATIKA* ki hada duk ki tafi dasu.....
Banda Mummy da Baffa da suka san wacece Atika, babu wanda a cikinsu yasan wacece Atika??
Sunan Atika ya shiga yawo a kunnuwan dukkan yaran dake gurin.......WACECE ATIKA???? Shine tambayar da zuciyoyin mazauna gurin ke yi.......!
Mrs Tijjani Shattima......
[07/03 6:31 AM] fareedah: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 2⃣2⃣
By *Aysha Ya'u Kurah*
Share zufa Goggo tayi cike da tashin hankali tace "To Allah ya kaimu, sai kunzo,
Ajiyar zuciya Mummy tayi tace "to Goggo, amma bakya ganin fadin sirrin zai iya kawo karshen zama na da Muntari,
"Ko kusa, Goggo ta fadi cike da dakiya tace "in ya rabu dake ina zai kai yaran da kika haifa mishi, ai zancen rabuwa babu shi, domin kuwa yanzu girma ya kamaku, ki kwantar da hankalinki ni nasan abun da zanyi.....
Ajiye wayar Goggo tayi ta shiga safa da marwa a cikin dakinta,
Gumin dake tsatstsafowa a fuskarta bai tsaya ba duk ko da irin sanyin fankar dake kad'awa a dakin,
jiki na rawa ta haye can saman gadonta mai rumfa dakyar tana numfarfashi, ta mika hannu tayi ta dauko wani akushi,
bude cikin shi tayi ta zuraa mishi idonuwanta duk jikinta a sanyaye kamar wacce aka tsinkewa lakka,
nan take tunaninta ya tafi can shekaru da dama da suka wuce...
Shekarun da Allah subhanahu wa ta'ala ya arawa Goggo su,
Shekaru masu cike da abubuwan al'ajabi wadanda aka shafe tunaninsu a doron kasa...
"sau tari Allah na arawa mutane lokaci ko zasu samu su gyara abubuwan da sukeyi marasa kyau,
amma ita Goggo a gareta gani takeyi cancantarta ne yasa har yanzu Allah bai mata komai ba, saboda yasan irin gwagwarmayar da tasha ....
*********TARABA 1969*********
Kauyen *GEMBU* dake Karkashin karamar hukumar *SARDAUNA* a cikin jahar TARABA,
Babban kauye ne wanda yake cike da fulani arna da kuma tsirarun musulmai,
Irin arnan da babu abinda sukeyi a rayuwarsu sai kiwo da noma,
mazan su da matansu,
Hatta abin da zasu ci ma su suke noma shi da kansu,
Kauye ne inda babu wanda ya damu da addini bare har sukai ga assasa shi, "walau Addinin kirista ko na musulunci"
kowa harkar gabanshi yakeyi, da yawansu saboda rashin addini basu dauki kowacce irin mugunta a bakin komai ba, komai suke aikatawa a garin su a ganinsu dai dai ne......
Ihun shanaye ne kawai ke fitowa daga cikin wagegen bukkar gidan JAURO,
Samarin dake zaune a kofar gidan kowa ya fara gyara zaman jarkarshi dan sun san yanzu za'a fara kiran layi..
Cike da gadara ya ajiye jarkarshi a gaban ta kowa, ya koma jikin gidan yana sakuce hakorinshi..
Shuru sauran mutanen sukayi saboda tsoronshi da sukeji,
Cike da damuwa saurayin da ke zaune tun safe a gaba ya daga jarkarshi a kasa,
ya kuma ga in yayi shuru to fa za'a cuce shi,
Mikewa yayi cikin sanyi ya fara magana da gurbatacciyar hausarshi ta kabilun fulani
"Tun asuba nake nan,
kayi hakuri can tsauni zan kai madara kaga da nisa banasan dare yayi mana,
bude idoo saurayin yayi cike da gatsali yace "amma kai bako ne anan ko?
gyada kai saurayin yayi yace "eh a can tsaunin Mambila nake,
nazo siyan madara ne akwai bakin da suka zo daga Cameroon zasu tafi anjima da maraice kuma suna son madara irin ta gidan jauro, shine nazo siya, kayi hakuri a bamu, tare muke da yar su gata can a zaune duk ta gaji,
Dago kai saurayin me suna SHAHO yayi ya kalli gurin bishiyar da saurayin ya nuna mishi,
kyakyawar budurwa ya hango zaune a gefen bishiyar fuskarta da alamun gajiya,
da ganinta kasan ba yar nigeria bace,
jikinta rufe yake ruff da bakar riga har kanta,
sandar dake hannunshi ya ajiye yace "a zuba maka in ma jarkar da ka kawo sun kai goma,
kanshi ya fara kakkabewa ya fara nufar inda budurwar take,
Da sauri saurayin ya taro shi yace "ina zaka je?
Yarinyar nan bata jin hausa haka fulatanci, larabci kadai take ji, kayi hakuri muyi abinda ya kawo mu, mu tafi mu bar muku garinku,