← Book details Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 111 OF 113

Sashe 111

Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"To ina nan dai ina zuba ido, nasan dai baka saba alkawari bansani ba ko ka koya kasan shekarun da yawa,

Dariya suka saki a tare saboda yasan tabbas tsokanarshi takeyi,

"In ma na koya bazan so in gwada miki shi ba,
domin an daďe ba'a hadu ba, ya kamata a barwa juna memories masu daďi bayan rabuwa,
ina nan zuwa,
just a second plss inada baki zan kiraki,
bai jira jin amsarta ba ya kashe wayar ya cigaba da duba abubuwan da aka kawo mishi...

*BAYAN RABUWA*

Shi ta dinga maimaitawa a cikin ranta,
yana tunanin rabuwa da ita kenan bayan shekarun da suka dauka basuga juna ba,
har yanzu Mukhtar baya tunaninta kamar yadda tayi a baya da kuma yanzu da ganinshi ya tado mata matacciyar soyayyarshi....

*Flash back a gurguje*

_Shekaru da dama da suka wuce Allah ya jarabci Anty Saude da Soyayyar abokin makocinsu kuma malaminta wanda yake mata lesson Uncle Abubakar, a duk lokacin da uncle Abu yazo yi mata lesson Kyari kan je gidansu yayi ta tsokanarta musamman in akazo kan mathematics, tun abun na bata haushi har ya rikiďe ya koma birgeta, in yana tsokanarta sai ta biye mishi suyi tayi har lokacin tashi lesson yayi ba'a tabuka mata wani abun arziki ba, in Kyari yayi tafiya babu zancen karatu ta dinga damun uncle Abu kenan tana tambayarshi ranar da zai dawo, kasancewarsu dukkansu 'yayan masu kudin lokacin sai ya zamana tasu tazo daya musamman ta bangaren Anty Saude, ita duk a tunaninta soyayya ce ke kawo Kyari (kamar yadda taji uncle Abu na cewa) gurinta, bata san shakuwar da sukayi da Abubakar tun suna makaranta ita ce ta sanya ďaya baya barin daya ba, a ranar da ta yanke shawarar faďa mishi abinda ke ranta a ranar taji mummunan labari daga gareshi na haďuwa da wata yar makaranta wacce ya kwallafawa ran aurenta, cikin sanyin jiki ta tattara takardunta tace ma Uncle Abu bata da lafiya, bata tsaya duba kulawar da Kyari ke kokarin nunawa a gareta ba ta wuce cikin gida idanuwanta na zubar da hawaye, tasan tabbas kyari ya faďa cikin tarkon so domin a yadda ta kula baya son kula mata gashi da yawan kushesu tasan wannan din da ya gani ta dabance, a daren ranar taci kuka har ta gode Allah sannan ta roki Allah da ya kawo mata wanda zai aureta cikin gaggawa ko ta samu ta mance *Mukhtar Garba Kyari*..._

Washe gari da safe da taje gaida Mahaifinta  Alhaji Halliru Ďan Magarya, bayan sun gaisa yake tambayarta yaushe zasu fara jarabawa,
cike da damuwa ta amsa mishi da cewa
"Jibi in shaa Allah,
"Mashaa Allah Mamana,
Allah yasa ku rubuta alkhairi, yasa ku fito da sakamako mai kyau, tunda an kusa zana jarabawar karshe sai maganar aure,
shin kina da wanda kike so?
nasan dai bazaki rasa ba kar inyi miki katsalandan,

Kauda kanta gefe tayi dan bata so sam mahaifinta ya gane halin da take ciki tace
"A'a Pappa, duk wanda ka zabar min ina maraba dashi,

Cike da murna yace
"Mashaa Allah, shiyasa nake daďa sonki a cikin raina,
sai yanzu na fahimci dalilin da yasa Allah ya mallaka min ke kadai,
saboda yasan ke ďin daya ce tamkar da dubu,
Allah yayi miki albarka,
ki shirya gobe,
Haroun Yallo dan wazirin Agadez zaizo neman aurenki,
satin da ya wuce da naje Agadez na bawa mahaifinshi ke,
shi mazaunin nan ne, a nan yake kasuwancinshi,
Allah ya sanyawa haďin albarka,

Amsa mishi tayi da Ameen sannan ta tashi ta wuce ďaki tana kuka ririss....

Bayan tayi candy da sati biyu aka daura aurenta da Haroun,
da fari ta dan samu matsalar zama dashi saboda tunanin kyari da takewa son da bai san tanayi ba,
sai daga baya kyautatawar Haroun ta kashe boyayyar soyayyar cikin zuciyarta...

Ashe dai soyayyar ba mutuwa tayi ba,
ashe doguwar suma tayi,
wanda a yanzu ruwan soyayyar Daddy ya farfaďo da ita...

Ajiyar Zuciya tayi tace
"Wannan karan bazan rasaka ba Kyari,
koda zuciyarka bata sona zan koyar da ita yadda zatayi shi,
a yanzu na haďu da kai bayan na cire rai da sake yin wata soyayya bare har inyi aure,
haduwarmu dakai ta nuna min tabbas kai ďin nawa ne koda kuwa ba nawa bane ni kadai, rabuwa a tsakanin mu babu ita saidai mutuwa ka raba,
tana kaiwa nan ta tashi ta nufi daki dan sakeyin wani wankan....

Da ido Shareefah ta bita tana mata adduar samun abinda take so,
domin Allah ma yasan tayi hakurin rashin miji a gefenta, yadda ta damu da maganar Kyari ta tabbatar tana matukar sonshi, zata tayata da addu'a in alkhairi ne Allah ya tabbatar.....

Bayan isha'i Daddy yazo gidan, tarba mai kyau ya samu daga dukkansu harda Taheer wanda a yanzu yake matukar jin kunyar haďa ido dashi, kimarshi ta karu sosai a idonshi..

Bayan sun gama gaisawa Anty Saude ta cika gabanshi da abinci da sha,
zama tayi a gefenshi tana mishi hira yana cin abinci suna tuntsira dariyar tuna baya,
sosai sukayi hirarsu har Daddy yakai karfe goma bai san ya kai ba,
yayi matukar jin daďin hira da ita, zuciyarshi da tayi mishi nauyi ta rage saboda ta tuno mishi da memories ďin baya,
lokacin yana kan ganiyarshi, bashi da wani bacin rai sai tarin farin ciki musamman lokacin haďuwarshi da Suwaiba....

Rike murfin motar tayi bayan ta gama jin tambayarshi na
"Bayan biki zaki koma can canada ne?

Kallonshi takeyi cikin ido dan jinta takeyi kamar yar budurwar da ta fara tsayawa da saurayi tace

"In ka shirya komawa can me zai hana!

Dariya Daddy yayi yace
"Wato dai kin maidani joker, karfin ramawa ne bani dashi da kema kinsan bazaki sha ba,
dare na daďa yi bari in wuce,

Ina miki fatan alkhairi haďe da murnar samun suruka irin Nadeeyah,
Allah ya basu zaman lafiya...

"Ameen Anty Saude tace haďe da rufe mishi kofar cike da tausayawa halin da ďanshi yake ciki,
ya zatayi ta iya yin wannan taimakon?
Ya zatayi da zuciyar tata ďan in ya rasa Nadeeyah,
Addu'a ita kadai ce mafita a garesu domin Allah shine kadai mai sassautawa....

Bayan tafiyarshi da awa ďaya ta tura mishi text din godiya da ban gajiya sannan tace
"Akwai muhimmin abun da zan faďa maka,
in shaa Allahu bayan biki komai zai ziyarci ji da ganinka,
have a nice dream *Joker* ...

Dariyar rashin shiri Daddy yayi ya kashe wutar dakin da Musaddiq yake ya fita daga dakin, saida yayi shirin kwanciya sannan ya tura mata cewa...

*Same Sauden Himma, Amaryar gandiroba...*

Dariya sosai tayi na tuno sunan Himma,, gandiroban da ya like mata lokacin yarintarta,
ashe bai manta ba ta furta a hankali cike da nishaďi,

*Soyayya ruwan zuma, ita soyayya babu ruwanta da tsufan mutum, in ta kama ka dole ta zautaka*.....

Good morning bride,
Maleekah ta faďi tana haďawa Little Nadeeyah tea,

Rau Rau Nadeeyah tayi da idonta haďe da kwabe baki zatayi kuka,

"Hey, ba ruwana fa,
kiyi saving kukan nan zuwa anjima ki sakarwa Abbu shi,
kinsan yau zasu zo bikin unknown jika... ta karashe cike da zolaya,
kafaďunta Nadeeyah ta daka haďe da haďiye da kukan dake shirin zubo mata,

Dariya Maleekah tayi tace
"Let it flow beb,
kinsan in daďi yayi maka yawa hawaye kansu dadin fita sukeji,

My Inlaw da ciwo ke da kuka,
nd for once baki taba tunanin zuwa dubashi ba,
haba Nadeeyah,
if nt for him sai kiyi for his child, kinsan duk inda kikaje that child will always connect u saboda ya riga ya haďaku...

Share hawaye Nadeeyah tayi ta juya ma Maleekah baya,
zancen zuci takeyi wasu hawayen na sake bulbulowa,
rabon da tasa shi a idonta tun ranar mutuwar Goggo da ta shiga ďakin dan duba jikinshi lokacin yana bacci,
bata san abun da zai sake sawa ya ganta domin bata san yi mishi fami akan abun da take da yakinin yana yunkurin mantawa dashi,
kwana uku ya rage ta zama mallakin wani,
runtse idonta tayi saboda hangota cikin wata sabuwar rayuwa,
rayuwa ba tare da Mussadiq ba,
wanda ya fara koyar da ita soyayya,
wanda ya shayar da ita gubar soyayyar da ya illata ruhinta...

"Go nd see him for the last tym Nadeeyah,
atleast zai samu sukunin cewa kin damu dashi, kaddara ce zata rabaku, plsss Nadeeyah..
ta karashe haďe da hada hannayenta guri ďaya tana rokonta... duk wadannan maganganun cikin harcen turanci take yinsu...

Share hawaye Nadeeyah tayi da Hijab dinta ta fara tafiya dan bin umarnin yar uwarta,
tana zuwa kofar dakin taji kafarta ta fara rawa,
dakyar ta iya murďa kofar tana addu'ar Allah yasa yana bacci,

Ajiyar zuciya tayi bayan ta gansu kwance suna bacci shi da junior da fushi ya hanashi kwana a gurinta,
shagala tayi cikin kallonsu tanajin wata irin nutsuwa na saukar mata a curarrar zuciyarta,
ko ba komai hankalinta ya kwanta tunda Junior ya saki jiki da mahaifinshi,
ko a yanzu tasan Musaddiq zai samu saukin kaso 50 cikin ďari...

Cikin sanďa ta isa gurin gadon dan gyarawa Junior hannu dan gab yake da famawa Musaddiq ciwon dake hannunshi wanda hakan zaiyi sanadiyyar katsewar baccin da ta tabbatar yana jin dadinsa,
da dabara ta gyara mishi taji ya rikota yana sambatun
"Daddy am very angry with u, i will nt talk to u ever again,

Dariya tayi haďe da sumbatar kumatunshi ta zame hannunta cikin nashi,
bargon dake jikinsu ta gyara musu ta shafa kan Junior ta dago da niyyar yin hanyar waje,
kamar gizo haka taga idon Musaddiq a buďe,
sake juyowa tayi ta kalleshi tagansu a rufe,
ajiyar zuciya tayi ta fara tafiya dan zuwa kofar da zata sadata da waje,

"Nadeeyah...

Taji ya furta a hankali wanda ya sanya hantar cikinta kadawa,
tsayawa tayi cakk a gurin ba tare da ta amsa ko ta waigo ta kalleshi ba..
Chapter 111 · 0% Book details