Sashe 13
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta window Badariyya take lekensu daya bayan daya,
Husna da dawowarta daga saloon kenan ta fito daga bayi tana kallon Badariyya a jikin Window tana leke,
murmushi tayi ta zira Hijab dinta ta fito tsakar gidan tana ma mummy barka da dawowa, dan ita ba gidan rasuwar take kwana ba,
gidan Anty Raudha take bin ta su kwana,
yau ne kadai bata je gidan rasuwar ba taje saloon dan wanke kanta,
Anty Radiya da Anty Raudha suka kalleta cike da shakiyanci suka ce "Amarsu ta ango,
cikin rashin fahimta ta waiga bayanta taga babu kowa tace
"wacece haka? Dariya suka kwashe da ita suka ce ke mana!
Zatayi Magana Anty Reemah tace "wani irin sakarci ne wannan, ku dan matsa daga can mu wuce sai ku cigaba da shakiyancin tunda sa'arku ce Husnan,
darewa sukayi ta wuce ita da Anty Raliya, harara Raudha tabi Raliya dashi tayi tsaki tana kunkuni a ranta,
"su in an barsu mutanen kirki, Radiya tace "manta dasu dallah, taja Husna sukayi ciki,
mummy tayi kamar bata jinsu tace ma Nadeeyah su kamo kayan su shigo,
A d'arare ta dauki jakar ta fara tafiya, kama gefen jakar Hinad tayi suka karasa cikin parlon,
wani irin faduwar gaba Nadeeyah taji,
idanuwanta suka ciko da kwalla,
tuno abubuwa mabanbanta da suka faru da mahaifiyarta na rashin dadi ta dingayi,
wani lungu ta zauna inda suka saba zama da mahaifiyarta in sunzo gidan.....
Labulen windon Badariyya ta saki kirjinta kamar zai fado saboda bakin ciki,
bata hango Nadeeyah ba, amma ganin Zainab a gurin Musaddiq suna magana yana dariya ya tabbatar mata da lallai su Nadeeyah sun dawo gidansu da zama,
bata karasa tunaninta ba taji an shigo dakin ana dariya,
Cikin kaguwa Husnah tace
"Anty Raudha tell me, waye amaryar plss,
Radiya ta ajiye yaronta Fadeel a kan gadon tayi hanyar bayi tace
"ke mana, kece amaryar Hafeez,
wata dariyar suka sake kecewa da ita sannan Radiya ta shige bayi,
Husnah ta turnube fuska tace "wani Hafeez din,
Anty Raudha tace "Hafeez din mama Suwaiba mana,
kaff ta kwashe labarin abinda ya faru ta fadawa Husna suka karashe da dariya dukkaninsu,
Badariyya tayi tsaki mai karfi tace "da an hadasu din, da zaifi mana alkhairi walhy,
domin zuwansu nan din gaskiya akwai matsala,
bama mai yiwuwa bane zamansu anan!! ta karasa fadi a gadarance,
"Saboda kece mai gidan ko,
Raliya da shigowarta kenan ta fadi tana harararta,
Raudha tayi tsaki tace "nima zamansu anan din walhy bana sanshi,
ni fa Allah ya sani na tsani talaka,
ko sunan talauci banasan ji,
Radiya daga bayi ta dago murya tace "ai talauci masifa ne, ni na rasa laifin me talaka yayiwa Allah,
subhanallahi!!! Raliya tayi saurin cewa, ya salam, ku kuwa kuji tsoron Allah,
talaucin nan fa wadanda suke cikinsa basu suka sawa kansu ba,
kuma basu isa su cireshi ba sai Allah yaso,
haka zalika arzikin da kuke ciki baku kuka bawa kanku ba,
babu banbanci tsakaninmu, tunda duk abinda da talaka zaiyi mai kudi ma zaiyi,
wadatar zuci tafi komai a rayuwa,
suma Allah bai mance dasu ba,
kuyi fatan kar Allah ya jarbceku da dandana rayuwar talauc-----
"" eeeeeeh eeeh wait hang it, Radiya tayi saurin katseta,
" har abada bazamu taba dandanawa ba "idiotic being, saboda muna sharhi kan talauci shine zaki rabashi jikinmu,
to we reject it walhy, sakarai kawai,,
uhmmm kawai Raliya tace ta fita tana mamakinsu,
har ta kure dakin bata daina jiyo muryoyinsu ba....
Har karfe biyar na yamma Nadeeyah na zaune a inda take, da himilin kayansu,
anan taci abincin da me aikinsu ta zubo mata,
tana kallon dukkan ahalin mummy a cikin parlon ana hira,
Anty Reemah ce kawai bata cikinsu, dan ita tun zuwansu suka wuce can gidansu ita dasu Hinad,
ba yadda Hinad batayi tazo su tafi ba taki,
kwanciyar hankalinta daya zainab ta bisu shiyasa ma zaman bai gundureta ba,
gyangyadi ta farayi a zaune ta jiyo muryar Badariyya tana zuba rashin kunya tana fadin "wallahi mummy indai yarinyar can zata zauna a gidan nan ni bazan zauna ba,
saidai ku zabi daya,
janyota mummy tayi jikinta tace "haba baby,
kiyi hakuri mana, dalili ne yasa zata zauna, kiyi hakuri pls na lokaci ne, kuma kinga makaranta zata koma,
ba ganinta zaki dinga yi kullum ba,
Keyn mota Raliya ta dauka a kan center table, ta dauki danta tace "Mummy sai anjimanku,
tayi hanyar waje ba tare da ta jira amsarsu ba,
badan a karkashin wani take ba, wallhy babu abinda zai hanata tafiya da Nadeeyah,
mutuwa mai tonan asiri, duk talaucinsu basa zuwa gurinsu maula,
rikon na Nadeeyah nawa yake?
abinci ne fa kadai sai gurin kwanciya, sai dan kyautatawar yau da kullum,
share kwallar idonta tayi ta shiga motar tana fadin, "ya Allah ka raya mu cikin ya'yanmu....
Dakyar mummy ta shawo kan Badar ta yarda, da sharadin a dakin mai aikinsu Nadeeyah zata zauna,
dan ita sam bazata iya hada daki da Nadeeyah ba,
dan a samu kwanciyar hankali mummy ta yarda amma can cikin ranta badan taso ba,
Husna ma abin ya mata zafi sosai,
Raudha da Radiya kuwa tsaff suka goyi bayan Badar...
Dakin mai aikin nasu ma da d'an kyanshi,
kayanta kawai ta shigar ciki ta fada bayi,
sai da tayi kuka mai isarta sannan tayi wanka ta daura alwala ta fito...
A inda ta idar da sallar ishaa bacci yayi gaba da ita,
sai ajiyar zuciya take cikin baccinta,
mai aikin nasu yar dattijuwa ce, taji tausayinta matuka, ta kuma yi tirr da hali irin nasu mummy, masu yin watsi da jininsu saboda talauci, tashinta tayi ta maida ita kan gado taja mata abun rufa......
Mrs Tijjani Shattima........!
[07/03 6:31 AM] fareedah: ●ZUMUNCINMU A YAU● 1⃣8⃣
By Aysha Ya'u Kurah
Tsakurar abincin dake gabanta takeyi tana juya cokalin,
ta rasa menene asalin abinda take ji cikin ranta,
farin cikin sanin halin da Nadeeyah ke ciki na rashin iyayenta takeyi ko kuwa bakin cikin tarewar da kowa yayi a gidansu Nadeeyan,
Mutuwar mamma na iskarta tayi murmushin farin ciki,
tasan Nadeeyah na can cikin radadin da ta sanya ta,
saidai takaicinta daya musaddiq sam baya yarda su hadu, duk wata kafa da zata sadasu ya tosheta, dan sam baya son jin ko muryarta,
wani irin tsanarta yakeji a zuciyarshi na rashin imaninta,
babu wanda bai ziyarci gidan mutuwar ba sai ita,
kullum tana zaune a gida daga kallo sai cin abinci sai game,
babu yadda mummy batayi ba akan tazo gidan mutuwar tun farkon yin ta, amma sam taki zuwa,
gashi wata mutuwar ta sake bullo kai...
Tura abincin gefe tayi ta mike ta wuce daki dan ta watsa ruwa, ita kadai ta kwana a gidan, sai daddy da taji tashin motarshi da asuba tasan shima a gidan ya kwana,
ko gezau bata ji ba a zuciyarta bare ta karaya ta shirya zuwa gidan su Nadeeyan,
ita sam bata san zafin mutuwa ba, a ganinta kuncin da Nadeeyah ta sanyata yafi zafi akan radadin mutuwa, tsaki taja hade da wurgi da kayan jikinta ta fada bayi......
***********
Bayan doguwar addu'ar da aka gabatar a kofar gidan malam Adamu na sadakar ukun mamma Suwaiba,
sadakar abinci akayi sosai,
duk wanda yake gurin saida ya wadatu da abinci saboda yawanshi, cikin kankanin lokaci jama'a suka watse ya rage saura makusanta kawai,
Baffa da shock din mutuwar bai sakeshi ba har lokacin ya mike kamar ba laka a jikinshi ya shige cikin gidan,
Saida ya zauna yana maida numfashi sannan ya dubi gurin da mummy da Goggo ke magana,
fada mummy keyi akan rashin zuwan Badariyya,
ita kuwa goggo goyon bayan Badariyya take hade da fadin "kinsan yarinya ce kuma bata san hayaniya, duk mu da muka zauna a gidan har kwana uku bamu wakilceta ba,
Baffa dai kallonsu yakeyi zuciyarshi na tafasa amma bakinshi yayi nauyi ya gaza furta koda kalma daya ce,
Hinad dake zaune can gefe kusa da Nadeeyah ya yafito da hannu alamar tazo,
da sauri ta karaso gabanshi tace gani Baffa, cikin murya mai rauni yace, taje ta kira Hafeezu da Daddy a waje,
sai a sannan mummy tasan da shigowarshi, karasowa tayi ta zauna kusa dashi tace
"Baffa yaushe ka shigo, murmushin yake yayi yace "yanzun nan,
tafi ki kirawo min dukkan ya'yanki akwai maganar da nake so muyi daku, kai ta gyada tace "to Baffa, ta mike ta fita tsakar gidan,
Zama Goggo tayi tana matsa mishi hannu hade da cewa duk kwana ukun nan baka da wani kuzari,
mutuwar nan fa ba a kanta aka fara yi maka ba,
ka rasa uwa, uba, mata, da ya'ya,
saidai wannan mutuwar na lura tafi razana ka,
wanda ni bansan dalili ba,
mutuwa daya ce, in mutum yayi ta baya dawowa, inda ana dawowa sai ince ka cigaba da damuwar, watakil damuwar taka na iya dawo da ita,
ya kamata ka sanya wa kanka nutsuwa kayi tawakkali,
Hawayen da ya zubo a gefen idonshi ya share zuciyarshi na rawa yace "Asama'u! duk mutuwar da akemin ta Suwaiba tafi tsaya min,
kinfi kowa sanin hal---- da sauri ya dauke idonshi cikin nata, ya kauda kanshi ya canza maganar da cewa "ina matukar tausayin halin da yaran nan zasu shiga ne, waye zai rike su? Ina zasu je?
Goggo tayi saurin cewa "ai Nadeeya ta mallaki hankalin kanta,
sannan ga Hafeezu shi zai fito da mata yayi aure sai ya hada ya rikesu gaba daya,
in suka zauna anan shine hankalinsu zaifi kwanciya, d'an abun da baza'a rasa ba ma dinga taimaka musu,
ai su yan gata ne, tunda akwai Hafeezu, kuma su uku ne zasu dinga ganin junansu,
kama kwantar da hankalinka akan maganarsu babu abinda zai samesu,
ake mutuwa abar jariri ma bare su da suka mallaki hankalin kansu,
Daddy dake tsaye cike da al'ajabin kalaman Goggo ya kasa motsawa bare yayi magana,
jiran ta bakin Baffa kadai yake in hukuncin da zai yanke mai yiwuwa ne,
A d'arare Baffa yace "eh kuma haka ne kema kin kawo shawara,
rabasu din baida amfani gara Hafeezu yayi aure ya rike kannanshi tunda yanzu da dan jari a hannunshi,
yanzu bari Hafizun yazo sai mu ce mishi ya fito da matar da zai aura cikin gaggawa, kuma ya gyara gidannan ya zauna da matarshi ta rike mishi kannenshi...
Husna da dawowarta daga saloon kenan ta fito daga bayi tana kallon Badariyya a jikin Window tana leke,
murmushi tayi ta zira Hijab dinta ta fito tsakar gidan tana ma mummy barka da dawowa, dan ita ba gidan rasuwar take kwana ba,
gidan Anty Raudha take bin ta su kwana,
yau ne kadai bata je gidan rasuwar ba taje saloon dan wanke kanta,
Anty Radiya da Anty Raudha suka kalleta cike da shakiyanci suka ce "Amarsu ta ango,
cikin rashin fahimta ta waiga bayanta taga babu kowa tace
"wacece haka? Dariya suka kwashe da ita suka ce ke mana!
Zatayi Magana Anty Reemah tace "wani irin sakarci ne wannan, ku dan matsa daga can mu wuce sai ku cigaba da shakiyancin tunda sa'arku ce Husnan,
darewa sukayi ta wuce ita da Anty Raliya, harara Raudha tabi Raliya dashi tayi tsaki tana kunkuni a ranta,
"su in an barsu mutanen kirki, Radiya tace "manta dasu dallah, taja Husna sukayi ciki,
mummy tayi kamar bata jinsu tace ma Nadeeyah su kamo kayan su shigo,
A d'arare ta dauki jakar ta fara tafiya, kama gefen jakar Hinad tayi suka karasa cikin parlon,
wani irin faduwar gaba Nadeeyah taji,
idanuwanta suka ciko da kwalla,
tuno abubuwa mabanbanta da suka faru da mahaifiyarta na rashin dadi ta dingayi,
wani lungu ta zauna inda suka saba zama da mahaifiyarta in sunzo gidan.....
Labulen windon Badariyya ta saki kirjinta kamar zai fado saboda bakin ciki,
bata hango Nadeeyah ba, amma ganin Zainab a gurin Musaddiq suna magana yana dariya ya tabbatar mata da lallai su Nadeeyah sun dawo gidansu da zama,
bata karasa tunaninta ba taji an shigo dakin ana dariya,
Cikin kaguwa Husnah tace
"Anty Raudha tell me, waye amaryar plss,
Radiya ta ajiye yaronta Fadeel a kan gadon tayi hanyar bayi tace
"ke mana, kece amaryar Hafeez,
wata dariyar suka sake kecewa da ita sannan Radiya ta shige bayi,
Husnah ta turnube fuska tace "wani Hafeez din,
Anty Raudha tace "Hafeez din mama Suwaiba mana,
kaff ta kwashe labarin abinda ya faru ta fadawa Husna suka karashe da dariya dukkaninsu,
Badariyya tayi tsaki mai karfi tace "da an hadasu din, da zaifi mana alkhairi walhy,
domin zuwansu nan din gaskiya akwai matsala,
bama mai yiwuwa bane zamansu anan!! ta karasa fadi a gadarance,
"Saboda kece mai gidan ko,
Raliya da shigowarta kenan ta fadi tana harararta,
Raudha tayi tsaki tace "nima zamansu anan din walhy bana sanshi,
ni fa Allah ya sani na tsani talaka,
ko sunan talauci banasan ji,
Radiya daga bayi ta dago murya tace "ai talauci masifa ne, ni na rasa laifin me talaka yayiwa Allah,
subhanallahi!!! Raliya tayi saurin cewa, ya salam, ku kuwa kuji tsoron Allah,
talaucin nan fa wadanda suke cikinsa basu suka sawa kansu ba,
kuma basu isa su cireshi ba sai Allah yaso,
haka zalika arzikin da kuke ciki baku kuka bawa kanku ba,
babu banbanci tsakaninmu, tunda duk abinda da talaka zaiyi mai kudi ma zaiyi,
wadatar zuci tafi komai a rayuwa,
suma Allah bai mance dasu ba,
kuyi fatan kar Allah ya jarbceku da dandana rayuwar talauc-----
"" eeeeeeh eeeh wait hang it, Radiya tayi saurin katseta,
" har abada bazamu taba dandanawa ba "idiotic being, saboda muna sharhi kan talauci shine zaki rabashi jikinmu,
to we reject it walhy, sakarai kawai,,
uhmmm kawai Raliya tace ta fita tana mamakinsu,
har ta kure dakin bata daina jiyo muryoyinsu ba....
Har karfe biyar na yamma Nadeeyah na zaune a inda take, da himilin kayansu,
anan taci abincin da me aikinsu ta zubo mata,
tana kallon dukkan ahalin mummy a cikin parlon ana hira,
Anty Reemah ce kawai bata cikinsu, dan ita tun zuwansu suka wuce can gidansu ita dasu Hinad,
ba yadda Hinad batayi tazo su tafi ba taki,
kwanciyar hankalinta daya zainab ta bisu shiyasa ma zaman bai gundureta ba,
gyangyadi ta farayi a zaune ta jiyo muryar Badariyya tana zuba rashin kunya tana fadin "wallahi mummy indai yarinyar can zata zauna a gidan nan ni bazan zauna ba,
saidai ku zabi daya,
janyota mummy tayi jikinta tace "haba baby,
kiyi hakuri mana, dalili ne yasa zata zauna, kiyi hakuri pls na lokaci ne, kuma kinga makaranta zata koma,
ba ganinta zaki dinga yi kullum ba,
Keyn mota Raliya ta dauka a kan center table, ta dauki danta tace "Mummy sai anjimanku,
tayi hanyar waje ba tare da ta jira amsarsu ba,
badan a karkashin wani take ba, wallhy babu abinda zai hanata tafiya da Nadeeyah,
mutuwa mai tonan asiri, duk talaucinsu basa zuwa gurinsu maula,
rikon na Nadeeyah nawa yake?
abinci ne fa kadai sai gurin kwanciya, sai dan kyautatawar yau da kullum,
share kwallar idonta tayi ta shiga motar tana fadin, "ya Allah ka raya mu cikin ya'yanmu....
Dakyar mummy ta shawo kan Badar ta yarda, da sharadin a dakin mai aikinsu Nadeeyah zata zauna,
dan ita sam bazata iya hada daki da Nadeeyah ba,
dan a samu kwanciyar hankali mummy ta yarda amma can cikin ranta badan taso ba,
Husna ma abin ya mata zafi sosai,
Raudha da Radiya kuwa tsaff suka goyi bayan Badar...
Dakin mai aikin nasu ma da d'an kyanshi,
kayanta kawai ta shigar ciki ta fada bayi,
sai da tayi kuka mai isarta sannan tayi wanka ta daura alwala ta fito...
A inda ta idar da sallar ishaa bacci yayi gaba da ita,
sai ajiyar zuciya take cikin baccinta,
mai aikin nasu yar dattijuwa ce, taji tausayinta matuka, ta kuma yi tirr da hali irin nasu mummy, masu yin watsi da jininsu saboda talauci, tashinta tayi ta maida ita kan gado taja mata abun rufa......
Mrs Tijjani Shattima........!
[07/03 6:31 AM] fareedah: ●ZUMUNCINMU A YAU● 1⃣8⃣
By Aysha Ya'u Kurah
Tsakurar abincin dake gabanta takeyi tana juya cokalin,
ta rasa menene asalin abinda take ji cikin ranta,
farin cikin sanin halin da Nadeeyah ke ciki na rashin iyayenta takeyi ko kuwa bakin cikin tarewar da kowa yayi a gidansu Nadeeyan,
Mutuwar mamma na iskarta tayi murmushin farin ciki,
tasan Nadeeyah na can cikin radadin da ta sanya ta,
saidai takaicinta daya musaddiq sam baya yarda su hadu, duk wata kafa da zata sadasu ya tosheta, dan sam baya son jin ko muryarta,
wani irin tsanarta yakeji a zuciyarshi na rashin imaninta,
babu wanda bai ziyarci gidan mutuwar ba sai ita,
kullum tana zaune a gida daga kallo sai cin abinci sai game,
babu yadda mummy batayi ba akan tazo gidan mutuwar tun farkon yin ta, amma sam taki zuwa,
gashi wata mutuwar ta sake bullo kai...
Tura abincin gefe tayi ta mike ta wuce daki dan ta watsa ruwa, ita kadai ta kwana a gidan, sai daddy da taji tashin motarshi da asuba tasan shima a gidan ya kwana,
ko gezau bata ji ba a zuciyarta bare ta karaya ta shirya zuwa gidan su Nadeeyan,
ita sam bata san zafin mutuwa ba, a ganinta kuncin da Nadeeyah ta sanyata yafi zafi akan radadin mutuwa, tsaki taja hade da wurgi da kayan jikinta ta fada bayi......
***********
Bayan doguwar addu'ar da aka gabatar a kofar gidan malam Adamu na sadakar ukun mamma Suwaiba,
sadakar abinci akayi sosai,
duk wanda yake gurin saida ya wadatu da abinci saboda yawanshi, cikin kankanin lokaci jama'a suka watse ya rage saura makusanta kawai,
Baffa da shock din mutuwar bai sakeshi ba har lokacin ya mike kamar ba laka a jikinshi ya shige cikin gidan,
Saida ya zauna yana maida numfashi sannan ya dubi gurin da mummy da Goggo ke magana,
fada mummy keyi akan rashin zuwan Badariyya,
ita kuwa goggo goyon bayan Badariyya take hade da fadin "kinsan yarinya ce kuma bata san hayaniya, duk mu da muka zauna a gidan har kwana uku bamu wakilceta ba,
Baffa dai kallonsu yakeyi zuciyarshi na tafasa amma bakinshi yayi nauyi ya gaza furta koda kalma daya ce,
Hinad dake zaune can gefe kusa da Nadeeyah ya yafito da hannu alamar tazo,
da sauri ta karaso gabanshi tace gani Baffa, cikin murya mai rauni yace, taje ta kira Hafeezu da Daddy a waje,
sai a sannan mummy tasan da shigowarshi, karasowa tayi ta zauna kusa dashi tace
"Baffa yaushe ka shigo, murmushin yake yayi yace "yanzun nan,
tafi ki kirawo min dukkan ya'yanki akwai maganar da nake so muyi daku, kai ta gyada tace "to Baffa, ta mike ta fita tsakar gidan,
Zama Goggo tayi tana matsa mishi hannu hade da cewa duk kwana ukun nan baka da wani kuzari,
mutuwar nan fa ba a kanta aka fara yi maka ba,
ka rasa uwa, uba, mata, da ya'ya,
saidai wannan mutuwar na lura tafi razana ka,
wanda ni bansan dalili ba,
mutuwa daya ce, in mutum yayi ta baya dawowa, inda ana dawowa sai ince ka cigaba da damuwar, watakil damuwar taka na iya dawo da ita,
ya kamata ka sanya wa kanka nutsuwa kayi tawakkali,
Hawayen da ya zubo a gefen idonshi ya share zuciyarshi na rawa yace "Asama'u! duk mutuwar da akemin ta Suwaiba tafi tsaya min,
kinfi kowa sanin hal---- da sauri ya dauke idonshi cikin nata, ya kauda kanshi ya canza maganar da cewa "ina matukar tausayin halin da yaran nan zasu shiga ne, waye zai rike su? Ina zasu je?
Goggo tayi saurin cewa "ai Nadeeya ta mallaki hankalin kanta,
sannan ga Hafeezu shi zai fito da mata yayi aure sai ya hada ya rikesu gaba daya,
in suka zauna anan shine hankalinsu zaifi kwanciya, d'an abun da baza'a rasa ba ma dinga taimaka musu,
ai su yan gata ne, tunda akwai Hafeezu, kuma su uku ne zasu dinga ganin junansu,
kama kwantar da hankalinka akan maganarsu babu abinda zai samesu,
ake mutuwa abar jariri ma bare su da suka mallaki hankalin kansu,
Daddy dake tsaye cike da al'ajabin kalaman Goggo ya kasa motsawa bare yayi magana,
jiran ta bakin Baffa kadai yake in hukuncin da zai yanke mai yiwuwa ne,
A d'arare Baffa yace "eh kuma haka ne kema kin kawo shawara,
rabasu din baida amfani gara Hafeezu yayi aure ya rike kannanshi tunda yanzu da dan jari a hannunshi,
yanzu bari Hafizun yazo sai mu ce mishi ya fito da matar da zai aura cikin gaggawa, kuma ya gyara gidannan ya zauna da matarshi ta rike mishi kannenshi...