Sashe 71
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
parlon ya shiga ya tarar da Hafeez a kimtse yana zaune yana jiran azo kiranshi,
cike da zolaya ya dan naushi cikin Jamal dake kishingide yana game,
mikewa yayi yana dariya yace
"har ka iso,
"wallahi kuwa.. ban dade da shigowa ba,
mun sameku lafiya?
lafiya lau Hafeez yace yana kallon idon Hilal,
"yaushe ďana ya zama makaho?
Ya tambaya yana dariya,
shima Hilal dariyar yayi yace
"fashion ne kawu karami,
dariya mai sauti dukkansu sukayi suka hau wata hirar ta daban....
Inaa Amaryar take!!!!
Hajiya Aliya ta tambaya hade da bankado kofar dakin su Husnah,
lokacin Musaddiq na manne da ita kamar zai maida ita jikinshi,
samm baiji kunyar kawayensu dake gurin ba,
shigowar su Hajiya Aliya ne ya sanyashi matsawa kadan hade da gaishesu, amma har lokacin hannunshi na cikin nata..
Harara Hajiya Aliya ta watsa mishi sannan ta bude fuskar Nadeeyah da iya karfinta,
"auuu kece amaryar,
iko sai Allah,
ashe Hajiya Zainab munafurtarmu tayi Hajja Asiya,
"ashe dama tasan auren zumunci zasuyi ma dansu shine ta daura ma diyata dakon son da yake neman zamewa zuciyarta illa,
waigowa tayi ta kalli Mummy da tayi tsamo tsamo saboda kunya da takaici tace
"Wallahi tallahi Zainabun Muntari bashi kika ci,
na rantse da wanda raina ke hannunshi ni Aliya bazan kyaleku ba,
sai na sa kun muzanta a idon duniya,
yanda kikayi wasa da rayuwar 'yata kema sai nayi da ta naki yayan,
mu zuba mu gani,
wuce muje Hajja Asiya ta karashe hade da buga kofar dakin tana huci,
Kuka sosai Mummy ta fashe dashi hade da ficewa daga dakin itama,
a rude Musaddiq ya saki hannun Nadeeyah ya bi bayanta hankali a tashe,
itama Nadeeyar mikewa tayi tana share hawayen da ya ziraro mata tana kokarin bin bayan Mummy Anty Raly ta dakatar da ita,
zaunar da ita tayi ta rarrasheta da kalamai masu dadi da kwantar da hankali,
jakarta ta ajiye kusa da ita tace "ki kular min da jakar nan, yanzu zan dawo...
Sau uku wayar dake cikin jakar na ringing Nadeeyah na kin dauka, saboda bata san bude ajiyar da aka bata,
a na biyar ne ta bude ta fito da Wayar,
*Tahir Legacy*
ta gani a rubuce,
da sauri ta ajiye wayar saboda wani irin mugun faduwar gaba da taji,
"uncle Taheer ta fadi a cikin ranta,
gaba daya ta manta dashi a cikin rayuwarta,
gashi yanzu zata sake yi mishi mantuwar din din din,
bai fasa kira ba har saida ta gaji ta dauki wayar zata kaima Anty Raly sai a sannan taga wani suna daban,
*Aunt S 2*
a gaggauce ta dauka tace
"Assalamu Alaikum bari in kai mata...
yadda yayi haddar sanyin muryarta dake yawan yawo cikin kanshi ya tabbatar mishi da itace,
"My omri is going lv me,
dagaske ne?
Chakkk ta tsaya da tafiyar da ta farayi,
cire wayar tayi a kunnenta ta sake kallonta dan ta tabbatar da ko dai sunan gizo yayi mata,
maida wayar kunnenta tayi zatayi magana yayi saurin cewa
"tell me plss,
zama ta koma tayi tace
"ina wuni,
"Nadeeyah plss answr me,
"ummm dagaske ne, ta bashi amsa a hankali...
ji yayi gaba daya ya kusa zubewa a kasa,
dama lokacin da yagani a status din sabrinah saida yayi jinyar magudanar jininshi na dan lokaci,
hawayen da ya ziraro mishi ya share,
yace
"but why Nadeeyah,
why??
Cikin rawar Murya tace "Kaddara ta ce haka,
kayi min addu'a Allah yasa auren ya zame min alkhairi,
kayi hakuri uncle,
Allah ya baka wacce ta fini a komai da kake so,
bata jira jin amsarshi ba ta kashe wayar ta dunkule kanta guri daya, dama dakin babu kowa dan Husna sun fita da Hafeez da kawayensu.....
Kaga abun da ka janyo min ko Musaddiq,
kaga irin cin mutuncin da ka janyo min gurin aminai na,
yanzu gaba daya kawayena zasuyi Allah wadai dani,
saida na fada maka Nadeeyah ba alkhairi bace a gareni ka nace saboda kaga jar fata da kyawun dan maciji wanda zai diga maka dafin sa ya tafi ya barka da ciwo,
Wallahi Musaddiq ka cuceni kuma ka cuci kanka....
Anty Reemah ce ta zauna kusa da ita tace haba Mummy,
matar mutum fa kabarinsa,
kuma babu wanda yasan alkhairin dake tattare da auren Nadeeyah sai ubangijin halittu,
yanzu ita wacce kike so din me tafi Nadeeyah dashi,
"Gata da hanyoyin alkhairi, Mummy ta bata amsa tana harararta,
"Hanyoyin alkhairi ai na ubangiji ne,
shi ke budeshi ga wanda yaso,
sai kiga auren Nadee---
a harzuke ta katseta da cewa
"in kika kara magana zan balain saba miki,
mahaukaciyar banza sakaryar hofi,
tashi ki fita ki bani guri, shashasha kawai...
Rai a bace Anty Reemah ta tashi ta fita daga dakin,
Matsowa Musaddiq yayi ya share mata hawaye hade da kwantar mata da hankalin cewa ta kwantar da hankalinta,
babu abun da zai faru,
domin shi zai gyara komai,
Hannunshi Mummy ta kama tace
"Little ka taimakeni,
bayan auren da kake so kayi wanda nake so,
ka auri Faida,
shi kadai ne zai sanya hankalina ya kwanta, in kuma aminta da Nadeeya a matsayin matarka,
shuru yayi na dan lokacin zuciyarshi na harbawa da karfi,
tunanin mafita ya shiga yi,
Dakyar ya sama wa kanshi mafitar amincewa,
dan a samu zaman lafiya,
amma ko yayi hauka bazai auri Faida ba,
daga ya tafi da Nadeeyarsa lagos bazai kara waiwayosu ba sai yayi shekaru,
ganin ya amince zai auri Faida yasa Mummy farin ciki sosai har ta kira aminanta ta fada musu.....
Sai bayan Magriba akayi kamun amare,
"Mami da Anni su suka kama Husna,
sai Anty Reemah da sauran yan uwanta sukayi ma Nadeeyah,
Mummy ma in ka ganta zaka dauka albishir akayi mata da gidan aljanna saboda murna,
Rawa kam kawayen Amare da yan uwa suyi ta sosai har saida suka kure mawakin,
sai kusan goma makadin ya tattara kayanshi yayi gaba da tarin alkhairai masu yawa,
su kuwa kawayen suka koma dakin kwanansu suka cigaba da hirarsu ta yammata,
rabin hirar tasu ma akan Badar ta kare saboda sun so tana nan akayi bikin.....
Rana bata karya....
A ran 23 ga watan yuli..
ranar sati da safe dubban jama'a suka shaida daurin auren
*Musaddiq Mukhtar Kyari* da *Nadeeyah Adam*
da kuma auren
*Hafeez Adam* da *Husnah Mukhtar Kyari*...
Marokin gurin na gama sanarwa Jamal yayi dariya sosai yace
"vice versa,
gyara bakin madubi Hilal yayi yace
"ai fa, abin ya burgeni,
Allah ya basu zaman lafiya..
saura mu,
matsowa Jamal yayi yace
"ai ni nama gama samu,
saidai fatan dacewa,
jira kawai nakeyi komai ya lafa in aika sakon zuciyata,
bazan tsaya kallon ruwa kwado yayi min kafa ba....
"Kamar yadda Nayi Hilal ya fadi a cikin zuciyarshi..
amma a fili cewa yayi
"woww kace anjima akwai gist,
"Sosai ma In law...
au My son ya karashe yana dukan bakinshi..
Mikewa Hilal yayi yana kyakyata dariya yace
"ka tona kanka malam,
muje gurin walima kafin mutumin ya fara kumburi.....
Wannan kukan da kikeyi bazai taimakeki ba Amarya,
dama kinci abinci,
da kin samu sauki,
"Kinsan adadin matan da suka shigo gidannan ta haka kuwa?
to ki sani bake bace ta farko kuma bana tunanin zaki zamo ta karshe,
da yawa irin ku son duniyan iyayenku ke ja muku,
saboda son abun duniya sai idonsu ya rufe suyi kyautar da zata damesu nan gaba,
ta shi kici abincin,
kingani harda Farfesun Zomo,
ga tuwon lapshi miyar yauki gaskiya ke yar gata ce, dan abin bauta Garzar ki rage min, ta karashe tana turo langar tuwon gabanta,
Kafa Badariyya tasa ta ture langar tuwon,
nan naman ya zube a kasa,
komai ya bayyanar mata,
kan zomo ne da kayan cikinshi,
sai tsirarrun nama,
da sauri kande da ta durkusa tafara kwashe naman tana suďe hannu kamar mayya wacce tayi sabon kamu,
Idon da ya soye da bakin ciki Badariyya ta bita dashi tana hawayen zuci,
"wannan wace iriyar jarabawa ta fado,
kalmar na shiga uku har lokacin bata bar fita daga bakin Badar ba,
tana kallo kande ta sude gurin tass kamar an goge sannan ta russuna tace
"Ranki ya dade,
ko bakya jin yunwa bai kamata ki wulakanta abinci ba,
wannan naman yanzu da zan fita dashi tsakar gida sai an kusa kaini kasa saboda wawason shi,
ki daure kici ko kadan ne saboda kar yareemah yayi fada,
tsakii mai karfi Badariyya taja hade da sake yin tagumi tana tunanin way out..
Shigowar Yareemah ne yasanya kande fita da sauri bayan ta gaisheshi...
Zama yayi a gefen Badar hade da dauko langar farfesun...
"Sauka ki zauna a kasa ki cinyeshi tass domin ki samu karfin jikinki,
a fusace Badar ta mike tace "wannan kazantar ce zata sa in samu karfi a jikina,
wallahi kaji na rantse bazan zauna a gidannan ba,
kukan bakin ciki ta fasa mishi tace
"wallahi in na fita a gurin nan sunanku sorry, domin sai na gayyato muku sojoji sun tada wannan tsinannan kau----
"keeee...
ya katseta cike da tsawa,
nan take fuskarshi ta sauya yace "Zauna maza ki cinye abin dake cikin kwanukan nan,
"Bazan ci ba!
Nace bazan ci ba ka kashe n----
wani farin haske ne ya wuce ta makogoronta ya hanata Magana,
sai ma bin umarnin shi da ta fara yi...
tare suka zauna ya bata abincin a baki ta cinye tass cikin ficawar hayyaci,
tana gama shan ruwa ya umurceta da ta fitar da kwanukan waje,
ba musu ta kwashesu ta fitar dasu ta dawo dakin ta zauna a nutse,
mikewa yayi ya dawo inda take hade da kamo hannuwanta,
"ki kwantar da hankalinki, nima mutum ne kamar ki,
saidai mu Allah yayi mana baiwar sanin wasu abubuwa,
Tun kafin nayi auren farko lokacin ina yaro mahaifiyarki ta bani ke saboda jin dadi wani aiki da mahaifina yayi mata,
tun daga ranar muke kula da duk wani motsinta,
a ranar da aka haifeki mahaifina yayi murna domin a tunaninshi namiji zata haifa,
tun daga wannan lokacin muke bibiyar dukkan sawunki,
cike da zolaya ya dan naushi cikin Jamal dake kishingide yana game,
mikewa yayi yana dariya yace
"har ka iso,
"wallahi kuwa.. ban dade da shigowa ba,
mun sameku lafiya?
lafiya lau Hafeez yace yana kallon idon Hilal,
"yaushe ďana ya zama makaho?
Ya tambaya yana dariya,
shima Hilal dariyar yayi yace
"fashion ne kawu karami,
dariya mai sauti dukkansu sukayi suka hau wata hirar ta daban....
Inaa Amaryar take!!!!
Hajiya Aliya ta tambaya hade da bankado kofar dakin su Husnah,
lokacin Musaddiq na manne da ita kamar zai maida ita jikinshi,
samm baiji kunyar kawayensu dake gurin ba,
shigowar su Hajiya Aliya ne ya sanyashi matsawa kadan hade da gaishesu, amma har lokacin hannunshi na cikin nata..
Harara Hajiya Aliya ta watsa mishi sannan ta bude fuskar Nadeeyah da iya karfinta,
"auuu kece amaryar,
iko sai Allah,
ashe Hajiya Zainab munafurtarmu tayi Hajja Asiya,
"ashe dama tasan auren zumunci zasuyi ma dansu shine ta daura ma diyata dakon son da yake neman zamewa zuciyarta illa,
waigowa tayi ta kalli Mummy da tayi tsamo tsamo saboda kunya da takaici tace
"Wallahi tallahi Zainabun Muntari bashi kika ci,
na rantse da wanda raina ke hannunshi ni Aliya bazan kyaleku ba,
sai na sa kun muzanta a idon duniya,
yanda kikayi wasa da rayuwar 'yata kema sai nayi da ta naki yayan,
mu zuba mu gani,
wuce muje Hajja Asiya ta karashe hade da buga kofar dakin tana huci,
Kuka sosai Mummy ta fashe dashi hade da ficewa daga dakin itama,
a rude Musaddiq ya saki hannun Nadeeyah ya bi bayanta hankali a tashe,
itama Nadeeyar mikewa tayi tana share hawayen da ya ziraro mata tana kokarin bin bayan Mummy Anty Raly ta dakatar da ita,
zaunar da ita tayi ta rarrasheta da kalamai masu dadi da kwantar da hankali,
jakarta ta ajiye kusa da ita tace "ki kular min da jakar nan, yanzu zan dawo...
Sau uku wayar dake cikin jakar na ringing Nadeeyah na kin dauka, saboda bata san bude ajiyar da aka bata,
a na biyar ne ta bude ta fito da Wayar,
*Tahir Legacy*
ta gani a rubuce,
da sauri ta ajiye wayar saboda wani irin mugun faduwar gaba da taji,
"uncle Taheer ta fadi a cikin ranta,
gaba daya ta manta dashi a cikin rayuwarta,
gashi yanzu zata sake yi mishi mantuwar din din din,
bai fasa kira ba har saida ta gaji ta dauki wayar zata kaima Anty Raly sai a sannan taga wani suna daban,
*Aunt S 2*
a gaggauce ta dauka tace
"Assalamu Alaikum bari in kai mata...
yadda yayi haddar sanyin muryarta dake yawan yawo cikin kanshi ya tabbatar mishi da itace,
"My omri is going lv me,
dagaske ne?
Chakkk ta tsaya da tafiyar da ta farayi,
cire wayar tayi a kunnenta ta sake kallonta dan ta tabbatar da ko dai sunan gizo yayi mata,
maida wayar kunnenta tayi zatayi magana yayi saurin cewa
"tell me plss,
zama ta koma tayi tace
"ina wuni,
"Nadeeyah plss answr me,
"ummm dagaske ne, ta bashi amsa a hankali...
ji yayi gaba daya ya kusa zubewa a kasa,
dama lokacin da yagani a status din sabrinah saida yayi jinyar magudanar jininshi na dan lokaci,
hawayen da ya ziraro mishi ya share,
yace
"but why Nadeeyah,
why??
Cikin rawar Murya tace "Kaddara ta ce haka,
kayi min addu'a Allah yasa auren ya zame min alkhairi,
kayi hakuri uncle,
Allah ya baka wacce ta fini a komai da kake so,
bata jira jin amsarshi ba ta kashe wayar ta dunkule kanta guri daya, dama dakin babu kowa dan Husna sun fita da Hafeez da kawayensu.....
Kaga abun da ka janyo min ko Musaddiq,
kaga irin cin mutuncin da ka janyo min gurin aminai na,
yanzu gaba daya kawayena zasuyi Allah wadai dani,
saida na fada maka Nadeeyah ba alkhairi bace a gareni ka nace saboda kaga jar fata da kyawun dan maciji wanda zai diga maka dafin sa ya tafi ya barka da ciwo,
Wallahi Musaddiq ka cuceni kuma ka cuci kanka....
Anty Reemah ce ta zauna kusa da ita tace haba Mummy,
matar mutum fa kabarinsa,
kuma babu wanda yasan alkhairin dake tattare da auren Nadeeyah sai ubangijin halittu,
yanzu ita wacce kike so din me tafi Nadeeyah dashi,
"Gata da hanyoyin alkhairi, Mummy ta bata amsa tana harararta,
"Hanyoyin alkhairi ai na ubangiji ne,
shi ke budeshi ga wanda yaso,
sai kiga auren Nadee---
a harzuke ta katseta da cewa
"in kika kara magana zan balain saba miki,
mahaukaciyar banza sakaryar hofi,
tashi ki fita ki bani guri, shashasha kawai...
Rai a bace Anty Reemah ta tashi ta fita daga dakin,
Matsowa Musaddiq yayi ya share mata hawaye hade da kwantar mata da hankalin cewa ta kwantar da hankalinta,
babu abun da zai faru,
domin shi zai gyara komai,
Hannunshi Mummy ta kama tace
"Little ka taimakeni,
bayan auren da kake so kayi wanda nake so,
ka auri Faida,
shi kadai ne zai sanya hankalina ya kwanta, in kuma aminta da Nadeeya a matsayin matarka,
shuru yayi na dan lokacin zuciyarshi na harbawa da karfi,
tunanin mafita ya shiga yi,
Dakyar ya sama wa kanshi mafitar amincewa,
dan a samu zaman lafiya,
amma ko yayi hauka bazai auri Faida ba,
daga ya tafi da Nadeeyarsa lagos bazai kara waiwayosu ba sai yayi shekaru,
ganin ya amince zai auri Faida yasa Mummy farin ciki sosai har ta kira aminanta ta fada musu.....
Sai bayan Magriba akayi kamun amare,
"Mami da Anni su suka kama Husna,
sai Anty Reemah da sauran yan uwanta sukayi ma Nadeeyah,
Mummy ma in ka ganta zaka dauka albishir akayi mata da gidan aljanna saboda murna,
Rawa kam kawayen Amare da yan uwa suyi ta sosai har saida suka kure mawakin,
sai kusan goma makadin ya tattara kayanshi yayi gaba da tarin alkhairai masu yawa,
su kuwa kawayen suka koma dakin kwanansu suka cigaba da hirarsu ta yammata,
rabin hirar tasu ma akan Badar ta kare saboda sun so tana nan akayi bikin.....
Rana bata karya....
A ran 23 ga watan yuli..
ranar sati da safe dubban jama'a suka shaida daurin auren
*Musaddiq Mukhtar Kyari* da *Nadeeyah Adam*
da kuma auren
*Hafeez Adam* da *Husnah Mukhtar Kyari*...
Marokin gurin na gama sanarwa Jamal yayi dariya sosai yace
"vice versa,
gyara bakin madubi Hilal yayi yace
"ai fa, abin ya burgeni,
Allah ya basu zaman lafiya..
saura mu,
matsowa Jamal yayi yace
"ai ni nama gama samu,
saidai fatan dacewa,
jira kawai nakeyi komai ya lafa in aika sakon zuciyata,
bazan tsaya kallon ruwa kwado yayi min kafa ba....
"Kamar yadda Nayi Hilal ya fadi a cikin zuciyarshi..
amma a fili cewa yayi
"woww kace anjima akwai gist,
"Sosai ma In law...
au My son ya karashe yana dukan bakinshi..
Mikewa Hilal yayi yana kyakyata dariya yace
"ka tona kanka malam,
muje gurin walima kafin mutumin ya fara kumburi.....
Wannan kukan da kikeyi bazai taimakeki ba Amarya,
dama kinci abinci,
da kin samu sauki,
"Kinsan adadin matan da suka shigo gidannan ta haka kuwa?
to ki sani bake bace ta farko kuma bana tunanin zaki zamo ta karshe,
da yawa irin ku son duniyan iyayenku ke ja muku,
saboda son abun duniya sai idonsu ya rufe suyi kyautar da zata damesu nan gaba,
ta shi kici abincin,
kingani harda Farfesun Zomo,
ga tuwon lapshi miyar yauki gaskiya ke yar gata ce, dan abin bauta Garzar ki rage min, ta karashe tana turo langar tuwon gabanta,
Kafa Badariyya tasa ta ture langar tuwon,
nan naman ya zube a kasa,
komai ya bayyanar mata,
kan zomo ne da kayan cikinshi,
sai tsirarrun nama,
da sauri kande da ta durkusa tafara kwashe naman tana suďe hannu kamar mayya wacce tayi sabon kamu,
Idon da ya soye da bakin ciki Badariyya ta bita dashi tana hawayen zuci,
"wannan wace iriyar jarabawa ta fado,
kalmar na shiga uku har lokacin bata bar fita daga bakin Badar ba,
tana kallo kande ta sude gurin tass kamar an goge sannan ta russuna tace
"Ranki ya dade,
ko bakya jin yunwa bai kamata ki wulakanta abinci ba,
wannan naman yanzu da zan fita dashi tsakar gida sai an kusa kaini kasa saboda wawason shi,
ki daure kici ko kadan ne saboda kar yareemah yayi fada,
tsakii mai karfi Badariyya taja hade da sake yin tagumi tana tunanin way out..
Shigowar Yareemah ne yasanya kande fita da sauri bayan ta gaisheshi...
Zama yayi a gefen Badar hade da dauko langar farfesun...
"Sauka ki zauna a kasa ki cinyeshi tass domin ki samu karfin jikinki,
a fusace Badar ta mike tace "wannan kazantar ce zata sa in samu karfi a jikina,
wallahi kaji na rantse bazan zauna a gidannan ba,
kukan bakin ciki ta fasa mishi tace
"wallahi in na fita a gurin nan sunanku sorry, domin sai na gayyato muku sojoji sun tada wannan tsinannan kau----
"keeee...
ya katseta cike da tsawa,
nan take fuskarshi ta sauya yace "Zauna maza ki cinye abin dake cikin kwanukan nan,
"Bazan ci ba!
Nace bazan ci ba ka kashe n----
wani farin haske ne ya wuce ta makogoronta ya hanata Magana,
sai ma bin umarnin shi da ta fara yi...
tare suka zauna ya bata abincin a baki ta cinye tass cikin ficawar hayyaci,
tana gama shan ruwa ya umurceta da ta fitar da kwanukan waje,
ba musu ta kwashesu ta fitar dasu ta dawo dakin ta zauna a nutse,
mikewa yayi ya dawo inda take hade da kamo hannuwanta,
"ki kwantar da hankalinki, nima mutum ne kamar ki,
saidai mu Allah yayi mana baiwar sanin wasu abubuwa,
Tun kafin nayi auren farko lokacin ina yaro mahaifiyarki ta bani ke saboda jin dadi wani aiki da mahaifina yayi mata,
tun daga ranar muke kula da duk wani motsinta,
a ranar da aka haifeki mahaifina yayi murna domin a tunaninshi namiji zata haifa,
tun daga wannan lokacin muke bibiyar dukkan sawunki,