Sashe 40
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
wannan al'amarin zai fitar da rayuka da dama cikin tunanin da suka shekara da shekaru suna yinshi,
bude baki tayi da niyyar sake yin magana Baffa ya rigata da cewa "nasan kaima kana cikin zullumin da nake ciki, duk wanda ya ganmu ni da kai yasan jini daya ne
saboda kamanni,
wasu ka iya cewa yan biyu ne saidai yanayin tsufan da jikin shine kadai ya banbanta,
dan Allah ina son ka fada min wanene mahaifinka dan inason sanin ko inada wani sauran dan uwa wanda kaddara ta boye min shi,
ina son sanin inda mahaifinka yake dan inje mu gana,
in baya raye to dan Allah ka bani tarihin shi wanda zai iya warware min komai,
Papy baiyi magana ba ya fito da wayarshi,
dannata yayi hade da karata a kunnenshi,
"Hello Maimunah,
hadani da Anni a waya,
Papy na....,
Ruwaidah ta fadi murya a shake, "Mama na,
kuka kike yi?
Kukan ta sake fashewa dashi kamar zata tsaga wayar,
rage murya yayi yace "wanene, daina kukan and tell me,
M-a-mi ce ta fadi tana ajiyar zuciya,
tsaki yayi a hankali, yasan abin da aka mata bai taka kara ya karya ba,
"yi hakuri Mamanah,
jeki kai mata inji dalilin saki kuka,
da dan gudunta ta tashi taje kitchen inda Mami da mai aikinsu ke kwashe mangyadan da ta zubar,
a darare tace "Maami Papy ya kiraki,
kwafa tayi ta goge hannunta a jikin tsumma ta karbi wayar,
yana jin sallamarta yayi saurin amsawa,
ba tare da jin dalilin kukan Ruwaidah ba yace
"ina Anni?
tana bacci lafiya dai ko,
mami ta tambaya cike da zullumi,
ajiyar zuciya yayi yace "lafiya kalau Maimuna,
gobe da safe ku shirya guraren tara zan kira Badamasi yazo ya taho daku kaduna,
zama Mami tayi gabanta na tsananta faduwa tace "Dan Allah ka fada min abin da yake faruwa,
ina JAMAL da HAFEEZ?,
murmushi yayi cike da tsokana yace khairan in shaa Allah ruďaďďiya,
ke dai ku shirya kinji,
gyada kai tayi har lokacin gabanta bai daina faduwa ba...
Kallon Baffa yayi bayan ya ajiye wayar yace "Sanin abubuwan da ka tambayeni wannan sai maihaifiyata tazo,
domin nima ban san kaina ba, tashi nayi na ganni a hannun mahaifiyata ba tare da uba da yan uwa ba,
ni kadai na rayu a gabanta,
tare muka sha wahalhalun rayuwa,
na dai san a kullum tana fada min ina da uba, amma bata san inda yake ba,
A lokacin da Ma'u na tsaye to tabbas da ta kai kasa,
kokarin mikewa takeyi Papy yace "inna dawo ki zauna ayi komai a gabanki,
yau da za'a bincika zuciyata a gani to tabbas da an gano tafi takarda haske,
kallon shi Ma'u tayi tace "ďan nan ina ganin dai kamanni ne,
dan mu nan bamu da da namiji ko daya,
sannan duk wasu y'an uwa namu na kusa duk sun mutu,
kasan Allah yana iya halittar mutane masu kama da juna, akwai su da dama sab--- katseta Hafeez yayi cikin girmamawa yace "Goggo wannan ya wuce kamanni kawai,
akwai jini mai karfi,
ki duba girman makarantarmu duk daliban dake ciki ace dani kadai ya shaku har ya kaini gidanshi cikin iyalinshi,
sannan kuma idan kika ga Jamal da Ruwaidah a nan ne zaki tabbatar da su ďin jinin mu ne,
Daka mishi tsawa Goggo tayi "kai dalla rufe mana baki,
manya na magana kana yi saboda tsabar rashin kunya,
tashi ka fita kaba mutane guri,
mikewa Hafeez yayi yana fadin kiyi hakuri,
harara ta bishi dashi har ya bacewa ganinta sannan ta dawo da kallonta kan Papy tace
"to bawan Allah mun gode da ziyara, sai anjima,
sake gyara zama Papy yayi yace "Inna, bazan boye miki ba, barin gidannan a guri na sai da daddare,
sannan gobe da wuri zanzo domin kuwa ina hango cikar burina na sama da shekaru arbain da doriya zai tabbata,
cike da faduwar gaba ta kalli Baffa da ya kasa dauke idonshi a kan Papy,
yanayin maganarshi,
da komai irin nashi ne,
gayu, gogewa da yarinta ne kadai ya banbanta su,
taba shi Goggo tayi tace
"lokacin Sallah ya kusa tashi ka shiga kayi alwala,
da sauri Papy ya kalli agogon hannunshi yace "uku da kwata ne yanzu Inna lokaci baiyi ba,
tun Goggo na daurewa kar ta fara nuna mishi halinta,
har saida ya kaita bango ta dakawa Baffa tsawa tace "ya tashi su wuce daki,
wannan mutumin in ba aljani bane to maye ne,
jiki a sanyaye Baffa ya tashi yace ma Papy "yaya Sunanka,
da sauri papy yace "Abdallah" nan Baffa yayi ajiyar zuciya yace "ba SAIFU bane,
Ma'u ba saifu bane,
duk tunanina shine shiyasa na cika da tsoron ya za'ayi wanda ya mutu ya dawo,
nasan ni na binneshi da hannuna,
kallon Papy Goggo tayi tace "kaji ko,
dan Allah tashi ka fitar mana a gida,
kuma karka sake zuwa kaje can ka nemi ubanka..
Nan tsakar gida suka barshi zaune yana ta nazarin abubuwa,
kodai da gaske bashi bane mahaifinshi,
sai da yayi wasu yan mintuna sannan ya tashi hade da gamsar da zuciyarshi koma meye in Anni tazo zata warware mishi komai....
Ita kuwa Goggo safa da Marwah ta dinga yi a daki tana tunanin ta inda wannan mutumin ya fito,
tasan a hannunta saifu ya cika,
kuma a gabanta aka binne shi, anya ba aure Baffa yayi ba lokacin da yake tafiye tafiyenshi,
katse mata tunani yayi yace "Ma'u wannan yaron ko dai dan Hardejo ne,
kodai..... saurin katse shi tayi murya a kausashe tace "ko kuma naka ba,
ni zaka ciwa Amana Muhammadu,?
ashe dama kayi aure a boye ban sani ba,
"Nan jikin Baffa ya fara rawa yace "wallahi banda Atika ban taba auren wata mace ba, daga ke sai ita,
kwafa Goggo tayi cike da masifa tace "gaskiya zatayi halinta ai gobe,
da bana son yaron nan ya dawo gidannan amma gobe da kaina zansa Hafeez ya kawo shi dan a warware min wannan kullin,
ina ganin watan jin kunyarka ne ya tsaya,
saboda sanin yana da gaskiya shiyasa yace "Allah ya kaimu,
komawa yayi ya zaune a zuciyarshi yace "shi yaushe ma ya kalli wata mace a matsayin mace har ya aureta,
har yanzu gani yakeyi duk duniya babu macen da ta kamo kafar ma'u a komai,
sauran mata duk kallonsu yakeyi kamar gumaka,
tsaki yayi yace "Ma'u batayi mishi adalci ba,
tasan bazai taba cin amanarta ba,
amma babu komai gobe gaskiya zatayi halinta...
Haka suka kwana dukkansu zuciyoyinsu ba dadi,
kowa da abun da yake sakawa a ranshi,
har gari ya waye Baffa bai bar hango fuskar Abdallah ba.....
**********●●●*******
Karfe biyu da rabi suka iso kaduna,
Hotel din da su Papy suka sauka can Badamasi ya wuce dasu,
bayan sun huta a masauki suka ci abinci sannan ne Mami ta tambayi Papy dalilin zuwan nasu,
bai amsa ta ba saboda yaga Anni ta dan kashingide tana son tayi bacci,
Ruwaidah ya daura akan cinyarshi yace "me Mamana tayi miki jiya kika duketa,
irin kukan nan da tayi nasan ba karamin duka kikayi mata ba,
Harararta Mami tayi tace "ai badan Anni ba walhi da sai na balla hannunta sai ayi dauri,
kaga daga nan ma huta da barna,
turo baki Ruwaidah tayi hade da tura kanta cikin kirjin Papy,
"ni kike turowa baki,?
mami ta tambaya tana nuna kirjinta da yatsa,
a ina ta turo miki baki,
ki kyalemin uwata ta huta,
shikenan dan bana nan bazatayi abin da takeso ba,
Mikewa Mami tayi tace "ko kai da kana nan sai ka tayani,
man gyada na zaune cikin jarkarshi ta dauko tukunyarta ta wasan yara wai zata soya dankali,
tasan jarkar tafi karfinta haka tasa karfi ta yar da ita kasa,
gaba daya kitchen da store babu inda bai samu albarkar mai ba,
"tabbb...
ai Mami kin ma mata da sauki, da kin cire hannun ne sai a sa mata na roba..
harara Papy ya jefa gefen da Jamal ke zaune yana latsa waya kamar bashi yayi maganan ba,
"shikenan dan ta zubar da mai sai a duke ta,
ba koyon girki takeyi ba,
in bata koya ba waye zai dinga tayaki aiki,
"Na yafe Mami tayi saurin fadi tayi hanyar bayi tace "ka cigaba da shagwaba yarinyar nan,
ta riga ta maida mu kamar kakanninta,
bayan Ruwaidah Papy ya shafa yace "rabu da Mami kinji,
zan siyo miki kayan abincinki ki koya da kanki ki dinga dafa min inci kinji ko?
Gyada kai tayi tace "kuma bazamu samma Yaya Jamal ba,
dariya papy yayi yace
"eh mana wama zai bashi,
yaje can yaci jagwalgwalon Mamin shi,
dariya sosai Jamal yayi yace "opposite,
Kuma in na kara ganin kin taba ma Mami ko da gishiri ne sai na yanka hannun da wuka,
murguda mishi baki tayi tace "ni da Papy zai siyomin nawa me zanyi da naku,
ko kitchen din mami ma bazan kara shiga ba,
"yauwa Good Girl,
muna komawa zan yi miki cefanenki,
karki kalli kayan Mami sun tsufa,
mikewa Jamal yayi yana dariya yace "har abincin Mami ma kar ta kara ci papy,
ta dafa nata da kanta,
dakuwa Papy yayi mishi ya fita daga dakin yana dariya....
Suna idar da Sallar la'asar Papy yace su shirya zasu je wani guri,
manufar shi nakin fadawa Anni shine kar ya fada mata suje bashi bane hankalinta ya kara tashi,
gara in suka je yaga bata sanshi ba sai su tafi ba tare da ya daga mata hankali ba,
tun yana shekara bakwai ya yankewa kanshi daina matsa mata akan maganar mahaifinshi,
domin ya kan ganta cikin tsananin damuwa duk ranar da yayi mata maganar,
a irin yadda ya taso yaga ta wahala akanshi shi yasa baya san ganinta cikin damuwa ko kadan...
Biyar saura suka isa kofar gidan,
motar Mummy Hafeez ya gani a cikin gidan,
Addu'a ya fara yi zuciyarshi na Allah yasa kar su hadu su wulakanta bayin Allahn nan,
gabanshi bai tsananta faduwa ba saida ya jiyo muryar Radiya,
farin sani yayi mata akan rashin mutunci,
dake wa yayi ya karasa ciki dasu,
Sallama sukayi dukkansu suka shiga cikin gidan,
daga cikin daki sukaji an amsa Sallamar,
mikewa Goggo tayi ta fito dama zaman jiransu take,
bude baki tayi da niyyar sake yin magana Baffa ya rigata da cewa "nasan kaima kana cikin zullumin da nake ciki, duk wanda ya ganmu ni da kai yasan jini daya ne
saboda kamanni,
wasu ka iya cewa yan biyu ne saidai yanayin tsufan da jikin shine kadai ya banbanta,
dan Allah ina son ka fada min wanene mahaifinka dan inason sanin ko inada wani sauran dan uwa wanda kaddara ta boye min shi,
ina son sanin inda mahaifinka yake dan inje mu gana,
in baya raye to dan Allah ka bani tarihin shi wanda zai iya warware min komai,
Papy baiyi magana ba ya fito da wayarshi,
dannata yayi hade da karata a kunnenshi,
"Hello Maimunah,
hadani da Anni a waya,
Papy na....,
Ruwaidah ta fadi murya a shake, "Mama na,
kuka kike yi?
Kukan ta sake fashewa dashi kamar zata tsaga wayar,
rage murya yayi yace "wanene, daina kukan and tell me,
M-a-mi ce ta fadi tana ajiyar zuciya,
tsaki yayi a hankali, yasan abin da aka mata bai taka kara ya karya ba,
"yi hakuri Mamanah,
jeki kai mata inji dalilin saki kuka,
da dan gudunta ta tashi taje kitchen inda Mami da mai aikinsu ke kwashe mangyadan da ta zubar,
a darare tace "Maami Papy ya kiraki,
kwafa tayi ta goge hannunta a jikin tsumma ta karbi wayar,
yana jin sallamarta yayi saurin amsawa,
ba tare da jin dalilin kukan Ruwaidah ba yace
"ina Anni?
tana bacci lafiya dai ko,
mami ta tambaya cike da zullumi,
ajiyar zuciya yayi yace "lafiya kalau Maimuna,
gobe da safe ku shirya guraren tara zan kira Badamasi yazo ya taho daku kaduna,
zama Mami tayi gabanta na tsananta faduwa tace "Dan Allah ka fada min abin da yake faruwa,
ina JAMAL da HAFEEZ?,
murmushi yayi cike da tsokana yace khairan in shaa Allah ruďaďďiya,
ke dai ku shirya kinji,
gyada kai tayi har lokacin gabanta bai daina faduwa ba...
Kallon Baffa yayi bayan ya ajiye wayar yace "Sanin abubuwan da ka tambayeni wannan sai maihaifiyata tazo,
domin nima ban san kaina ba, tashi nayi na ganni a hannun mahaifiyata ba tare da uba da yan uwa ba,
ni kadai na rayu a gabanta,
tare muka sha wahalhalun rayuwa,
na dai san a kullum tana fada min ina da uba, amma bata san inda yake ba,
A lokacin da Ma'u na tsaye to tabbas da ta kai kasa,
kokarin mikewa takeyi Papy yace "inna dawo ki zauna ayi komai a gabanki,
yau da za'a bincika zuciyata a gani to tabbas da an gano tafi takarda haske,
kallon shi Ma'u tayi tace "ďan nan ina ganin dai kamanni ne,
dan mu nan bamu da da namiji ko daya,
sannan duk wasu y'an uwa namu na kusa duk sun mutu,
kasan Allah yana iya halittar mutane masu kama da juna, akwai su da dama sab--- katseta Hafeez yayi cikin girmamawa yace "Goggo wannan ya wuce kamanni kawai,
akwai jini mai karfi,
ki duba girman makarantarmu duk daliban dake ciki ace dani kadai ya shaku har ya kaini gidanshi cikin iyalinshi,
sannan kuma idan kika ga Jamal da Ruwaidah a nan ne zaki tabbatar da su ďin jinin mu ne,
Daka mishi tsawa Goggo tayi "kai dalla rufe mana baki,
manya na magana kana yi saboda tsabar rashin kunya,
tashi ka fita kaba mutane guri,
mikewa Hafeez yayi yana fadin kiyi hakuri,
harara ta bishi dashi har ya bacewa ganinta sannan ta dawo da kallonta kan Papy tace
"to bawan Allah mun gode da ziyara, sai anjima,
sake gyara zama Papy yayi yace "Inna, bazan boye miki ba, barin gidannan a guri na sai da daddare,
sannan gobe da wuri zanzo domin kuwa ina hango cikar burina na sama da shekaru arbain da doriya zai tabbata,
cike da faduwar gaba ta kalli Baffa da ya kasa dauke idonshi a kan Papy,
yanayin maganarshi,
da komai irin nashi ne,
gayu, gogewa da yarinta ne kadai ya banbanta su,
taba shi Goggo tayi tace
"lokacin Sallah ya kusa tashi ka shiga kayi alwala,
da sauri Papy ya kalli agogon hannunshi yace "uku da kwata ne yanzu Inna lokaci baiyi ba,
tun Goggo na daurewa kar ta fara nuna mishi halinta,
har saida ya kaita bango ta dakawa Baffa tsawa tace "ya tashi su wuce daki,
wannan mutumin in ba aljani bane to maye ne,
jiki a sanyaye Baffa ya tashi yace ma Papy "yaya Sunanka,
da sauri papy yace "Abdallah" nan Baffa yayi ajiyar zuciya yace "ba SAIFU bane,
Ma'u ba saifu bane,
duk tunanina shine shiyasa na cika da tsoron ya za'ayi wanda ya mutu ya dawo,
nasan ni na binneshi da hannuna,
kallon Papy Goggo tayi tace "kaji ko,
dan Allah tashi ka fitar mana a gida,
kuma karka sake zuwa kaje can ka nemi ubanka..
Nan tsakar gida suka barshi zaune yana ta nazarin abubuwa,
kodai da gaske bashi bane mahaifinshi,
sai da yayi wasu yan mintuna sannan ya tashi hade da gamsar da zuciyarshi koma meye in Anni tazo zata warware mishi komai....
Ita kuwa Goggo safa da Marwah ta dinga yi a daki tana tunanin ta inda wannan mutumin ya fito,
tasan a hannunta saifu ya cika,
kuma a gabanta aka binne shi, anya ba aure Baffa yayi ba lokacin da yake tafiye tafiyenshi,
katse mata tunani yayi yace "Ma'u wannan yaron ko dai dan Hardejo ne,
kodai..... saurin katse shi tayi murya a kausashe tace "ko kuma naka ba,
ni zaka ciwa Amana Muhammadu,?
ashe dama kayi aure a boye ban sani ba,
"Nan jikin Baffa ya fara rawa yace "wallahi banda Atika ban taba auren wata mace ba, daga ke sai ita,
kwafa Goggo tayi cike da masifa tace "gaskiya zatayi halinta ai gobe,
da bana son yaron nan ya dawo gidannan amma gobe da kaina zansa Hafeez ya kawo shi dan a warware min wannan kullin,
ina ganin watan jin kunyarka ne ya tsaya,
saboda sanin yana da gaskiya shiyasa yace "Allah ya kaimu,
komawa yayi ya zaune a zuciyarshi yace "shi yaushe ma ya kalli wata mace a matsayin mace har ya aureta,
har yanzu gani yakeyi duk duniya babu macen da ta kamo kafar ma'u a komai,
sauran mata duk kallonsu yakeyi kamar gumaka,
tsaki yayi yace "Ma'u batayi mishi adalci ba,
tasan bazai taba cin amanarta ba,
amma babu komai gobe gaskiya zatayi halinta...
Haka suka kwana dukkansu zuciyoyinsu ba dadi,
kowa da abun da yake sakawa a ranshi,
har gari ya waye Baffa bai bar hango fuskar Abdallah ba.....
**********●●●*******
Karfe biyu da rabi suka iso kaduna,
Hotel din da su Papy suka sauka can Badamasi ya wuce dasu,
bayan sun huta a masauki suka ci abinci sannan ne Mami ta tambayi Papy dalilin zuwan nasu,
bai amsa ta ba saboda yaga Anni ta dan kashingide tana son tayi bacci,
Ruwaidah ya daura akan cinyarshi yace "me Mamana tayi miki jiya kika duketa,
irin kukan nan da tayi nasan ba karamin duka kikayi mata ba,
Harararta Mami tayi tace "ai badan Anni ba walhi da sai na balla hannunta sai ayi dauri,
kaga daga nan ma huta da barna,
turo baki Ruwaidah tayi hade da tura kanta cikin kirjin Papy,
"ni kike turowa baki,?
mami ta tambaya tana nuna kirjinta da yatsa,
a ina ta turo miki baki,
ki kyalemin uwata ta huta,
shikenan dan bana nan bazatayi abin da takeso ba,
Mikewa Mami tayi tace "ko kai da kana nan sai ka tayani,
man gyada na zaune cikin jarkarshi ta dauko tukunyarta ta wasan yara wai zata soya dankali,
tasan jarkar tafi karfinta haka tasa karfi ta yar da ita kasa,
gaba daya kitchen da store babu inda bai samu albarkar mai ba,
"tabbb...
ai Mami kin ma mata da sauki, da kin cire hannun ne sai a sa mata na roba..
harara Papy ya jefa gefen da Jamal ke zaune yana latsa waya kamar bashi yayi maganan ba,
"shikenan dan ta zubar da mai sai a duke ta,
ba koyon girki takeyi ba,
in bata koya ba waye zai dinga tayaki aiki,
"Na yafe Mami tayi saurin fadi tayi hanyar bayi tace "ka cigaba da shagwaba yarinyar nan,
ta riga ta maida mu kamar kakanninta,
bayan Ruwaidah Papy ya shafa yace "rabu da Mami kinji,
zan siyo miki kayan abincinki ki koya da kanki ki dinga dafa min inci kinji ko?
Gyada kai tayi tace "kuma bazamu samma Yaya Jamal ba,
dariya papy yayi yace
"eh mana wama zai bashi,
yaje can yaci jagwalgwalon Mamin shi,
dariya sosai Jamal yayi yace "opposite,
Kuma in na kara ganin kin taba ma Mami ko da gishiri ne sai na yanka hannun da wuka,
murguda mishi baki tayi tace "ni da Papy zai siyomin nawa me zanyi da naku,
ko kitchen din mami ma bazan kara shiga ba,
"yauwa Good Girl,
muna komawa zan yi miki cefanenki,
karki kalli kayan Mami sun tsufa,
mikewa Jamal yayi yana dariya yace "har abincin Mami ma kar ta kara ci papy,
ta dafa nata da kanta,
dakuwa Papy yayi mishi ya fita daga dakin yana dariya....
Suna idar da Sallar la'asar Papy yace su shirya zasu je wani guri,
manufar shi nakin fadawa Anni shine kar ya fada mata suje bashi bane hankalinta ya kara tashi,
gara in suka je yaga bata sanshi ba sai su tafi ba tare da ya daga mata hankali ba,
tun yana shekara bakwai ya yankewa kanshi daina matsa mata akan maganar mahaifinshi,
domin ya kan ganta cikin tsananin damuwa duk ranar da yayi mata maganar,
a irin yadda ya taso yaga ta wahala akanshi shi yasa baya san ganinta cikin damuwa ko kadan...
Biyar saura suka isa kofar gidan,
motar Mummy Hafeez ya gani a cikin gidan,
Addu'a ya fara yi zuciyarshi na Allah yasa kar su hadu su wulakanta bayin Allahn nan,
gabanshi bai tsananta faduwa ba saida ya jiyo muryar Radiya,
farin sani yayi mata akan rashin mutunci,
dake wa yayi ya karasa ciki dasu,
Sallama sukayi dukkansu suka shiga cikin gidan,
daga cikin daki sukaji an amsa Sallamar,
mikewa Goggo tayi ta fito dama zaman jiransu take,