Sashe 57
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
kureshi da ido tayi alamar tuhuma,
ga mamakinta murmushi yayi kamar yaro karami,
haibarshi ta lokacin samartaka ta tariyo kanta,
shi ma ita din yake kallo amma fa a tsorace yake dan yana tsoron abun da zai canza ra'ayinshi akan auren nan,
dan kwanakin da ya jera yana haduwa da Anni yaji tayi matukar kwanta mishi a rai,
yana fatan suyi zaman tare har mai rabawa ta raba,
"Biki akeyi na ganka da sababbin kaya?
yadda ta jefo tambayar sai ta bawa mai kallonta tausayi,
"Gyada kai yayi yace "eh bikin Muhammadu da Hanne,
agogon bango ya kalla yace
"goma daidai za'a daura,
yanzu tara da rabi,
bari muyi saurin zuwa gurin, akwai kayan abinci a cikin drawer can kiyi kokari kici kafin mu dawo, sai ki fada min inda kika je kuma da izinin wa,
*IZINI*
Goggo ta maimaita kamar me koyon magana,
yana gab da fita tayi karfi da jikinta ta damki babbar rigarshi hade da fadin
"wallahi babu inda zaka,
kai baka isa ka wulakanta ni ba Muhammadu,
ko kunya bakaji,
banda jika har tattaba kunni gareka amma dan budurwar zuciya irin taka harda yin anko kai a dole zaka angance,
to wallhi saidai in ka kasheni ka ka fita,
saboda rashin kuzarin da take ciki yasa shi kwace rigar yace
"Raya sunnar ne abin kunya, bazan kasheki ba,
kuma aure babu fashi mutuwa ka raba,
yana kaiwa nan yasa kai ya fice,
"aiko zaku mutu,
wallahi tallahi kaji rantsuwar da bata da kaff------
ido cikin idon da sukayi da Daddy ne ya hanata karasa mummunan furucinta,
ciki ta juya hawayen ido suka kafe sai na zuci da suka dinga kara kaini,
kasa zaune tayi tanata safa da marwa tana tunanin ta inda ta kuskuro har wadannan abubuwan suka cakude mata haka,
ga kayan dakinta duk an fitar dasu bare ta samo wasu cikin surkullenta tayi amfani dashi,
dakyar ta zauna tana maida numfashi kamar zata mutu......
Foiling naman walima Nadeeyah da Husnah sukeyi a cikin tray suna hira,
Mummy na bayansu tana hada coleslaw na dole dan ba yadda zatayi Daddy ya dauki nauyin walimar a gidanshi,
suna gamawa suka jere komai a inda ya dace,
rissinawa Nadeeyah tayi tace "Mummy akwai wani abun ne?
gyada tayi kawai alamar a'a kamar me ciwon baki,
Daki suka wuce dan yin wanka,
kaya kala daya Papy ya dinka musu harda su Anty Raly,
lace ne dark purple mai ratsin manyan pattern pink flower,
dinkin riga da skirt mai matukar kyau,
ko ina an sanya farin stones wanda ya kara kayata lace din,
*Bismid cream* Husna ta dauko tana shafawa tana dariya,
wayaga Baffa ango,
wallahi ni abun kunya ma yake bani,
su Daddy kuma harda wani daurewa karya ...... wai harda walima,
dariya Nadeeyah tayi hade da jan zip din rigarta tace
"ni kaina abun jinshi nake wani iri,
saidai ba yadda za'ayi da hukuncin Allah,
Badar sarkin nukufurci tana kwance cikin bargo tana latsa waya bata ma san suna shiri ba,
light make up sukayi wanda ya dace da fatarsu,
sunyi kyau sosai saboda lace din kalar farare ne,
dauri sukayi mai matukar kyau iri daya suka feshe jikinsu da turaruka masu kamshi da saukin karfi,
kara wayar Nadeeyah tayi alamar shigowar sako,
da sauri ta dauka dan tasan wanda yayi text din,
"baya kiranta a waya, amma text duk minti biyar yinsa yakeyi,
ko ya rasa abin cewa sai ya nemo write up na yaudarar maza, ko yadda zata kula da kanta, ko adduoi ya tura mata,
reply dinta koda kalma daya ce means the world to him,
*Yunwaaaaaaaa, plss ku kawo min abinci kar in mutu*.....
Dariya sosai tayi dan ganin mai sakon, ta mikawa Husna wayar,
itama dariyar tayi tace acici,
kinsan yau ya tashi da wuri to fa kowa ya bani a gidannan,
flat shoe suka saka suka wuce kitchen,
flask Nadeeyah ta dauka da hot chocolate da ta san yafi san karyawa dashi,
ita kuma Husnah ta dibi naman kaza cikin pepper din da sukayi foiling,
wani sakon ne ya sake shigowa..
*Nadeeyah so kikeyi in mutu ko, ba komai... ya sanyo alamar kuka*
Reply tayi mishi tana murmushi tace
*Sorry, kana ina ne*
Yana ganin reply din yayi saurin kiranta
"ina BQ, yanzu muka dawo,
plss kiyi sauri cikina na ta kiran sunanki,
yasan ke kadai zaki taimaka,
kashe wayar tayi tana dariya suka wuce BQ din,
Murda kofar Husna tayi saboda ita ke da rangwamen kaya a hannu,
karo tayi da mutum shima ya sako kai zai fito,
subhanallah ta fadi hade ja baya tana kallon tray din da ya fadi kasa,
kallon shi tayi taga shaddarshi ta baci da source
"Ya salam.. Ya Hafeez dan Allah kayi hakuri,
wallhy bansan zaka fito ba,
Murmushi yayi yace "haba karki damu,
da kinsani bazaki shigo ba nasani,
ke da gaisuwa ma sai na roka, yaushe zakiso kiyi karo dani,
dariya tayi sosai tace
"kiji sharri Nadeeyah,
bari in duba maka kayan Ya Musaddiq ka canza,
"inyi yawo dai a ciki ya fadi yana goge jikinshi hade da kallon Musaddiq da yayi fuskar tausayi,
dariya yayi ya kalli Nadeeyah yace
"saura kiris a zare ran fa,
maza kije ki bashi break fast..
Da sauri ta zare takalmin kafarta ta shiga da sallama tana fadin "sorry pls,
rike cikin yayi ya kara bata fuska yace
"naki sorryn na koshi,
bude flask din tayi ta zuba ruwan zafi ta hada mishi tace
"gashi kayi hakuri dan Allah kar a zare ran,
in aka zare bamu san inda zamu sa kanmu ba,
"Dadi zakuji mana ku huta da acici,
sosai sukayi dariya Nadeeyah ta gimtse tata dariyar tace
"ai ci dole ne yayana,
kowa ma acici ne,
gashi kaji, plssssss, ta fadi tana karkace kai gefe,
"badan ni zansha ba sai dan tausayin hanjin cikina,
Saboda dariya saida Nadeeyah ta durkushe a gurin,
"dan Allah karka kashe ni,
bari in kawo maka wani abinci me nauyi,
kallon Husnah yayi dake kara jaddaddawa Hafeez suje ta bashi kayan shi ya saka,
"in kinje ki bashi riga kadai ta isheshi,
kinga sai kuji dadin zagin halitta ta,
ya karashe yana kai kofin bakinshi,
dariyar ma kin fitowa Husnah tayi suka fita tare da Nadeeyah,
Dariya Hafeez yayi yace
"manta da ita kaji,
gida zan koma in canza kaya,
bari in kira Jamal ya kawo min mota,
ciro key Musaddiq yayi yace "ga tawa kaje ka dawo kafin a fara walimar,
karbar keyn yayi yace "ka dai ajiye min nawa abincin kar ka cinye kai kadai,
"Haaahaha...
zan daina cin abinci kwata kwata a idon mutane,
gara in rage wannan kibar,
da zan iya ma harda tsawo zan rage,
"dariyar Shirmen Musaddiq Hafeez yayi ya fita yana jin dadin yadda al'amura suke kasancewa kamar yadda Mamma take so,
Allah sarki Mamma,
ina ma ana mutuwa a dawo kiga yadda wuya take neman rikide mana ta zamto dadi,
kiga yadda dan uwan da baki sani ba yake gatata mu kamar shi ya tsuguna ya haifemu,
Allah yayi miki Rahama ya fadi ya shiga motar zuciyarshi a dagule saboda tuno iyayenshi da yayi.......
Ana idar da sallar isha'i su Nadeeyah suka fara shirin barin gurin su Anni,
hankalin Nadeeyah a kwance ta gama shiri dan tasan yanzu su Anty Radiya sun bar gidan,
"kallon banza da habaicin talauci hade da rashin asali da suke mata yana sosa ranta matuka,
kalmar da Anty Raudah ta fadi na "anyi clean fata ta murje da abinci akan kari sai kace wata yar shugaban kasa,
a dai dinga tuno asali dan kar garin iyawa a wuce gona da iri!!
Wadannan kalamai sun matukar tsaya mata,
dan ma Musaddiq dake bayanta wanda dan shi Anty Raudah tayi mata habaicin yace
"Haba Anty, sai kace sa'arki,
dani take magana bada ke ba,
ku ke jawa kanku raini wallahi, yayi tsaki a hankali hade da cewa Nadeeyah ta kira Husnah su tafi...
Hannu ya kyasta mata a kusa da idonta,
a firgice ta dawo daga tunanin abubuwan da suka gifta dazu a gidan,
rage Murya yayi yace
"Tunanin su Anty ko?
Abin da ya kamata ki saba dashi ne tunda saidai in basu zo gidan ba,
in kika kula mutum a kullum burin shi ya bata miki rai to sai kiyi fatali da duk abin da yace, domin shi kadai zaiyi dakon bacin ransa,
"Zuciya is very special my sister,
fill it with love,
karki bari bacin rai ya samu kofar shiga cikinta, dan bacin rai na destroying duk abin da aka tanadarwa zuciya, dan haka bana san ganin tunani ko bacin rai nan a tare dake,
kinji ko?
gyada kai tayi hade da murmushinta mai kyau,
"Thats my lovely sis,
oya kira mana Husnah mu tafi,
kafin ta kai ga amsawa suka hango Husnah sun fito tare da Hafeez da Ruwaidah a tsakiya,
gefe kuma Jamal ne sanye da kayan bacci shima yana dosar inda suke,
"Badai bacci zakayi ba,
Musaddiq ya tambayeshi yana mishi kallon mamaki,
jingina jikin motar yayi yace
"in banyi bacci ba ai sai in kasa moruwa,
yau ko tamola bata kaini garuwa ba,
wahalar da Baffa ya bani yau ba kadan bace,
"duk wani abokinshi da yazo gurin daurin aure wanda baida mota saida na maidashi gida,
just imagine kaine,
hmmm thank Goodness akwai ruwan zafi,
da yau sai na tashi aiki, ya karashe yana danna bayanshi,
"Lazy youth!!
Ruwaidah ta fadi tana boyewa a bayan Hafeez,
dariya ta basu dukkansu Nadeeyah tace
"duk kokarin nan da yayi ki kirashi lazy,
murya cakwai tace
"Allah Adda he is very lazy and he can exaggerate,
yanzu haka gida uku yaje,
haka Mami ke fama dashi baya san a moreshi,
Rai a bace Jamal yayi inda take yana fadin
"ni sa'anki,
wani irin ihu ta saki hade da rugawa ciki,
bayanta yabi da gudu dan yaci alwashin ko a gaban Papy ne sai ya gurji bakinta,
Dariya Hafeez yayi yace ku shiga mota ku tafi dare nayi,
indai su Jamal ne kullum sai sunyi sau ba adadi,
ya kasa gane dadin tsokanarshi takeyi,
saboda bata da abokin wasa shiyasa ta maidashi abokin wasanta, shi kuma san girma yasa baya wasa da ita,
" haushin hakan yasa ta rainashi sosai,
motar suka bude suka shiga suna dariyar Ruwaidah da Jamal,
ga mamakinta murmushi yayi kamar yaro karami,
haibarshi ta lokacin samartaka ta tariyo kanta,
shi ma ita din yake kallo amma fa a tsorace yake dan yana tsoron abun da zai canza ra'ayinshi akan auren nan,
dan kwanakin da ya jera yana haduwa da Anni yaji tayi matukar kwanta mishi a rai,
yana fatan suyi zaman tare har mai rabawa ta raba,
"Biki akeyi na ganka da sababbin kaya?
yadda ta jefo tambayar sai ta bawa mai kallonta tausayi,
"Gyada kai yayi yace "eh bikin Muhammadu da Hanne,
agogon bango ya kalla yace
"goma daidai za'a daura,
yanzu tara da rabi,
bari muyi saurin zuwa gurin, akwai kayan abinci a cikin drawer can kiyi kokari kici kafin mu dawo, sai ki fada min inda kika je kuma da izinin wa,
*IZINI*
Goggo ta maimaita kamar me koyon magana,
yana gab da fita tayi karfi da jikinta ta damki babbar rigarshi hade da fadin
"wallahi babu inda zaka,
kai baka isa ka wulakanta ni ba Muhammadu,
ko kunya bakaji,
banda jika har tattaba kunni gareka amma dan budurwar zuciya irin taka harda yin anko kai a dole zaka angance,
to wallhi saidai in ka kasheni ka ka fita,
saboda rashin kuzarin da take ciki yasa shi kwace rigar yace
"Raya sunnar ne abin kunya, bazan kasheki ba,
kuma aure babu fashi mutuwa ka raba,
yana kaiwa nan yasa kai ya fice,
"aiko zaku mutu,
wallahi tallahi kaji rantsuwar da bata da kaff------
ido cikin idon da sukayi da Daddy ne ya hanata karasa mummunan furucinta,
ciki ta juya hawayen ido suka kafe sai na zuci da suka dinga kara kaini,
kasa zaune tayi tanata safa da marwa tana tunanin ta inda ta kuskuro har wadannan abubuwan suka cakude mata haka,
ga kayan dakinta duk an fitar dasu bare ta samo wasu cikin surkullenta tayi amfani dashi,
dakyar ta zauna tana maida numfashi kamar zata mutu......
Foiling naman walima Nadeeyah da Husnah sukeyi a cikin tray suna hira,
Mummy na bayansu tana hada coleslaw na dole dan ba yadda zatayi Daddy ya dauki nauyin walimar a gidanshi,
suna gamawa suka jere komai a inda ya dace,
rissinawa Nadeeyah tayi tace "Mummy akwai wani abun ne?
gyada tayi kawai alamar a'a kamar me ciwon baki,
Daki suka wuce dan yin wanka,
kaya kala daya Papy ya dinka musu harda su Anty Raly,
lace ne dark purple mai ratsin manyan pattern pink flower,
dinkin riga da skirt mai matukar kyau,
ko ina an sanya farin stones wanda ya kara kayata lace din,
*Bismid cream* Husna ta dauko tana shafawa tana dariya,
wayaga Baffa ango,
wallahi ni abun kunya ma yake bani,
su Daddy kuma harda wani daurewa karya ...... wai harda walima,
dariya Nadeeyah tayi hade da jan zip din rigarta tace
"ni kaina abun jinshi nake wani iri,
saidai ba yadda za'ayi da hukuncin Allah,
Badar sarkin nukufurci tana kwance cikin bargo tana latsa waya bata ma san suna shiri ba,
light make up sukayi wanda ya dace da fatarsu,
sunyi kyau sosai saboda lace din kalar farare ne,
dauri sukayi mai matukar kyau iri daya suka feshe jikinsu da turaruka masu kamshi da saukin karfi,
kara wayar Nadeeyah tayi alamar shigowar sako,
da sauri ta dauka dan tasan wanda yayi text din,
"baya kiranta a waya, amma text duk minti biyar yinsa yakeyi,
ko ya rasa abin cewa sai ya nemo write up na yaudarar maza, ko yadda zata kula da kanta, ko adduoi ya tura mata,
reply dinta koda kalma daya ce means the world to him,
*Yunwaaaaaaaa, plss ku kawo min abinci kar in mutu*.....
Dariya sosai tayi dan ganin mai sakon, ta mikawa Husna wayar,
itama dariyar tayi tace acici,
kinsan yau ya tashi da wuri to fa kowa ya bani a gidannan,
flat shoe suka saka suka wuce kitchen,
flask Nadeeyah ta dauka da hot chocolate da ta san yafi san karyawa dashi,
ita kuma Husnah ta dibi naman kaza cikin pepper din da sukayi foiling,
wani sakon ne ya sake shigowa..
*Nadeeyah so kikeyi in mutu ko, ba komai... ya sanyo alamar kuka*
Reply tayi mishi tana murmushi tace
*Sorry, kana ina ne*
Yana ganin reply din yayi saurin kiranta
"ina BQ, yanzu muka dawo,
plss kiyi sauri cikina na ta kiran sunanki,
yasan ke kadai zaki taimaka,
kashe wayar tayi tana dariya suka wuce BQ din,
Murda kofar Husna tayi saboda ita ke da rangwamen kaya a hannu,
karo tayi da mutum shima ya sako kai zai fito,
subhanallah ta fadi hade ja baya tana kallon tray din da ya fadi kasa,
kallon shi tayi taga shaddarshi ta baci da source
"Ya salam.. Ya Hafeez dan Allah kayi hakuri,
wallhy bansan zaka fito ba,
Murmushi yayi yace "haba karki damu,
da kinsani bazaki shigo ba nasani,
ke da gaisuwa ma sai na roka, yaushe zakiso kiyi karo dani,
dariya tayi sosai tace
"kiji sharri Nadeeyah,
bari in duba maka kayan Ya Musaddiq ka canza,
"inyi yawo dai a ciki ya fadi yana goge jikinshi hade da kallon Musaddiq da yayi fuskar tausayi,
dariya yayi ya kalli Nadeeyah yace
"saura kiris a zare ran fa,
maza kije ki bashi break fast..
Da sauri ta zare takalmin kafarta ta shiga da sallama tana fadin "sorry pls,
rike cikin yayi ya kara bata fuska yace
"naki sorryn na koshi,
bude flask din tayi ta zuba ruwan zafi ta hada mishi tace
"gashi kayi hakuri dan Allah kar a zare ran,
in aka zare bamu san inda zamu sa kanmu ba,
"Dadi zakuji mana ku huta da acici,
sosai sukayi dariya Nadeeyah ta gimtse tata dariyar tace
"ai ci dole ne yayana,
kowa ma acici ne,
gashi kaji, plssssss, ta fadi tana karkace kai gefe,
"badan ni zansha ba sai dan tausayin hanjin cikina,
Saboda dariya saida Nadeeyah ta durkushe a gurin,
"dan Allah karka kashe ni,
bari in kawo maka wani abinci me nauyi,
kallon Husnah yayi dake kara jaddaddawa Hafeez suje ta bashi kayan shi ya saka,
"in kinje ki bashi riga kadai ta isheshi,
kinga sai kuji dadin zagin halitta ta,
ya karashe yana kai kofin bakinshi,
dariyar ma kin fitowa Husnah tayi suka fita tare da Nadeeyah,
Dariya Hafeez yayi yace
"manta da ita kaji,
gida zan koma in canza kaya,
bari in kira Jamal ya kawo min mota,
ciro key Musaddiq yayi yace "ga tawa kaje ka dawo kafin a fara walimar,
karbar keyn yayi yace "ka dai ajiye min nawa abincin kar ka cinye kai kadai,
"Haaahaha...
zan daina cin abinci kwata kwata a idon mutane,
gara in rage wannan kibar,
da zan iya ma harda tsawo zan rage,
"dariyar Shirmen Musaddiq Hafeez yayi ya fita yana jin dadin yadda al'amura suke kasancewa kamar yadda Mamma take so,
Allah sarki Mamma,
ina ma ana mutuwa a dawo kiga yadda wuya take neman rikide mana ta zamto dadi,
kiga yadda dan uwan da baki sani ba yake gatata mu kamar shi ya tsuguna ya haifemu,
Allah yayi miki Rahama ya fadi ya shiga motar zuciyarshi a dagule saboda tuno iyayenshi da yayi.......
Ana idar da sallar isha'i su Nadeeyah suka fara shirin barin gurin su Anni,
hankalin Nadeeyah a kwance ta gama shiri dan tasan yanzu su Anty Radiya sun bar gidan,
"kallon banza da habaicin talauci hade da rashin asali da suke mata yana sosa ranta matuka,
kalmar da Anty Raudah ta fadi na "anyi clean fata ta murje da abinci akan kari sai kace wata yar shugaban kasa,
a dai dinga tuno asali dan kar garin iyawa a wuce gona da iri!!
Wadannan kalamai sun matukar tsaya mata,
dan ma Musaddiq dake bayanta wanda dan shi Anty Raudah tayi mata habaicin yace
"Haba Anty, sai kace sa'arki,
dani take magana bada ke ba,
ku ke jawa kanku raini wallahi, yayi tsaki a hankali hade da cewa Nadeeyah ta kira Husnah su tafi...
Hannu ya kyasta mata a kusa da idonta,
a firgice ta dawo daga tunanin abubuwan da suka gifta dazu a gidan,
rage Murya yayi yace
"Tunanin su Anty ko?
Abin da ya kamata ki saba dashi ne tunda saidai in basu zo gidan ba,
in kika kula mutum a kullum burin shi ya bata miki rai to sai kiyi fatali da duk abin da yace, domin shi kadai zaiyi dakon bacin ransa,
"Zuciya is very special my sister,
fill it with love,
karki bari bacin rai ya samu kofar shiga cikinta, dan bacin rai na destroying duk abin da aka tanadarwa zuciya, dan haka bana san ganin tunani ko bacin rai nan a tare dake,
kinji ko?
gyada kai tayi hade da murmushinta mai kyau,
"Thats my lovely sis,
oya kira mana Husnah mu tafi,
kafin ta kai ga amsawa suka hango Husnah sun fito tare da Hafeez da Ruwaidah a tsakiya,
gefe kuma Jamal ne sanye da kayan bacci shima yana dosar inda suke,
"Badai bacci zakayi ba,
Musaddiq ya tambayeshi yana mishi kallon mamaki,
jingina jikin motar yayi yace
"in banyi bacci ba ai sai in kasa moruwa,
yau ko tamola bata kaini garuwa ba,
wahalar da Baffa ya bani yau ba kadan bace,
"duk wani abokinshi da yazo gurin daurin aure wanda baida mota saida na maidashi gida,
just imagine kaine,
hmmm thank Goodness akwai ruwan zafi,
da yau sai na tashi aiki, ya karashe yana danna bayanshi,
"Lazy youth!!
Ruwaidah ta fadi tana boyewa a bayan Hafeez,
dariya ta basu dukkansu Nadeeyah tace
"duk kokarin nan da yayi ki kirashi lazy,
murya cakwai tace
"Allah Adda he is very lazy and he can exaggerate,
yanzu haka gida uku yaje,
haka Mami ke fama dashi baya san a moreshi,
Rai a bace Jamal yayi inda take yana fadin
"ni sa'anki,
wani irin ihu ta saki hade da rugawa ciki,
bayanta yabi da gudu dan yaci alwashin ko a gaban Papy ne sai ya gurji bakinta,
Dariya Hafeez yayi yace ku shiga mota ku tafi dare nayi,
indai su Jamal ne kullum sai sunyi sau ba adadi,
ya kasa gane dadin tsokanarshi takeyi,
saboda bata da abokin wasa shiyasa ta maidashi abokin wasanta, shi kuma san girma yasa baya wasa da ita,
" haushin hakan yasa ta rainashi sosai,
motar suka bude suka shiga suna dariyar Ruwaidah da Jamal,