Sashe 22
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tsugune take tana wanke geron safe tana gyangyadawa hade da shashshekar kuka,
sanyin dake shigarta ta sama da kasa shi ya haifar mata da rawar sanyi sosai,
jingina tayi jikin kwaryar ta fara kiran sunan Allah a cikin ranta, nutsuwace ta fara ratsata kaďan kaďan har bacci ya soma ďaukarta,
ko mintina biyar batayi ba taji muryar Baffa da ya lallabo ya fito yazo inda take,
murya kasa kasa yace "Atika, Atika,
tashi muje ki kwanta,
Kuka sosai ta fashe mishi dashi cikin yarenta na larabci wanda bayaji tace "Dan Allah ka kaini gurin "ummi Aisha",
sunan Aishan da yaji ta kira ne yasa shi cewa "Mai babban suna? Gyada kanta tayi jikinta na rawar sanyi,
Yace "to me mai babban suna tayi?
Ganin da tayi bai gane abun da tace bane yasa ta mike ta fara tafiya dakyar,
wani tausayinta ne ya ratsashi ya tuna abin da ya mata dazu kuma bai samu damar tsayawa ya taimaka mata ba saboda kar ma'u ta dawo,
takawa yayi da dan sauri ya isa gareta ya kamo hannunta ya zaunar da akan dakali,
dan ihu ta saki ta mike tsaye saboda zafi,
"yi hakuri ya fadi jiki a sanyaye tsoro duk ya cikashi,
yaayi ya debo da yawa ya iza wuta ya daura ruwa,
saida ya tabbatar ruwan yayi zafi sannan ya juye mata cikin kwarya yayi mata nuni da ruwan,
da sauri ta matso kusa da ruwan bata damu da tsayuwar da yayi a gurin ba, ta cire kaya ta tsugunna ta fara tsarki tana kuka sosai saboda azaba,
saida ta tabbatar daga zafi ta fara jin dadi sannan ta watsa sauran ruwan a jikinta,
kayanta ta dauka tasa ta wuce dakin da take kwana ta runtse idonta ko baccin da ta fara zaizo ya dauketa,
saidai fa bacci yace ki nemani inda kika ajiye ni,
mikewa tayi tana adduo'i tana rokon Allah abin da yafi zama mata alkairi koda kuwa ace mutuwa ce,
ta tabbatar da yanzu bata da ragowar gata daga Allah sai Hardejo,
shi kuma Hardejo sam bashi da masaniyar halin da take ciki,
da wannan tunanin ta fara gyangyadi har bacci mai cike da mafarkai yayi gaba da ita.....
Watanni uku sun shude,
watanni masu cike da tsananin wuya ga Atika,
duk wani aikin gidan na karfi ita take yinsu, kama da wanki, surfe, da sauransu,
a cikin watannin an samu sauyi na cigaba sosai a kauye,
cigaba daga bangarori da dama,
sannan ci baya ga Baffa,
kullum kwanan duniya sai shanayen da aka bar musu da wadanda ya siyo da kudinshi sun kasa,
saidai ya yanka ya kaisu kauyuka domin a saya,
a haka ne ya zamto mahaucin karfi da yaji,
bai kara marmarin bi takan Atika ba saboda kar tsautsayi yasa har ma'u ta gane,
a cikin wannan halin Ma'u ta dage da sana'oi kala domin ta yi hidimar gidanta da ya'yanta,
Atika itace karfin sana'oin domin ita ke yinsu amma ko dankwali Ma'u bata taba tunanin siyan mata ba...
Yammacin ranar asabar Ma'u na tsugune tana gasa naman gafiya, nan take kamshi mai hade da kauri ya gaurayen gidan,
sannu a hankalin kamshin ke ziyartar hancin Atika dake tsugune tana goga gero a jikin dutse,
tun tana daure jin kamshin har ya gagareta tayi saurin mikewa baki cike da amai ta dinga kwaro shi,
saida ta amayar da komai na cikinta,
ta zaune a gurin tana maida numfashi bayan ta dauraye bakinta,
Bingel wacce ta zamo kawar hirarta ita ta matso da sauri tana shafa mata kai,
ita kuwa ma'u sam bata kawo komai a ranta ba sai ma cigaba da gashi da tayi,
duk tunaninta shawara ce ke damunta, tana gama gashin ta kalli Atika shekeke tayi mata nuni da geron,
a hankali ta mike ta koma bakin aikinta,
tana kallon ma'u ta kasafta naman ita da ya'yanta,
dama naman bai bata sha'awa ba samm,
aikinta ta cigaba dayi,
in kaga yadda take aikin sai ka dauka baiwa ce...,
Jin nama tayi a saitin bakinta,
da sauri ta dago taga Bingel a tsaye tana mata murmushi,
a kasonta ta cire mata da yawa dan taga ba'a bata ba,
wani aman taji ya kara tahowa gadan gadan,
wannan karan a gurin ta sakeshi, wata irin Ashar Ma'u ta saki tace "A kan gari na kikayi min amai,
bata karasa maganar ba taji ta kara kwararo Aman har akan dutsen,
"A'a wannan ba lafiya ba, Ma'u ta fadi tana matsowa kusa da ita,
hannunta ta finciko ta duba,
jiki na kyarma ta daga mata riga, ganin da tayi nonuwanta sun ciko kansu yayi bakikkirin ya sata sakin wata yar kara hade kiran sunan Allah,
ciki gareki?
Ciki gareki Atika?
Babu mayafi haka ta fita ta nufi gidan Haire dan taga Atikar zata bata mata lokaci,
a tsakar gida ta samu Haire da maryam yar Hardejo tana koya musu karatu,
"Haireeeeee ta fadi da karfin gaske,
a kidime Haire tace "lafiya Ma'u? Kuka ne ya kufce mata tace "Haire Atika ciki gareta,
mikewa Haire tayi tace "ci me? Ciki Ma'u ta fadi cikin rawar murya,
Gaba daya idonsu ya rufe sun manta akwai Maryam da yar Hairen kawar maryam a gurin,
"anya ma'u ciki ne, ba kince Baffa bai taba kusantarta ba,
to waye ya mata cikin?
Ma'u tace "nima tunanin da nakeyi kenan,
mayafi Haire ta dauko tace "muje gidan,
Suna fita maryam tace ma Laraba "bari inje gida bayan la'asar zan dawo,
Laraba tace "to sai kin dawo, kinga zanyi aiki da na raka ki,
"babu komai maryam tace sannan ta kwashe yan littafanta tayi gida...
Da gaske kike Maryama? Wallahi ummi (sunan da Atika ta radawa mai babban suna kenan) dagaske nake,
Aisha batayi kasa a gwiwa ba tasa yaro yayi mata magana da Hardejo,
kwashe komai tayi ta fada mishi sannan tace
"Dama Laminjo tasha fada min halin da Atika take ciki a gidan, bana kamawa ne saboda kowa yasan Laminjo yawancin maganganunta karya ne,
rai a bace Hardejo yace "ki shirya zansa Bala ya rakaki sai kuje ku taho min da ita,
tunda Muhammadu ya fara tafiye tafiyen nan nasan lallai rayuwar Atika na cikin garari..
cikin gida Aisha ta shiga ta shirya tsaff da mawafi,
Bala shaho wanda a yanzu ya zamto shakikin gidan Malam Harďejo shi yayi mata rakiya har gidan..
A tsakiya suka sata suna ta jero mata tambayoyi irin na kurame,
da haushi ya ishi ma'u ta tashi ta dauko sandar shaďi ta fara narkarta dashi,
bata taba raba dayan biyu Baffa ne yayi cikin nan,
dukanta takeyi sosai Haire na tarewa tana faďin karki kashe musu 'ya Ma'u,
ki bi komai a hankali,
wani irin hankali zan bishi shi amm,
ni Baffa zai ciwa amana?
Ni zai ha'inta?
kuka sosai takeyi tana dada narkar baiwar Allah da sanda,
kwace sandar Haire tayi tace "shiyasa nace baki da wayau Ma'u,
in ba rashin dabara ba kya fara jibgarta, maimakon ki bari mu yi komai cikin hikima,
ga magunguna nan da zaisa cikin ya fita cikin makwarara....
Saidai kiga bin makwarara a gidanki da yardar Allah Aisha ta fadi tana karasa shigowa cikin gidan rai a baceee.....
Mrs Tijjani Shattima.....
[03/03 9:47 AM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 2⃣6⃣
By *Aysha Ya'u Kurah*
*Rabon Ajali*
Da gudu Bingel ta rungume Aisha tana kuka tana fada mata irin dukan da mamanta tayi ma Atika, share mata hawaye tayi tace "Allah ya turo mai cetonta Zainabu,
in da take tsugune suka karaso Aisha ta dagata tace "muje can gida,
in shaa Allahu daga yau kin bar zaman wahala,
cikin nan kuma sai kin haifeshi koda kuwa dukkan kauyen nan zasu taru akanki,
kuma dole ya amsa sunan Muhammadu a matsayin uba,
wani irin kululun bakin ciki ne ya ziyarci Ma'u,
bata dubi girma da darajar da Aisha kedashi a kauyen ba ta fara zaginta,
ta inda take shiga bata nan take fita ba,
Aisha dai bata waigo ta kalleta ba tace "sai dai ki mutu da bakin ciki dan cikin nan babu abin da zai hanashi zuwa duniya,
wani sabon faifan zagin ta bude idanuwanta sukayi jajur,
asalinta na arniyar ukari marar imani ya bayyana a jikinta,
da sauri Haire ta toshe mata baki tace "mai babban suna kike zagi Ma'u?,
kinason Allahn Hardejo yayi fushi da dukka yan kauyen nan ne?, idan hankali ya gushe nemo shi akeyi,
cike da masifa ta ture Haire tace "wallee sai kunga abinda zai sameku, dukkanku, badai ni *NANKWAT MANASIR* kukayi wa haka ba,(sunanta kenan kafin haduwarsu da Baffa) walle duk sai kun gani,
ta finciko hannun Bingel hade da daukar Boddo ta fice a gidan, hakuri Haire ta bita tana bata, sam bata saurareta ba ta wuce da yaran, Bingel na kuka taki ko kallonta bare ta kula da abinda take so,
Alkhairi!!!
in shaa Allah Aisha ta fadi tana kallon ma'u da tayi nisa da gidan,
gida suka wuce suma Haire na biye dasu tana fadin "Dan Allahn Hardejo kiyi hakuri mai babban suna,
walle ko taba jikinta banyi baa,
katseta Aisha tayi tace "Babu komai Haire, kowa yayi nagari dan kansa...
Suna isa yaran gidan suka rugo suna ihu hade rungumeta,
dama sunyi kewarta matuka dan ma'u bata yarda suzo gidansu,
Matan Hardejo ma suka fito suna musu barka da zuwa hade da jajantawa Atika,
Ďaki Aisha ta wuce da ita, tasa maryam ta iza wuta tasa ruwan wanka,
kafin ruwan yayi zafi ta dama mata fura da nono,
sannan tasa aka karbo mata kwadon zogale a gurin Laure matar Hardejo ta biyu,
zogalen kadai ta iya ci, tasha ruwa, ta dan kwanta a inda take zaune,
bacci ne mai karfi da dadi yayi gaba da ita,
gyara mata kwanciya Aisha tayi cike da tausayawa,
kyakykyawar fuskarta ta kalla ta sa hannu ta share mata hawayen dake gangarowa ta gefen idonta,
a zuciyarta tana Hailala ga ubangijin da yake da ikon mayar da mai gata bawa,
Allah ka ďaura mana jarabawa mai sauki wacce zamu iya daukarta,
da waďannan adduoin mai babban suna ta tashi ta fita tsakar gidan dan samowa Atika naman da zata gasa mata,
sanyin dake shigarta ta sama da kasa shi ya haifar mata da rawar sanyi sosai,
jingina tayi jikin kwaryar ta fara kiran sunan Allah a cikin ranta, nutsuwace ta fara ratsata kaďan kaďan har bacci ya soma ďaukarta,
ko mintina biyar batayi ba taji muryar Baffa da ya lallabo ya fito yazo inda take,
murya kasa kasa yace "Atika, Atika,
tashi muje ki kwanta,
Kuka sosai ta fashe mishi dashi cikin yarenta na larabci wanda bayaji tace "Dan Allah ka kaini gurin "ummi Aisha",
sunan Aishan da yaji ta kira ne yasa shi cewa "Mai babban suna? Gyada kanta tayi jikinta na rawar sanyi,
Yace "to me mai babban suna tayi?
Ganin da tayi bai gane abun da tace bane yasa ta mike ta fara tafiya dakyar,
wani tausayinta ne ya ratsashi ya tuna abin da ya mata dazu kuma bai samu damar tsayawa ya taimaka mata ba saboda kar ma'u ta dawo,
takawa yayi da dan sauri ya isa gareta ya kamo hannunta ya zaunar da akan dakali,
dan ihu ta saki ta mike tsaye saboda zafi,
"yi hakuri ya fadi jiki a sanyaye tsoro duk ya cikashi,
yaayi ya debo da yawa ya iza wuta ya daura ruwa,
saida ya tabbatar ruwan yayi zafi sannan ya juye mata cikin kwarya yayi mata nuni da ruwan,
da sauri ta matso kusa da ruwan bata damu da tsayuwar da yayi a gurin ba, ta cire kaya ta tsugunna ta fara tsarki tana kuka sosai saboda azaba,
saida ta tabbatar daga zafi ta fara jin dadi sannan ta watsa sauran ruwan a jikinta,
kayanta ta dauka tasa ta wuce dakin da take kwana ta runtse idonta ko baccin da ta fara zaizo ya dauketa,
saidai fa bacci yace ki nemani inda kika ajiye ni,
mikewa tayi tana adduo'i tana rokon Allah abin da yafi zama mata alkairi koda kuwa ace mutuwa ce,
ta tabbatar da yanzu bata da ragowar gata daga Allah sai Hardejo,
shi kuma Hardejo sam bashi da masaniyar halin da take ciki,
da wannan tunanin ta fara gyangyadi har bacci mai cike da mafarkai yayi gaba da ita.....
Watanni uku sun shude,
watanni masu cike da tsananin wuya ga Atika,
duk wani aikin gidan na karfi ita take yinsu, kama da wanki, surfe, da sauransu,
a cikin watannin an samu sauyi na cigaba sosai a kauye,
cigaba daga bangarori da dama,
sannan ci baya ga Baffa,
kullum kwanan duniya sai shanayen da aka bar musu da wadanda ya siyo da kudinshi sun kasa,
saidai ya yanka ya kaisu kauyuka domin a saya,
a haka ne ya zamto mahaucin karfi da yaji,
bai kara marmarin bi takan Atika ba saboda kar tsautsayi yasa har ma'u ta gane,
a cikin wannan halin Ma'u ta dage da sana'oi kala domin ta yi hidimar gidanta da ya'yanta,
Atika itace karfin sana'oin domin ita ke yinsu amma ko dankwali Ma'u bata taba tunanin siyan mata ba...
Yammacin ranar asabar Ma'u na tsugune tana gasa naman gafiya, nan take kamshi mai hade da kauri ya gaurayen gidan,
sannu a hankalin kamshin ke ziyartar hancin Atika dake tsugune tana goga gero a jikin dutse,
tun tana daure jin kamshin har ya gagareta tayi saurin mikewa baki cike da amai ta dinga kwaro shi,
saida ta amayar da komai na cikinta,
ta zaune a gurin tana maida numfashi bayan ta dauraye bakinta,
Bingel wacce ta zamo kawar hirarta ita ta matso da sauri tana shafa mata kai,
ita kuwa ma'u sam bata kawo komai a ranta ba sai ma cigaba da gashi da tayi,
duk tunaninta shawara ce ke damunta, tana gama gashin ta kalli Atika shekeke tayi mata nuni da geron,
a hankali ta mike ta koma bakin aikinta,
tana kallon ma'u ta kasafta naman ita da ya'yanta,
dama naman bai bata sha'awa ba samm,
aikinta ta cigaba dayi,
in kaga yadda take aikin sai ka dauka baiwa ce...,
Jin nama tayi a saitin bakinta,
da sauri ta dago taga Bingel a tsaye tana mata murmushi,
a kasonta ta cire mata da yawa dan taga ba'a bata ba,
wani aman taji ya kara tahowa gadan gadan,
wannan karan a gurin ta sakeshi, wata irin Ashar Ma'u ta saki tace "A kan gari na kikayi min amai,
bata karasa maganar ba taji ta kara kwararo Aman har akan dutsen,
"A'a wannan ba lafiya ba, Ma'u ta fadi tana matsowa kusa da ita,
hannunta ta finciko ta duba,
jiki na kyarma ta daga mata riga, ganin da tayi nonuwanta sun ciko kansu yayi bakikkirin ya sata sakin wata yar kara hade kiran sunan Allah,
ciki gareki?
Ciki gareki Atika?
Babu mayafi haka ta fita ta nufi gidan Haire dan taga Atikar zata bata mata lokaci,
a tsakar gida ta samu Haire da maryam yar Hardejo tana koya musu karatu,
"Haireeeeee ta fadi da karfin gaske,
a kidime Haire tace "lafiya Ma'u? Kuka ne ya kufce mata tace "Haire Atika ciki gareta,
mikewa Haire tayi tace "ci me? Ciki Ma'u ta fadi cikin rawar murya,
Gaba daya idonsu ya rufe sun manta akwai Maryam da yar Hairen kawar maryam a gurin,
"anya ma'u ciki ne, ba kince Baffa bai taba kusantarta ba,
to waye ya mata cikin?
Ma'u tace "nima tunanin da nakeyi kenan,
mayafi Haire ta dauko tace "muje gidan,
Suna fita maryam tace ma Laraba "bari inje gida bayan la'asar zan dawo,
Laraba tace "to sai kin dawo, kinga zanyi aiki da na raka ki,
"babu komai maryam tace sannan ta kwashe yan littafanta tayi gida...
Da gaske kike Maryama? Wallahi ummi (sunan da Atika ta radawa mai babban suna kenan) dagaske nake,
Aisha batayi kasa a gwiwa ba tasa yaro yayi mata magana da Hardejo,
kwashe komai tayi ta fada mishi sannan tace
"Dama Laminjo tasha fada min halin da Atika take ciki a gidan, bana kamawa ne saboda kowa yasan Laminjo yawancin maganganunta karya ne,
rai a bace Hardejo yace "ki shirya zansa Bala ya rakaki sai kuje ku taho min da ita,
tunda Muhammadu ya fara tafiye tafiyen nan nasan lallai rayuwar Atika na cikin garari..
cikin gida Aisha ta shiga ta shirya tsaff da mawafi,
Bala shaho wanda a yanzu ya zamto shakikin gidan Malam Harďejo shi yayi mata rakiya har gidan..
A tsakiya suka sata suna ta jero mata tambayoyi irin na kurame,
da haushi ya ishi ma'u ta tashi ta dauko sandar shaďi ta fara narkarta dashi,
bata taba raba dayan biyu Baffa ne yayi cikin nan,
dukanta takeyi sosai Haire na tarewa tana faďin karki kashe musu 'ya Ma'u,
ki bi komai a hankali,
wani irin hankali zan bishi shi amm,
ni Baffa zai ciwa amana?
Ni zai ha'inta?
kuka sosai takeyi tana dada narkar baiwar Allah da sanda,
kwace sandar Haire tayi tace "shiyasa nace baki da wayau Ma'u,
in ba rashin dabara ba kya fara jibgarta, maimakon ki bari mu yi komai cikin hikima,
ga magunguna nan da zaisa cikin ya fita cikin makwarara....
Saidai kiga bin makwarara a gidanki da yardar Allah Aisha ta fadi tana karasa shigowa cikin gidan rai a baceee.....
Mrs Tijjani Shattima.....
[03/03 9:47 AM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 2⃣6⃣
By *Aysha Ya'u Kurah*
*Rabon Ajali*
Da gudu Bingel ta rungume Aisha tana kuka tana fada mata irin dukan da mamanta tayi ma Atika, share mata hawaye tayi tace "Allah ya turo mai cetonta Zainabu,
in da take tsugune suka karaso Aisha ta dagata tace "muje can gida,
in shaa Allahu daga yau kin bar zaman wahala,
cikin nan kuma sai kin haifeshi koda kuwa dukkan kauyen nan zasu taru akanki,
kuma dole ya amsa sunan Muhammadu a matsayin uba,
wani irin kululun bakin ciki ne ya ziyarci Ma'u,
bata dubi girma da darajar da Aisha kedashi a kauyen ba ta fara zaginta,
ta inda take shiga bata nan take fita ba,
Aisha dai bata waigo ta kalleta ba tace "sai dai ki mutu da bakin ciki dan cikin nan babu abin da zai hanashi zuwa duniya,
wani sabon faifan zagin ta bude idanuwanta sukayi jajur,
asalinta na arniyar ukari marar imani ya bayyana a jikinta,
da sauri Haire ta toshe mata baki tace "mai babban suna kike zagi Ma'u?,
kinason Allahn Hardejo yayi fushi da dukka yan kauyen nan ne?, idan hankali ya gushe nemo shi akeyi,
cike da masifa ta ture Haire tace "wallee sai kunga abinda zai sameku, dukkanku, badai ni *NANKWAT MANASIR* kukayi wa haka ba,(sunanta kenan kafin haduwarsu da Baffa) walle duk sai kun gani,
ta finciko hannun Bingel hade da daukar Boddo ta fice a gidan, hakuri Haire ta bita tana bata, sam bata saurareta ba ta wuce da yaran, Bingel na kuka taki ko kallonta bare ta kula da abinda take so,
Alkhairi!!!
in shaa Allah Aisha ta fadi tana kallon ma'u da tayi nisa da gidan,
gida suka wuce suma Haire na biye dasu tana fadin "Dan Allahn Hardejo kiyi hakuri mai babban suna,
walle ko taba jikinta banyi baa,
katseta Aisha tayi tace "Babu komai Haire, kowa yayi nagari dan kansa...
Suna isa yaran gidan suka rugo suna ihu hade rungumeta,
dama sunyi kewarta matuka dan ma'u bata yarda suzo gidansu,
Matan Hardejo ma suka fito suna musu barka da zuwa hade da jajantawa Atika,
Ďaki Aisha ta wuce da ita, tasa maryam ta iza wuta tasa ruwan wanka,
kafin ruwan yayi zafi ta dama mata fura da nono,
sannan tasa aka karbo mata kwadon zogale a gurin Laure matar Hardejo ta biyu,
zogalen kadai ta iya ci, tasha ruwa, ta dan kwanta a inda take zaune,
bacci ne mai karfi da dadi yayi gaba da ita,
gyara mata kwanciya Aisha tayi cike da tausayawa,
kyakykyawar fuskarta ta kalla ta sa hannu ta share mata hawayen dake gangarowa ta gefen idonta,
a zuciyarta tana Hailala ga ubangijin da yake da ikon mayar da mai gata bawa,
Allah ka ďaura mana jarabawa mai sauki wacce zamu iya daukarta,
da waďannan adduoin mai babban suna ta tashi ta fita tsakar gidan dan samowa Atika naman da zata gasa mata,