Sashe 19
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Labarin abin da ya faru ta fada mata hade da cewa "yanzu Hardejo yasa a dauke gawar yaron ayi mata sallah, dan ance saurayin musulmi ne,
kuma ya wakilta wani yaje can tsaunin ya nemo inda yan uwanshi suke a fada musu,
cike da damuwa Haire tace "ni yanzu yar buduwar nake tausayi, dan shaho na can ya tashi hankalin gari,
kuma yace duk wanda ya dauketa ya boyeta in dai ya samu labari sai ya hallaka shi,
kinsan shaho,
a wala hore na,,
duk dakiya irin ta ma'u saida cikinta ya dauki kugi saboda yadda take jin labarin shi tun zuwanta garin da aure ya kawota,,
magana ta fara yi jiki a sanyaye tace
"Haire am kinsan babu abinda zan boye miki,
gyada kai Haire tayi tace "nasani ma'u,
yauwa tace tana mai gyara tsayuwa,
ta kwashe yadda akayi Baffa ya kawo yar makka gidan da kuma amfanin da take ganin yar makkan zata yi mata,
ta karashe da fadin duk irin kokarin da zanyi in ga na samu wani abu a gurin iyayenta da ita zanyi,
sannan kema bazan barki a baya ba, rabawa zamuyi daidai in kin yarda zaki rufa mana asiri,
Ajiye kwarya Haire tayi ta zauna tana washe baki tace "wannan ai karuwar mu ce duka,
ke ni har na fara hango ni a kasa mai tsarki,
yadda su Hardejo suke fadin kasar ace muma gamu a cikinta, shewa sukayi dukkansu Ma'u tace "ai kaff kauyen nan sai sun dawo yi mana bauta,
ke dai ki bani hadin kai mu samu abinda muke so,
yanzu bari kiga sarkar da na dauke mata na hadata da tarkacen tawa,
"aiko dakko ta mu gani,
kin gani, ashe dai dama gaskiyar Hardejo da yace musulunci dadi gareshi,
gashi nan cikin kwanaki kadan da karbarshi mun sami damin arziki, dariyar murna ma'u tayi ta wuce daki inda take jiyo kukan boddo, rashin ganin Baffa a dakin baisa ta kawo komai a ranta ba, ta dauki Boddo Halima ta duba gurin da ta ajiye sarkar taga wayam ba komai,
dube dube ta farayi a gefen da tayi ajiyar, nan ma bata ga komai ba,
a kidime ta fito da sauri tana kiran sunan Baffa,
Rashin ganin bakuwar a inda ta barta ne ya kara daga hankalinta matuka,
bayin gidan ta duba ko tana ciki, nan ma taga wayam babu kowa,
gurin Haire ta koma jiki a sanyaye tace "Baffa ya dauketa a gidannan,
dama yace zai koreta na hanashi, shine ya faki idona ya aiwatar,
shi tsoro gareshi,
daya barni da shaho ni nasan yadda zanyi inyi maganinshi, yanzu gashi ya janyo min asarar sarkar gwal da kyautar da iyayenta zasu mana in sunzo daukarta,
Cike da kunan rai Haire da ta gama hango kanta a wata duniyar tace "amma Baffan Bingel bai kyauta mana ba,
badan sunan annabin Hardejo gareshi ba da sai inyi kokwanton amsar musuluncin shi, tunda ai addinin Hardejo yace mu sowa dan uwanmu abin da muke sowa kanmu,
jugum dai ma'u tayi tana bawa Boddo nono, tunanin ko ina mijinta zai kai yar Makkah ne ya cikata ya hanata magana.....
Shi kuwa Baffa jin hirar da sukeyi da Haire ne ya sashi dauko sarkar da rigarta ya rufe mata fuska hade da kamo hanunta suka fita a gidan,
Hanyar gidan yayanshi Hardejo yayi,
duk wanda ya gansu a hanya sai yayi tunanin Ma'u ce,
wasu a ganinsu wani abu ne ya faru ta rufe fuskarta take kuka,
babu wanda ya ganeta kasancewar ma'u ma fara ce sosai,
saidai farin nasu ba iri daya bane..
A kofar gida ya samu Hardejo yana koyar da samari karatun Allo,
can ciki ya shige gurin matan shi, aiki ya samesu sunayi dukkan su a tsakar gidan,
dakin uwar gidan ya shige kai tsaye tare da ita,
ganin su a haka ya sa uwar gidan cire hannu a aikin ta wankesu tabi bayansu dan jin ko lafiya taga Ma'u haka,
A tsaye ta sameshi yana safa da marwah a cikin dakin,
yana ganinta yace "yauwa me babban suna, dama ke nake jira, taimakona nazo kiyi,
zama tayi kusa da budurwar da take tunanin ma'u ce, tace "me ya sameki ma'u?
Zama yayi daidai kafarta ya bude fuskar budurwar yace ba ma'u bace,
bakuwa ce wacce rayuwarta ke cikin hatsari,
labarin abinda ya faru kaff ya kwashe ya fada mata har dalilin da yasa ya kawota gurinsu,
ya cigaba da fadin "nasan Shaho bashi da karfin da zaizo gidan nan yace zai dauke ta ko ya mata illah,
gata nan zan bar miki ita,
domin Allahn Hardejo ki kula da ita har iyayenta suzo daukarta,,,
A tsorace Aisha (mai babban suna) ta kalli budurwar tace "a wani gari take?
Inafa zan san daga inda take, Baffa ya fadi cike da zullumi, gyara zama tayi tace "to babu matsala, na samu labarin abinda ya faru sama sama dazu,
Kuma naji ance malam ya tura aje a dauko gawarshi mutanen shaho sun hana sun zauna jiran dawowar budurwar ko wanda zai dauki gawar,
cike da tausayawa ta kalli budurwar tace "ya sunanki,
Baffa yayi dariya yace "ai bata jin komai, larabcin kadai na lura take ji,
da yake Aisha ta dade cikin musulunci,
babanta babban malami ne a jalingo, kuma sanadiyyarsu Hardejo ya musulunta har aka bashi aure, tace "maa ismuki ya ukhtee...
cike da jin dadi budurwar tace "ATIKA " *ATIKA SHEIK SAHEEB SAIFUDDEEN*
Juya sunan Baffa yayi tayi yace "kai ilimi akwai dadi, yanzu kinga sai musan labarinta ta dalilinki mai babban suna....
Mikewa Aisha tayi tace "bari in kawo mata abinci taci sai tayi sallah, kaga magariba ta kusa....
Bayan sallar isha'i kowa ya nutsu a gida,
kuka da karai kainin shanaye kadai ke tashi a cikin gidan,
matasa da yaran gidan duk suna zaure suna daukar karatun dare, yayin da wasu daga cikin malaman hardejo suka wanke gawar Habeeb da suka samu daukowa da kyar, hade da suturceta kamar yadda hardejo ya koya musu...
Zaune yake cike da damuwa ya zurawa abincin gabanshi ido, "mutanen kauyen nan har yanzu imani bai gama ratsasu ba,
duk irin fatawar nan da ake badawa bazai sa su hankalta su saduda ba,
Hannu yasa a sama yace " *YA ALLAH DUK WANDA ZUCIYARSHI TAKE A KESASHE BATA DA NIYYAR RUSSUNAWA KUMA BA MAI SHIRYUWA BACE YA ALLAH KAYI MANA MAGANINSU DA GAGGAWA* AMEEN
suka amsa dashi dukkansu,
Adduoi yayi sosai akan duk abinda zai zamto barazana akan alummar musulmi Allah ya kauda shi....
******
Cikin Harshen larabci take bawa Aisha da Hardejo labarinta...
Sheik Saheeb Saifuddeen shine sunan mahaifina,
dan asalin kasar cairo ne, babban malami ne kuma dan kasuwa wanda ake ji dashi a egypt..
Ummuna ta rasu shekara shida da suka wuce gurin haihuwar kanina,
ummuna mahaifinta dan cameroon ne,
mahaifiyarta ce yar cairo,
kasancewata babba gurin mahaifina yasa yake ji dani fiye da kowa,,
Tun bayan rasuwar mahaifiyata aka aura mishi kanwarta Ummul khair saboda ta kula da kanina,
tun daga lokacin rayuwa ta fara sauya mana zuwa yanayi na ban mamaki da tsoro,
abin ya faro ne saboda ganin da ummulkhair tayi Abbuna ya dauki dukkan kulawarshi ya bamu ni da kanina *ATEEK*
kiyayya iri iri babu wacce Ummul bata nuna ma Ateek,
kiyayyarta a garemu batayi karfi sosai ba har saida ta haihu,
a lokacin ne ta nuna wa Ateek karara ba ita ta haifeshi ba,
in na tafi makaranta na barshi kafin in dawo gida ya jigata da yunwa,
gaba daya Ummul ta shafe idonta ta manta da zumunci saboda kasa ta rufe idon ummuna wacce ta zamto yar uwarta ta jini,
burinta a kullum Abbuna ya kula da ita da yaranta guda uku " Haidar, Affan, da Farouk,"
saboda rashin zaman Abbunmu shiyasa bai taba sanin halin da muke ciki ba,
bai kuma kula ya duba ba, saboda a ganin shi kamar da ummunmu muke tare,
bai taba kawo ummul zata taba koda yi mana kallon banza ba, bare har ta kai ga cuzguna mana,
Kakarmu ita kadai ce gatanmu, gurinta hankalinmu ke kwanciya, wannan zuwan da mukayi ma ta'aziyar rasuwarta muka zo, daga can muka taho nan mambila inda kanwar kakanmu (wanda ya haifi ummunmu) take domin gaisheta..
gidan sam baya min dadi saboda duk yan uwa basa kulawa da lamarin mu saboda rashin idon uwa,
kuma suna ganin Ummul ce mai rike damu sannan ga kudi tana musu facaka dashi shiyasa duk suka dauke idonsu akan mu,
rashin jin dadin zaman gidan yasa da na ga Habeeb ya fito zai taho siyan madara na biyoshi dan in zaga inga gari hankalina ya kwanta,
ashe kaddararmu ce anan ni da shi,
tunanina daya *Ateek* da na tafi na barshi yana bacci,
yaya rayuwarshi zata kasance in har babu wanda ya biyo sahun duba ni,
yaya rayuwar Ateek zata kasance, ta karashe cikin kuka mai ratsa zuciya,,,,,
Share hawayen tausayi Hardejo yayi yace "zasu zo su sameki, nasan zasu zo dan na tura a nemo inda iyayen yaron suke,
ko basu zo ba ni zan je har mambilan in kaiki gobe,
cikin kuka tace jirgin su a daren yau zai tashi ya koma cairo,
kuma kasani ba'a samun jirgi akai akai,
Kwantar mata da hankali Hardejo yayi yace "Gobe tun da asuba zan tafi in kaiki, ki kwantar da hankalinki, "
"Abin da Hardejo bai sani ba shine labarin mutuwar Habeeb ya karade ko ina a tsaunin mambila, kuma an hade harda ita Atikar ance an kasheta,
saboda firgicin labarin kuma ance musu limamin garin yasa an dauke gawar an suturce yasa gaba daya yan uwanta suka shirya komawa Cameroon a daren,
harda ita kanwar kakar tasu wacce dama Habeeb din ne karfinta a garin....
Suna idar da sallar asuba sukayi janaizar gawar Habeebu,
bayan an binneshi kamar yadda Hardejo ya karanta sukayi mishi adduoi sosai sannan kowa ya wuce gidanshi,
ko abincin safe bai ci ba ya shirya ya tarar da Atika tana shan fura,
tana gamawa ta mike suka dauki hanyar tafiya tun kafin garin ya gama yin haske,
sai da sukayi tafiyar awa daya sannan suka samu motar awaki ta karasa dasu,
kuma ya wakilta wani yaje can tsaunin ya nemo inda yan uwanshi suke a fada musu,
cike da damuwa Haire tace "ni yanzu yar buduwar nake tausayi, dan shaho na can ya tashi hankalin gari,
kuma yace duk wanda ya dauketa ya boyeta in dai ya samu labari sai ya hallaka shi,
kinsan shaho,
a wala hore na,,
duk dakiya irin ta ma'u saida cikinta ya dauki kugi saboda yadda take jin labarin shi tun zuwanta garin da aure ya kawota,,
magana ta fara yi jiki a sanyaye tace
"Haire am kinsan babu abinda zan boye miki,
gyada kai Haire tayi tace "nasani ma'u,
yauwa tace tana mai gyara tsayuwa,
ta kwashe yadda akayi Baffa ya kawo yar makka gidan da kuma amfanin da take ganin yar makkan zata yi mata,
ta karashe da fadin duk irin kokarin da zanyi in ga na samu wani abu a gurin iyayenta da ita zanyi,
sannan kema bazan barki a baya ba, rabawa zamuyi daidai in kin yarda zaki rufa mana asiri,
Ajiye kwarya Haire tayi ta zauna tana washe baki tace "wannan ai karuwar mu ce duka,
ke ni har na fara hango ni a kasa mai tsarki,
yadda su Hardejo suke fadin kasar ace muma gamu a cikinta, shewa sukayi dukkansu Ma'u tace "ai kaff kauyen nan sai sun dawo yi mana bauta,
ke dai ki bani hadin kai mu samu abinda muke so,
yanzu bari kiga sarkar da na dauke mata na hadata da tarkacen tawa,
"aiko dakko ta mu gani,
kin gani, ashe dai dama gaskiyar Hardejo da yace musulunci dadi gareshi,
gashi nan cikin kwanaki kadan da karbarshi mun sami damin arziki, dariyar murna ma'u tayi ta wuce daki inda take jiyo kukan boddo, rashin ganin Baffa a dakin baisa ta kawo komai a ranta ba, ta dauki Boddo Halima ta duba gurin da ta ajiye sarkar taga wayam ba komai,
dube dube ta farayi a gefen da tayi ajiyar, nan ma bata ga komai ba,
a kidime ta fito da sauri tana kiran sunan Baffa,
Rashin ganin bakuwar a inda ta barta ne ya kara daga hankalinta matuka,
bayin gidan ta duba ko tana ciki, nan ma taga wayam babu kowa,
gurin Haire ta koma jiki a sanyaye tace "Baffa ya dauketa a gidannan,
dama yace zai koreta na hanashi, shine ya faki idona ya aiwatar,
shi tsoro gareshi,
daya barni da shaho ni nasan yadda zanyi inyi maganinshi, yanzu gashi ya janyo min asarar sarkar gwal da kyautar da iyayenta zasu mana in sunzo daukarta,
Cike da kunan rai Haire da ta gama hango kanta a wata duniyar tace "amma Baffan Bingel bai kyauta mana ba,
badan sunan annabin Hardejo gareshi ba da sai inyi kokwanton amsar musuluncin shi, tunda ai addinin Hardejo yace mu sowa dan uwanmu abin da muke sowa kanmu,
jugum dai ma'u tayi tana bawa Boddo nono, tunanin ko ina mijinta zai kai yar Makkah ne ya cikata ya hanata magana.....
Shi kuwa Baffa jin hirar da sukeyi da Haire ne ya sashi dauko sarkar da rigarta ya rufe mata fuska hade da kamo hanunta suka fita a gidan,
Hanyar gidan yayanshi Hardejo yayi,
duk wanda ya gansu a hanya sai yayi tunanin Ma'u ce,
wasu a ganinsu wani abu ne ya faru ta rufe fuskarta take kuka,
babu wanda ya ganeta kasancewar ma'u ma fara ce sosai,
saidai farin nasu ba iri daya bane..
A kofar gida ya samu Hardejo yana koyar da samari karatun Allo,
can ciki ya shige gurin matan shi, aiki ya samesu sunayi dukkan su a tsakar gidan,
dakin uwar gidan ya shige kai tsaye tare da ita,
ganin su a haka ya sa uwar gidan cire hannu a aikin ta wankesu tabi bayansu dan jin ko lafiya taga Ma'u haka,
A tsaye ta sameshi yana safa da marwah a cikin dakin,
yana ganinta yace "yauwa me babban suna, dama ke nake jira, taimakona nazo kiyi,
zama tayi kusa da budurwar da take tunanin ma'u ce, tace "me ya sameki ma'u?
Zama yayi daidai kafarta ya bude fuskar budurwar yace ba ma'u bace,
bakuwa ce wacce rayuwarta ke cikin hatsari,
labarin abinda ya faru kaff ya kwashe ya fada mata har dalilin da yasa ya kawota gurinsu,
ya cigaba da fadin "nasan Shaho bashi da karfin da zaizo gidan nan yace zai dauke ta ko ya mata illah,
gata nan zan bar miki ita,
domin Allahn Hardejo ki kula da ita har iyayenta suzo daukarta,,,
A tsorace Aisha (mai babban suna) ta kalli budurwar tace "a wani gari take?
Inafa zan san daga inda take, Baffa ya fadi cike da zullumi, gyara zama tayi tace "to babu matsala, na samu labarin abinda ya faru sama sama dazu,
Kuma naji ance malam ya tura aje a dauko gawarshi mutanen shaho sun hana sun zauna jiran dawowar budurwar ko wanda zai dauki gawar,
cike da tausayawa ta kalli budurwar tace "ya sunanki,
Baffa yayi dariya yace "ai bata jin komai, larabcin kadai na lura take ji,
da yake Aisha ta dade cikin musulunci,
babanta babban malami ne a jalingo, kuma sanadiyyarsu Hardejo ya musulunta har aka bashi aure, tace "maa ismuki ya ukhtee...
cike da jin dadi budurwar tace "ATIKA " *ATIKA SHEIK SAHEEB SAIFUDDEEN*
Juya sunan Baffa yayi tayi yace "kai ilimi akwai dadi, yanzu kinga sai musan labarinta ta dalilinki mai babban suna....
Mikewa Aisha tayi tace "bari in kawo mata abinci taci sai tayi sallah, kaga magariba ta kusa....
Bayan sallar isha'i kowa ya nutsu a gida,
kuka da karai kainin shanaye kadai ke tashi a cikin gidan,
matasa da yaran gidan duk suna zaure suna daukar karatun dare, yayin da wasu daga cikin malaman hardejo suka wanke gawar Habeeb da suka samu daukowa da kyar, hade da suturceta kamar yadda hardejo ya koya musu...
Zaune yake cike da damuwa ya zurawa abincin gabanshi ido, "mutanen kauyen nan har yanzu imani bai gama ratsasu ba,
duk irin fatawar nan da ake badawa bazai sa su hankalta su saduda ba,
Hannu yasa a sama yace " *YA ALLAH DUK WANDA ZUCIYARSHI TAKE A KESASHE BATA DA NIYYAR RUSSUNAWA KUMA BA MAI SHIRYUWA BACE YA ALLAH KAYI MANA MAGANINSU DA GAGGAWA* AMEEN
suka amsa dashi dukkansu,
Adduoi yayi sosai akan duk abinda zai zamto barazana akan alummar musulmi Allah ya kauda shi....
******
Cikin Harshen larabci take bawa Aisha da Hardejo labarinta...
Sheik Saheeb Saifuddeen shine sunan mahaifina,
dan asalin kasar cairo ne, babban malami ne kuma dan kasuwa wanda ake ji dashi a egypt..
Ummuna ta rasu shekara shida da suka wuce gurin haihuwar kanina,
ummuna mahaifinta dan cameroon ne,
mahaifiyarta ce yar cairo,
kasancewata babba gurin mahaifina yasa yake ji dani fiye da kowa,,
Tun bayan rasuwar mahaifiyata aka aura mishi kanwarta Ummul khair saboda ta kula da kanina,
tun daga lokacin rayuwa ta fara sauya mana zuwa yanayi na ban mamaki da tsoro,
abin ya faro ne saboda ganin da ummulkhair tayi Abbuna ya dauki dukkan kulawarshi ya bamu ni da kanina *ATEEK*
kiyayya iri iri babu wacce Ummul bata nuna ma Ateek,
kiyayyarta a garemu batayi karfi sosai ba har saida ta haihu,
a lokacin ne ta nuna wa Ateek karara ba ita ta haifeshi ba,
in na tafi makaranta na barshi kafin in dawo gida ya jigata da yunwa,
gaba daya Ummul ta shafe idonta ta manta da zumunci saboda kasa ta rufe idon ummuna wacce ta zamto yar uwarta ta jini,
burinta a kullum Abbuna ya kula da ita da yaranta guda uku " Haidar, Affan, da Farouk,"
saboda rashin zaman Abbunmu shiyasa bai taba sanin halin da muke ciki ba,
bai kuma kula ya duba ba, saboda a ganin shi kamar da ummunmu muke tare,
bai taba kawo ummul zata taba koda yi mana kallon banza ba, bare har ta kai ga cuzguna mana,
Kakarmu ita kadai ce gatanmu, gurinta hankalinmu ke kwanciya, wannan zuwan da mukayi ma ta'aziyar rasuwarta muka zo, daga can muka taho nan mambila inda kanwar kakanmu (wanda ya haifi ummunmu) take domin gaisheta..
gidan sam baya min dadi saboda duk yan uwa basa kulawa da lamarin mu saboda rashin idon uwa,
kuma suna ganin Ummul ce mai rike damu sannan ga kudi tana musu facaka dashi shiyasa duk suka dauke idonsu akan mu,
rashin jin dadin zaman gidan yasa da na ga Habeeb ya fito zai taho siyan madara na biyoshi dan in zaga inga gari hankalina ya kwanta,
ashe kaddararmu ce anan ni da shi,
tunanina daya *Ateek* da na tafi na barshi yana bacci,
yaya rayuwarshi zata kasance in har babu wanda ya biyo sahun duba ni,
yaya rayuwar Ateek zata kasance, ta karashe cikin kuka mai ratsa zuciya,,,,,
Share hawayen tausayi Hardejo yayi yace "zasu zo su sameki, nasan zasu zo dan na tura a nemo inda iyayen yaron suke,
ko basu zo ba ni zan je har mambilan in kaiki gobe,
cikin kuka tace jirgin su a daren yau zai tashi ya koma cairo,
kuma kasani ba'a samun jirgi akai akai,
Kwantar mata da hankali Hardejo yayi yace "Gobe tun da asuba zan tafi in kaiki, ki kwantar da hankalinki, "
"Abin da Hardejo bai sani ba shine labarin mutuwar Habeeb ya karade ko ina a tsaunin mambila, kuma an hade harda ita Atikar ance an kasheta,
saboda firgicin labarin kuma ance musu limamin garin yasa an dauke gawar an suturce yasa gaba daya yan uwanta suka shirya komawa Cameroon a daren,
harda ita kanwar kakar tasu wacce dama Habeeb din ne karfinta a garin....
Suna idar da sallar asuba sukayi janaizar gawar Habeebu,
bayan an binneshi kamar yadda Hardejo ya karanta sukayi mishi adduoi sosai sannan kowa ya wuce gidanshi,
ko abincin safe bai ci ba ya shirya ya tarar da Atika tana shan fura,
tana gamawa ta mike suka dauki hanyar tafiya tun kafin garin ya gama yin haske,
sai da sukayi tafiyar awa daya sannan suka samu motar awaki ta karasa dasu,