Sashe 105
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kashe wakar Kamal yayi Taheer ya kama hannun junior suka bi bayansu..
Hannu Hilal ya mika ma Taheer da fara'a dauke a fuskarshi,
"Wow,
matured mind, Taheer ya faďi cikin tsokana,
yanzu ba faďa ko?
Dariya Hilal yayi yace we are Family,
hannu Taheer ya mika mishi da sauri haďe da rungumeshi....
Durkusawa Hilal yayi ya kalli junior,
a hankali ya zare glass din idonshi yace
"Mashaa Allah Junior Kyari,
Mr soft or Hard?
ya tambayeshi yana nuna mishi hannu,
da karfi junior ya dunkule hannu ya buga hannun Hilal yace
"Mr Hard ofcourse!!
Dariya sosai Hilal yayi yace
"Name?
*MHK TAHEER*
amma
*MUKTHAR HILAL MUSADDIQ KYARI* ake cemin a school....
Runtse ido Hilal yayi ya kankame Junior kamar zai maidashi ciki,
my nmsake,
ya Allah..,
I love you boy...
ya karashe haďe da sumbatar shi.....
I love yhu too Junior ya faďi yana mai mayar mishi da sumba..
Hannunshi ya kama suka nufi mota dan su fita ya dan jiyar dashi dadi kafin ya zauna....
A cikin parlon kuwa kowa mamakin ganin Nadeeyah yayi banda Raliya daketa dariya da farin cikin ganin yadda Nadeeyah ta koma...
Anty Reemah da Anni kuwa faďa suka rufeta dashi wanda ita kanta tasan na daďi ne....
Sun dade rungume da Anty Reema tana tambayar ina Zainab?
Cikin kuka Anty Reemah tace "Tayi Fushi,
kika manta da ita ma bare ita, tuni ta mance dake,
tana can gida suna jarabawa ne shiyasa ban taho da ita ba...
Dakyar Nadeeyah ta iya gane Mummy dasu Raudha,
har kasa ta tsuguna ta gaida Mummy wacce fuskarta tayi faca faca da hawayen farin ciki,
rungumae Nadeeyah tayi wani irin kamshin sanyi ya daki hancin dukkaninsu wanda tun zuwansu duniya har kawo yau basu taba jin irinshi ba...
Dafa kafaďunta taji anyi ta raba jikinta da Mummy ta waigo tana murmushi tana kallon matar cikin rashin fahimta,
"Nadeeyah,
dan Allah ki yafe min,
yadda ta haďe hannayenta biyu tana kuka sosai yasa Nadeeyah rike hannun tace
"Me kikayi min, baiwar Allah? Wallahi na yafe miki duk da ban sank----
Badariyyah zanyi fitsari,
Hannafi ya katse Nadeeyah yana matse cinya dan fitsarin ya fara zubar mishi,
Zaro ido Nadeeyah tayi,,
"Badar!!
Ke---ce... ta faďi cikin rawar murya,
nan take wani tsagoron tsoron Allah ya tsarga a zuciyar Nadeeyah,
tana kallon Badariyya ta ďaga yaron da yayi faca faca da fitsari tayi famfon waje dashi...
Jikin Papy Nadeeyah ta kwanta bayan ya gama mata faďa tana tambayarshi Ruwaidah...
"Tana can gurin su Jamal, a can take makaranta...
ya bata amsa yana mai jin dadin ganinta...
Husnah da ta tura mijinta daki saboda mijin Badar, ta fito kamo hannun Nour da Abi taga parlon a nutse sai manyan mutane masu rawuna dake zaune kowa na kasa a nutse,
Gefen da Papy yake ta kalla ta hango fuska kamar ta Nadeeyah,
tasan dai ta baro Maleekah a cikin daki tana sallah, to wacece wannan?
Karasawa tayi ta tsuguna ta gaida bak'in sannan ta kai dubanta kan Nadeeyah,
"Nadeeyah...
ta faďi da karfi har saida Hafeez ya jiyota..
Da sauri ya buďe kofar ya fito yana dube dube yana faďin
"Me ya sameta?,
duk tunaninshi Nadeeyar Hilal ce,
Ganinsu kankame da juna yasa shi saurin matsawa kusa dasu dan ya gasgasta idonshi...
"Yaya Hafeez..
ta faďi tana nufo inda yake,
Share hawayen dake idonshi yayi ya juya zai koma inda ya fito,
Da gudu ta bi bayanshi ta rungumeshi,
"Am sorry,
dan Allah kayi hakuri,
rufe idonshi yayi hawaye na mishi ambaliya..
gabanshi ta dawo tace
"Dan Allah yaya..
Share hawayen yayi yace
"In kowa yayi deserving haka ni banyi ba Nadeeyah,
in akwai wanda ya kamata yasan inda kike to nine,
meyasa zaki bar min tabo a raina?,
kullum ina ganin kamar gazawata ce tasa kika bace,
samm na kasa rike zumuncinmu..
Meyasa zaki min haka?
Sake kankameshi tayi tace
"Nasan ban kyauta,
haka kaddararmu take,
Dan Allah kayi hakuri Yaya....
sunfi minti biyar suna tattaunawa kafin ya sauko ya fara share mata hawaye....
Tun fitowar Hafeez Sarki Tidjani ya mike fadawan shi suka fara yan yameshi,
haka itama Shareefah da hirar Daddy da Anty Saude ta hanata jin komai ta mike cike da firgicin ganin Hafeez...
"ADAMOU YALLO...
sarki ya faďi cikin rawar murya,
Adamou,
innalillahi wa inna ilaihir rajiun, ashe kana nan da ranka Adamou?
Ajiye sandar hannunshi yayi ya isa gurin Hafeez,
sai a lokacin ya dawo hayyacinshi ya fahimci cewa shekarun da yawa Adamou bazai kasance haka ba,
fuskar Hafeez ya shafa yace
"Ina Adamou?
Mikewa Papy da Daddy sukayi suka isa gurin cikin girmamawa,
"Ranka ya dade,
ba Adamu bane,
wannan Hafeezu sunansa,
"Eh na gane yanzu,
ina Adamoun yake,
nasan tunda naga gudan jininshi dole shima ya kasance a kusa....
Garammm....
gaban mutanen parlon ya faďi,
Sai a lokacin yawancin su suka tuna cewa sunan buzu mai gadi marar asali da galihu
*Adamu*,
Daddy ne yayi saurin cewa "Kwarai Adamu shine mahaifin Hafeezu da Nadeeyah ne,
Allah dai yasa lafiya,
ya karashe cikin zullumi ko Adamun ya taba yi musu wani mummunan abu ne,
"Lafiya kalau sai alheri,
Shareefah ta faďi idonta cike da kwallar farin ciki,
"Ina Yayana Adamou??
Dan Allah ku nuna min shi,
ku nuna min shi ko zan samu salama a cikin zuciyata....
Kallon kallo aka fara yi a cikin parlon,
Papy ne yayi karfin halin cewa Sarki ya zauna sai ayi maganar a nutse,
Kamo hannun Hafeez yayi suka koma inda yake zaune,
share kwallar da ta ziraro mishi yayi yace
"Dan Allah ku kira min Adamou, ashe munada rabon sake ganin juna...
Anya ba kuskure kukayi ba?
Wannan buzu Adamu, mai gadi ne, bashi da wata alaka da sarauta,
inajin kamanni ne kawai,
kunsan babu yadda Allah bai iya yi cikin halittarshi...
Baffa ne ke maganar cikin taka tsan tsan dan kar ya bata ran Sarkin...
Murmushin takaici Shareefah tayi ta nuna Hafeez da hannu tace
"In dai wannan jinin Mai gadin ne, to tabbas jinina ne,
idan yayana yayi nisa dan Allah ko zan iya samun hotonshi saboda in tabbatar da zancenku in karyata kaina...
Cikin azama Daddy ya tashi zai nufi sama,
kafin ya karasa Hafeez ya dakatar dashi ya ciro wallet a aljihunshi,
kananan hotunan iyayenshi ne suka bayyana,
da sauri ya mika mata...
*Pappa.....*
Ta faďi cikin kuka dan fuskar mahaifinta ta gani a cikin ta dattijo Adamu,
shi kuwa Hafeez fuskar Yareemah Adamou Sarki Tidjani ke gani a idonshi,
Dan Allah ina yake,
Ku faďa mana inda yake??
Sarki ya tambaya cikin ďaga murya...
Da sauri fadawa suka shiga faďin Allah ya huci zuciyarka...
Baya tare damu,
dan uwanku ya rigamu gidan gaskiya,
ya tafi inda duk zamu tafi komi daren dadewa,
shin dama shi ďin dan gata ne kuka barshi cikin gararin rayuwa?
Ya ilahi me muka maida *ZUMUNCINMU A YAU*
ace yanzu sai in baka raye za'ayi Zumunci da kai,
To Adamu yayi tafiyar da ganinshi yake da matukar wuya,
Adamu yayi muku nisa,
saidai 'ya'yanshi....
yadda Daddy yake maganar ya sanya Parlon yin shuru, sai tashin sheshshekar kuka....
Cikin matsanancin kuka Shareefah ta zaune a kan carpet tace
"Yareemah shine Gata,
kalmar Gata in aka zo kanshi an disa aya,
Shine ďan Sarkin Agadez
*Diya Muradun Abdallah Yallo* na farko,
shine Yareeman Agadez....
Kaddararshi a nan take,
kaddarar samun magaji a nan Nigeria take,
hannayen Hafeez ta rike tana kuka sosai tace
"Rubutun Allah baya goguwa, Allah bai nufeshi da zama Sarki ba wanda hakan shine muradin mahaifinmu da duk daukacin mutanen Agadez,
lallai sarauta rigar ubangiji ce,
ya baiwa mijina wanda yake ďan uwa ga mahaifinka,
sannan ya hanamu haihuwa dan dama ya tanade ta ne domin ka..
Wallahi Allah dole ya zama abin tsoro da girmamawa cikin mu bayinsa,
domin ya wuce duk yadda muke tsammani,
ku duba kuga yadda ya maida dan sarki wanda ya kamata ya zama sarki bawa, mai gadi kaskantacce a gidan bayin da ya kamata su zasu bauta mishi,
cikin kankanin lokaci ubangiji ke sauya alkalaminsa,
ku dubi nisan Agadez da Nigeria, haka kudurar ubangiji ta ingizo shi nan da taimakon marasa imani da tsoron Allah,
duk dan saboda me?
saboda yasan akwai wanda ya tanadarwa aron rigar sarautarshi,
Lallai zaren kaddara baki ne,
ganinshi sai wanda ya halicci kaddarar kanta,
haďuwar Taheer da Nadeeyah,,
zuwan mu nan domin su biyun duk zaren ne ke janmu ba tare da mun ganshi ba,
Allahu Ahad,
Allahu Samad,
buwayi gagara misali,
mai dauke da rayukan da babu wanda yasan adadinsu sai shi kaďai...
Naji dadi matuka da Allah bai dauki raina ba sai da naga gudan jinina,
rungume Hafeez tayi ta yafito Nadeeyah ta haďesu tana kuka tace
"Ina sauran 'yayana?
Share hawayen farin ciki Papy yayi yace
"ďaya ce ta rage,
Zainab,
tana can Cyprus tana karatu,
ga wacce take rikonta can ya nuna Anty Reemah da hannu,
Kiranta gabanta tayi itama ta rungumeta tana mata godiya haďe yin hamdala gurin ubangiji....
Na faďa muku,
yanzu kun gasgata zancena? Yareemah Suhail ya faďi cike da kasaita,
maida dubansu inda yake zaune shi da 'ya'yanshi sukayi,
a harzuke Daddy ya mike yace
"Kai ku tashi ku fice min a gida,
mikewa Papy yayi ya dakatar dashi yace
"Yau ranar farin ciki ce,
ka bar shi alkhairin ne zai fitar dashi in shaa Allah.....
Labarin irin gatan da Yareemah Adamou ya samu da kuruciyarshi suka shiga basu har kawo sanadiyyar barinshi gida...
sannan Sarki ya faďa musu yadda suke da Adamoun ya kuma nuna Taheer yace
"Wannan shine dan kanina, shima dan uwan Adamoun ne....
Kallon juna sukayi shi da Nadeeyah yayi murmushi haďe da kashe mata ido,
da sauri ta kauda kanta cike da kunya,
dadin da takeji a yau kamar an mata albishir da gidan aljanna...
Ashe Taheer dan uwan Nadeeyah ne na jini, haba kaunar tayi yawa, Taheer baya taba likewa mace haka,
ashe connection din mai karfi ne, Anty Saude ta faďi tana dariyar farin ciki....
Dariya akayi a parlon duk da zuciyar Daddy ta ďan sosu da jin maganar kauna daga bakin Anty Saude.....
Baffa ne ya fara basu labarin irin wahalar da Adamun yasha da kuma haďuwarsu da Mamma Suwaiba har mutuwarsu...
Cike da jin daďi hira ta barke a tsakaninsu...
Hannu Hilal ya mika ma Taheer da fara'a dauke a fuskarshi,
"Wow,
matured mind, Taheer ya faďi cikin tsokana,
yanzu ba faďa ko?
Dariya Hilal yayi yace we are Family,
hannu Taheer ya mika mishi da sauri haďe da rungumeshi....
Durkusawa Hilal yayi ya kalli junior,
a hankali ya zare glass din idonshi yace
"Mashaa Allah Junior Kyari,
Mr soft or Hard?
ya tambayeshi yana nuna mishi hannu,
da karfi junior ya dunkule hannu ya buga hannun Hilal yace
"Mr Hard ofcourse!!
Dariya sosai Hilal yayi yace
"Name?
*MHK TAHEER*
amma
*MUKTHAR HILAL MUSADDIQ KYARI* ake cemin a school....
Runtse ido Hilal yayi ya kankame Junior kamar zai maidashi ciki,
my nmsake,
ya Allah..,
I love you boy...
ya karashe haďe da sumbatar shi.....
I love yhu too Junior ya faďi yana mai mayar mishi da sumba..
Hannunshi ya kama suka nufi mota dan su fita ya dan jiyar dashi dadi kafin ya zauna....
A cikin parlon kuwa kowa mamakin ganin Nadeeyah yayi banda Raliya daketa dariya da farin cikin ganin yadda Nadeeyah ta koma...
Anty Reemah da Anni kuwa faďa suka rufeta dashi wanda ita kanta tasan na daďi ne....
Sun dade rungume da Anty Reema tana tambayar ina Zainab?
Cikin kuka Anty Reemah tace "Tayi Fushi,
kika manta da ita ma bare ita, tuni ta mance dake,
tana can gida suna jarabawa ne shiyasa ban taho da ita ba...
Dakyar Nadeeyah ta iya gane Mummy dasu Raudha,
har kasa ta tsuguna ta gaida Mummy wacce fuskarta tayi faca faca da hawayen farin ciki,
rungumae Nadeeyah tayi wani irin kamshin sanyi ya daki hancin dukkaninsu wanda tun zuwansu duniya har kawo yau basu taba jin irinshi ba...
Dafa kafaďunta taji anyi ta raba jikinta da Mummy ta waigo tana murmushi tana kallon matar cikin rashin fahimta,
"Nadeeyah,
dan Allah ki yafe min,
yadda ta haďe hannayenta biyu tana kuka sosai yasa Nadeeyah rike hannun tace
"Me kikayi min, baiwar Allah? Wallahi na yafe miki duk da ban sank----
Badariyyah zanyi fitsari,
Hannafi ya katse Nadeeyah yana matse cinya dan fitsarin ya fara zubar mishi,
Zaro ido Nadeeyah tayi,,
"Badar!!
Ke---ce... ta faďi cikin rawar murya,
nan take wani tsagoron tsoron Allah ya tsarga a zuciyar Nadeeyah,
tana kallon Badariyya ta ďaga yaron da yayi faca faca da fitsari tayi famfon waje dashi...
Jikin Papy Nadeeyah ta kwanta bayan ya gama mata faďa tana tambayarshi Ruwaidah...
"Tana can gurin su Jamal, a can take makaranta...
ya bata amsa yana mai jin dadin ganinta...
Husnah da ta tura mijinta daki saboda mijin Badar, ta fito kamo hannun Nour da Abi taga parlon a nutse sai manyan mutane masu rawuna dake zaune kowa na kasa a nutse,
Gefen da Papy yake ta kalla ta hango fuska kamar ta Nadeeyah,
tasan dai ta baro Maleekah a cikin daki tana sallah, to wacece wannan?
Karasawa tayi ta tsuguna ta gaida bak'in sannan ta kai dubanta kan Nadeeyah,
"Nadeeyah...
ta faďi da karfi har saida Hafeez ya jiyota..
Da sauri ya buďe kofar ya fito yana dube dube yana faďin
"Me ya sameta?,
duk tunaninshi Nadeeyar Hilal ce,
Ganinsu kankame da juna yasa shi saurin matsawa kusa dasu dan ya gasgasta idonshi...
"Yaya Hafeez..
ta faďi tana nufo inda yake,
Share hawayen dake idonshi yayi ya juya zai koma inda ya fito,
Da gudu ta bi bayanshi ta rungumeshi,
"Am sorry,
dan Allah kayi hakuri,
rufe idonshi yayi hawaye na mishi ambaliya..
gabanshi ta dawo tace
"Dan Allah yaya..
Share hawayen yayi yace
"In kowa yayi deserving haka ni banyi ba Nadeeyah,
in akwai wanda ya kamata yasan inda kike to nine,
meyasa zaki bar min tabo a raina?,
kullum ina ganin kamar gazawata ce tasa kika bace,
samm na kasa rike zumuncinmu..
Meyasa zaki min haka?
Sake kankameshi tayi tace
"Nasan ban kyauta,
haka kaddararmu take,
Dan Allah kayi hakuri Yaya....
sunfi minti biyar suna tattaunawa kafin ya sauko ya fara share mata hawaye....
Tun fitowar Hafeez Sarki Tidjani ya mike fadawan shi suka fara yan yameshi,
haka itama Shareefah da hirar Daddy da Anty Saude ta hanata jin komai ta mike cike da firgicin ganin Hafeez...
"ADAMOU YALLO...
sarki ya faďi cikin rawar murya,
Adamou,
innalillahi wa inna ilaihir rajiun, ashe kana nan da ranka Adamou?
Ajiye sandar hannunshi yayi ya isa gurin Hafeez,
sai a lokacin ya dawo hayyacinshi ya fahimci cewa shekarun da yawa Adamou bazai kasance haka ba,
fuskar Hafeez ya shafa yace
"Ina Adamou?
Mikewa Papy da Daddy sukayi suka isa gurin cikin girmamawa,
"Ranka ya dade,
ba Adamu bane,
wannan Hafeezu sunansa,
"Eh na gane yanzu,
ina Adamoun yake,
nasan tunda naga gudan jininshi dole shima ya kasance a kusa....
Garammm....
gaban mutanen parlon ya faďi,
Sai a lokacin yawancin su suka tuna cewa sunan buzu mai gadi marar asali da galihu
*Adamu*,
Daddy ne yayi saurin cewa "Kwarai Adamu shine mahaifin Hafeezu da Nadeeyah ne,
Allah dai yasa lafiya,
ya karashe cikin zullumi ko Adamun ya taba yi musu wani mummunan abu ne,
"Lafiya kalau sai alheri,
Shareefah ta faďi idonta cike da kwallar farin ciki,
"Ina Yayana Adamou??
Dan Allah ku nuna min shi,
ku nuna min shi ko zan samu salama a cikin zuciyata....
Kallon kallo aka fara yi a cikin parlon,
Papy ne yayi karfin halin cewa Sarki ya zauna sai ayi maganar a nutse,
Kamo hannun Hafeez yayi suka koma inda yake zaune,
share kwallar da ta ziraro mishi yayi yace
"Dan Allah ku kira min Adamou, ashe munada rabon sake ganin juna...
Anya ba kuskure kukayi ba?
Wannan buzu Adamu, mai gadi ne, bashi da wata alaka da sarauta,
inajin kamanni ne kawai,
kunsan babu yadda Allah bai iya yi cikin halittarshi...
Baffa ne ke maganar cikin taka tsan tsan dan kar ya bata ran Sarkin...
Murmushin takaici Shareefah tayi ta nuna Hafeez da hannu tace
"In dai wannan jinin Mai gadin ne, to tabbas jinina ne,
idan yayana yayi nisa dan Allah ko zan iya samun hotonshi saboda in tabbatar da zancenku in karyata kaina...
Cikin azama Daddy ya tashi zai nufi sama,
kafin ya karasa Hafeez ya dakatar dashi ya ciro wallet a aljihunshi,
kananan hotunan iyayenshi ne suka bayyana,
da sauri ya mika mata...
*Pappa.....*
Ta faďi cikin kuka dan fuskar mahaifinta ta gani a cikin ta dattijo Adamu,
shi kuwa Hafeez fuskar Yareemah Adamou Sarki Tidjani ke gani a idonshi,
Dan Allah ina yake,
Ku faďa mana inda yake??
Sarki ya tambaya cikin ďaga murya...
Da sauri fadawa suka shiga faďin Allah ya huci zuciyarka...
Baya tare damu,
dan uwanku ya rigamu gidan gaskiya,
ya tafi inda duk zamu tafi komi daren dadewa,
shin dama shi ďin dan gata ne kuka barshi cikin gararin rayuwa?
Ya ilahi me muka maida *ZUMUNCINMU A YAU*
ace yanzu sai in baka raye za'ayi Zumunci da kai,
To Adamu yayi tafiyar da ganinshi yake da matukar wuya,
Adamu yayi muku nisa,
saidai 'ya'yanshi....
yadda Daddy yake maganar ya sanya Parlon yin shuru, sai tashin sheshshekar kuka....
Cikin matsanancin kuka Shareefah ta zaune a kan carpet tace
"Yareemah shine Gata,
kalmar Gata in aka zo kanshi an disa aya,
Shine ďan Sarkin Agadez
*Diya Muradun Abdallah Yallo* na farko,
shine Yareeman Agadez....
Kaddararshi a nan take,
kaddarar samun magaji a nan Nigeria take,
hannayen Hafeez ta rike tana kuka sosai tace
"Rubutun Allah baya goguwa, Allah bai nufeshi da zama Sarki ba wanda hakan shine muradin mahaifinmu da duk daukacin mutanen Agadez,
lallai sarauta rigar ubangiji ce,
ya baiwa mijina wanda yake ďan uwa ga mahaifinka,
sannan ya hanamu haihuwa dan dama ya tanade ta ne domin ka..
Wallahi Allah dole ya zama abin tsoro da girmamawa cikin mu bayinsa,
domin ya wuce duk yadda muke tsammani,
ku duba kuga yadda ya maida dan sarki wanda ya kamata ya zama sarki bawa, mai gadi kaskantacce a gidan bayin da ya kamata su zasu bauta mishi,
cikin kankanin lokaci ubangiji ke sauya alkalaminsa,
ku dubi nisan Agadez da Nigeria, haka kudurar ubangiji ta ingizo shi nan da taimakon marasa imani da tsoron Allah,
duk dan saboda me?
saboda yasan akwai wanda ya tanadarwa aron rigar sarautarshi,
Lallai zaren kaddara baki ne,
ganinshi sai wanda ya halicci kaddarar kanta,
haďuwar Taheer da Nadeeyah,,
zuwan mu nan domin su biyun duk zaren ne ke janmu ba tare da mun ganshi ba,
Allahu Ahad,
Allahu Samad,
buwayi gagara misali,
mai dauke da rayukan da babu wanda yasan adadinsu sai shi kaďai...
Naji dadi matuka da Allah bai dauki raina ba sai da naga gudan jinina,
rungume Hafeez tayi ta yafito Nadeeyah ta haďesu tana kuka tace
"Ina sauran 'yayana?
Share hawayen farin ciki Papy yayi yace
"ďaya ce ta rage,
Zainab,
tana can Cyprus tana karatu,
ga wacce take rikonta can ya nuna Anty Reemah da hannu,
Kiranta gabanta tayi itama ta rungumeta tana mata godiya haďe yin hamdala gurin ubangiji....
Na faďa muku,
yanzu kun gasgata zancena? Yareemah Suhail ya faďi cike da kasaita,
maida dubansu inda yake zaune shi da 'ya'yanshi sukayi,
a harzuke Daddy ya mike yace
"Kai ku tashi ku fice min a gida,
mikewa Papy yayi ya dakatar dashi yace
"Yau ranar farin ciki ce,
ka bar shi alkhairin ne zai fitar dashi in shaa Allah.....
Labarin irin gatan da Yareemah Adamou ya samu da kuruciyarshi suka shiga basu har kawo sanadiyyar barinshi gida...
sannan Sarki ya faďa musu yadda suke da Adamoun ya kuma nuna Taheer yace
"Wannan shine dan kanina, shima dan uwan Adamoun ne....
Kallon juna sukayi shi da Nadeeyah yayi murmushi haďe da kashe mata ido,
da sauri ta kauda kanta cike da kunya,
dadin da takeji a yau kamar an mata albishir da gidan aljanna...
Ashe Taheer dan uwan Nadeeyah ne na jini, haba kaunar tayi yawa, Taheer baya taba likewa mace haka,
ashe connection din mai karfi ne, Anty Saude ta faďi tana dariyar farin ciki....
Dariya akayi a parlon duk da zuciyar Daddy ta ďan sosu da jin maganar kauna daga bakin Anty Saude.....
Baffa ne ya fara basu labarin irin wahalar da Adamun yasha da kuma haďuwarsu da Mamma Suwaiba har mutuwarsu...
Cike da jin daďi hira ta barke a tsakaninsu...