Sashe 28
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Naso yin hakan,amma abin yaci tura saboda guduwa tayi tabar gidan, Baffa ya karashe cike da damuwa,
wani abu Muntarin yaji ya soki kahon zuciyarshi,
har kiyayyar ta kai haka,
ta ina ya gaza da ya samu macen da ta nuna mishi irin wannan kiyayyar,
me ya rasa,
babu abinda bai mallaka ba na daga dangin kyau, ilimi, gayu, uwa uba arziki na jama'a da kuma na dukiya,
me yasa Suwaiba zata rusa tanadin da yayi wa rayuwarsu, yanzu kenan dukkan mafarkinshi zai zamto cikakken mafarki, kenan babu ko daya a cikin mafarkinshi da zai zamto gaskiya,
baisan Hawaye ya fito a cikin idanuwanshi ba saida yaji duminsu a kuncinshi,
mikewa yayi ya fita zauren hade da share hawayen fuskarshi,
motar da suka zo shi da abokanshi ya shiga hade rufe fuskarsa dan hawayen sunki daina zuba,
Allah ya sani ba karamin so yake yi ma Suwaiba ba....
Godiya sosai Baffa yayi wa Baban muntari saboda fahimtarshi da yayi,da Kuma alkawarin da yayi mishi na yarshi bazata wulakanta a cikin zuri'arshi ba,
ko yana so ko baya so dole ya karbeta hannu bibbiyu a matsayin matarshi,
dan zuri'armu kaff babu me wulakanta mace...
Sai dare suwaiba ta dawo gida lokacin Ma'u na buduri da makota ana shirin kai Zainab dakin miji,
kallo ne ya dawo kanta,
daga mai yi mata habaici,
sai mai yi mata kallon marar hankali,
dakin Baffa ta shige a darare, zaune ta sameshi yayi tagumi yana tunanin ta inda zai fara neman suwaiba,
jin muryarta ne ya sanyashi waigowa da sauri,
sanyi yaji a zuciyarshi da ya ganta lafiya kalau,
a fili kuwa fada ya rufeta dashi, saida yayi mata cin mutunci sannan a karshe yace "Wallahi, wallahi, kinga rantsuwar nan, bata da kaffara, bazaki kara daga kafarki kije makaranta ba,
kina cikin gidannan har sai na samu wanda zan bawa ke sadaka, ke ba takamarki kinada farin jinin samari ba,
kin daukesu kamar rigar canji,
to ki sani kin jawa kanki a gurina,
fita ko nan da kofar gida ne ban yarda kiyi ta ba,
sai ki zauna a gidan tunda kin zabi butulcewa Allah da ni'imar da yayi miki,
tashi ki fita ki bani guri mutuniyar banza mutuniyar hofi,
tashi tayi ta fita da gudu tana rusa kuka,
a kofar dakin tayi karo da masu kai Amarya ana wakar "Ayye mama",
ta gefensu tabi ta shige dakinsu ta kara bude wani sabon babin kukan.... (oyoyo talauci inji Meela)
Rayuwar auren Zainab da Muntari kadaran kadaham,
sam baya wulakanta ta saboda ya karanci hakkin mace akan miji, kuma mahaifinshi ya sake tunasar dashi,
Da fari ta dan samu matsala da mahaifiyarshi domin sam bata san zainab,
gani takeyi an lika mishi ita ne dan a cuceshi,
saida "Abba" yayi mata nasihar cewa matar mutum kabarinsa, kuma wata bata auren mijin wata,
sannan ne ta dan sakko,
amma duk da haka bata cika bata muhimmanci ba,
biyayyar da zainab ke mishi ne ya sanya shi sake sakewa da ita,
wani lokaci yakan tuna suwaiba wani shashin zuciyarshi yaji yayi mugun tsanarta,
wani shashin kuma yaji ta ciki a killece,
ya sha in zai ambaci sunan zainab yace suwaiba,
in ko yayi tafiya to fa sai ya cirewa suwaiba tsaraba,
kome zaiyi da ita yake hadawa yayi,
wannan abu shi ya kara dungunzuma zuciyar Zainab taji gaba daya Suwaiba ta fice a ranta,
kullum cikin kulli Goggo take dan dai kawai kar auren yarta ya mutu,
a irin zaman da sukeyi Zainab ta samu ciki har ta haihu, haihuwarta ita ta kara daraja ta a idon iyayenshi da shi kanshi,
sannu sannu ya fara fitar da Suwaiba a cikin ranshi, saboda samun zuri'a da ya farayi.
Saida Zainab ta jera mishi 'ya'ya Mata uku a karancin tsakani (gwarne ) cikin shekara hudun aurensu,
Reemah ce Babba,
sai Radiya
Sai Raudha,
a lokacin da take da cikin na hudu ne Muntari ya saduda ya mika mata ragamar rayuwarshi,
domin yasan yanzu indai za'a kirashi to itace ta biyun da za'a kira a rayuwarshi....
Ita kuwa suwaiba baiwar Allah ta zama baiwa ta gidi,
komai na gidan ita takeyi,
babu makarantar islamiyya, babu fita cikin gari,
iyakarta shagon buzu Adamu mai gadin jikin gidansu,
duk irin kyawun da ta ke dashi ya disashe,
rayuwar dai yinta kawai takeyi saboda Allah a hakan yaso ya ganta,
kullum saidai tayita yi mishi Godiya da bai daura mata ciwo ba....
Leemah kuwa ta zama yar gayu sosai,
university take zuwa Abu zaria,
babu abinda zatace tana dauka a makaranta,
ita dai kawai ta shiga gayu,
yau ta tsaya da wannan gobe wancen,
Baffa daga yayi niyyar yi mata magana Ma'u zata hanashi,
takan ce in ba'a barta taje makaranta ba ina zata samu mijin aure,
dole badan yaso ba ya barta tayi abin da taga dama..
"Bani omo malam Ado, !
dauko mata kullin bulan omo biyar yayi yace "jeki kiyi amfani dashi, na bar miki kudin ki siya silifas naga naki ya tsinke,
murmushi tayi tace "nagode Adamu,
"ba komai suwaiba kedai ki daina yawo ba takalmi,
gyada mishi kai tayi ta wuce cikin gida,
kallo ya bita dashi hade da girgiza kai cike da tausayawa,
duk wannan abun da sukayi a idon Baffa wanda yazo shiga da mota gida,
wani abu ya darsu a ranshi ya shiga gida yayi parking...
"Kanason 'yata Suwaiba?
Daburcewa Adamu yayi da yaji tambayar yace "a'a Alhaji,
ai tafi karfina,
in ba cutarwa ba ta yaya zan auri mace cikin gata alhali ni din ba kowa bane,
dariya Baffa yayi yace "in dai kanajin zaka iya zama da ita to zan aura maka ita,
washe baki Adamu yayi yace "suwaiba mace ce mai kawaici da hakuri Alhaji,
waye zai kita a matsayin mata, bana tunanin akwaishi,
murmushin farin ciki Baffa yayi yace "kaje ka shirya,
rana ita yau zan daura muku aure,
godiya sosai Adamu ya tsuguna yayi ma Baffa sannan ya wuce cikin gidan da yake gadi dan sanar dasu....
Koda ya fada ma Suwaiba nan take ta amince saboda a ganinta gara taje tayi bauta mai dalili, domin ta gaji da aikin jakin da takeyi....
Ranar da aka daura auren duk wani masoyin Suwaiba saida yayi mata bakin cikin karewa da kaskantaccen mutum irin Adamu mai gadi,
shi kuwa Muntari gani yakeyi Hakkinshi ne ke bibiyarta shiyasa ta dade batayi auren ba a karshe ta auri mai gadi...
Rayuwa mai cike da jin dadi da rufin asiri daidai gwargwado sukeyi,
gidan da ya dade yana tari ya siya mai dauke da daki biyu da kitchen nan aka kaita,
sosai take jin dadin zama dashi dan dama sun saba,
shekararsu biyar da aure ta samu cikin Hafeez bayan ta fidda rai,
lokacin Zainab Mummy ta haifi yarta Raudha,
dakatar da haihuwar tayi ta hanyar allura saboda ita a ganinta in dai zata cigaba da haihuwa tofa tabbas mata zata haifa,
wannan jinin zuri'ar mahaifinta ne kamar yadda suka canfa,
a lokacin da aka haifi Hafeez ba karamin girgiza mummy tayi ba, ta dinga tambayar suwaiba yadda akayi ta samu namiji a haihuwar farko wanda saidai tajishi a gari ba'a zuri'arsu ba,
ko da ta tambayeta saidai tayi murmushi tace "daga Allah ne,
tun daga haihuwar Hafeez abubuwa suka fara dan ja baya saboda mai gidan da Adamu ke gadi ya bar garin,
jikin gidanshi ya manna shagonshi da babu isassun kaya a ciki,
dama da albashin shi yake cika shagon yayi hidimar gida,
babu wanda a cikin yan uwanta yake taimaka musu, a ganinta basai ta fito ta fada ba sun san bata dashi...
Shekarar Reemah 15 ta tafi karatun gaba da secondary sokoto,
hazakar ta tasa aka dinga promoting dinta har Allah ya kaita jami'a, anan ne ta hadu da Gaddafi dan 400l,
sanadiyar haduwarsu saboda ya kasance hazikin da ake ji dashi a engineering department,
ko wani irin science course ya iya, kuma yana koya musu dan su biyashi ya samu na siyan hand out,
zuwan Reemah ne yasa suka shaku,
itace siyan hand out da komai nashi,
shiyasa baya kasa a gwiwa gurin kowa mata karatu,
ko da ya gama makaranta ya fito da first class babu wanda ya lura dashi bare yayi yunkurin bashi aiki,
ajiye takardunshi yayi ya dawo cikin school yana hada tutorial dan a dinga biyanshi,
tausayinshi yasa Reemah tayi ma Daddy magana har ya amshi takardunshi ya samar mishi babban aiki a lagos,
tun daga lokacin kauna mai karfi ta kullu a tsakaninsu har ta kaisu ga aure...
A shekarar Farko Allah ya azurta ta da ciki,,
lokacin Mummy ta fidda rai da haihuwa saboda dadewar da tayi, bata san akwai dan makale a tare da ita ba,
Tsirar Haihuwar su kwana tara ne,
domin Reemah ta haihu da kwana tara Mummy ma ta haihu, wannan abun ga mutanen "Da", bawani abun kunya bane,
murnar Samun Musaddiq ba a gurin mummy bane kadai,
har da kakanninshi da babanshi da ya dauki dukkan so ya daura mishi, gata babu irin wacce (Mukhtar) Hilal da Musaddiq basu gani ba, babu tafiyar da Daddy zaiyi ba tare dasu ba..
Kamar yan biyu haka suka taso, kansu daya, kayansu iri daya, kamanni ne kadai suka banbanta shi Hilal fari ne musaddiq kuma Baki ne irin bakin barebari,
gasu da jikin girma Masha Allah, komawar su Reema Cypros ne ya raba su, amma kafin nan koda yaushe suna yare.....
Bangaren Halima kuwa tunda tayi karyar makaranta sun tura ta china karatu shikenan su Goggo suka hau suka zauna ba tare da bincike ba,
yawon barikinta ta tafi yi da kuma neman kudi,
saida ta zama hamshakiyar kanta sannan ta waiwayi gida bayan shudaddun shekaru,
ko da ta dawo saida ta gyara gidansu dan acewarta bazata iya zama a irin gidan ba,
Sana'arta ta business ta cigaba dayi tunda dai yanzu ta gama rikewa tasan babu wanda zaizo yace zai aureta,
abu daya gareta wanda za'a yabeta dashi
shine duk irin duniyancin ta bata yarda da karunwanci ba saboda shegen kyankyami gareta,
shekaru da dama bayan dawowarta ta hadu da wani mayaudarin yaro mai tsantsar *SIHRUL KALAM*
a take ya baibayeta ta fada tarkon kaunarshi,
bata tsaya dogon bincike ba ta yarda ya aureta, hatta sadaki ita ta biya mishi saboda shaukin samun wanda ya furta mata kalmar so...
wani abu Muntarin yaji ya soki kahon zuciyarshi,
har kiyayyar ta kai haka,
ta ina ya gaza da ya samu macen da ta nuna mishi irin wannan kiyayyar,
me ya rasa,
babu abinda bai mallaka ba na daga dangin kyau, ilimi, gayu, uwa uba arziki na jama'a da kuma na dukiya,
me yasa Suwaiba zata rusa tanadin da yayi wa rayuwarsu, yanzu kenan dukkan mafarkinshi zai zamto cikakken mafarki, kenan babu ko daya a cikin mafarkinshi da zai zamto gaskiya,
baisan Hawaye ya fito a cikin idanuwanshi ba saida yaji duminsu a kuncinshi,
mikewa yayi ya fita zauren hade da share hawayen fuskarshi,
motar da suka zo shi da abokanshi ya shiga hade rufe fuskarsa dan hawayen sunki daina zuba,
Allah ya sani ba karamin so yake yi ma Suwaiba ba....
Godiya sosai Baffa yayi wa Baban muntari saboda fahimtarshi da yayi,da Kuma alkawarin da yayi mishi na yarshi bazata wulakanta a cikin zuri'arshi ba,
ko yana so ko baya so dole ya karbeta hannu bibbiyu a matsayin matarshi,
dan zuri'armu kaff babu me wulakanta mace...
Sai dare suwaiba ta dawo gida lokacin Ma'u na buduri da makota ana shirin kai Zainab dakin miji,
kallo ne ya dawo kanta,
daga mai yi mata habaici,
sai mai yi mata kallon marar hankali,
dakin Baffa ta shige a darare, zaune ta sameshi yayi tagumi yana tunanin ta inda zai fara neman suwaiba,
jin muryarta ne ya sanyashi waigowa da sauri,
sanyi yaji a zuciyarshi da ya ganta lafiya kalau,
a fili kuwa fada ya rufeta dashi, saida yayi mata cin mutunci sannan a karshe yace "Wallahi, wallahi, kinga rantsuwar nan, bata da kaffara, bazaki kara daga kafarki kije makaranta ba,
kina cikin gidannan har sai na samu wanda zan bawa ke sadaka, ke ba takamarki kinada farin jinin samari ba,
kin daukesu kamar rigar canji,
to ki sani kin jawa kanki a gurina,
fita ko nan da kofar gida ne ban yarda kiyi ta ba,
sai ki zauna a gidan tunda kin zabi butulcewa Allah da ni'imar da yayi miki,
tashi ki fita ki bani guri mutuniyar banza mutuniyar hofi,
tashi tayi ta fita da gudu tana rusa kuka,
a kofar dakin tayi karo da masu kai Amarya ana wakar "Ayye mama",
ta gefensu tabi ta shige dakinsu ta kara bude wani sabon babin kukan.... (oyoyo talauci inji Meela)
Rayuwar auren Zainab da Muntari kadaran kadaham,
sam baya wulakanta ta saboda ya karanci hakkin mace akan miji, kuma mahaifinshi ya sake tunasar dashi,
Da fari ta dan samu matsala da mahaifiyarshi domin sam bata san zainab,
gani takeyi an lika mishi ita ne dan a cuceshi,
saida "Abba" yayi mata nasihar cewa matar mutum kabarinsa, kuma wata bata auren mijin wata,
sannan ne ta dan sakko,
amma duk da haka bata cika bata muhimmanci ba,
biyayyar da zainab ke mishi ne ya sanya shi sake sakewa da ita,
wani lokaci yakan tuna suwaiba wani shashin zuciyarshi yaji yayi mugun tsanarta,
wani shashin kuma yaji ta ciki a killece,
ya sha in zai ambaci sunan zainab yace suwaiba,
in ko yayi tafiya to fa sai ya cirewa suwaiba tsaraba,
kome zaiyi da ita yake hadawa yayi,
wannan abu shi ya kara dungunzuma zuciyar Zainab taji gaba daya Suwaiba ta fice a ranta,
kullum cikin kulli Goggo take dan dai kawai kar auren yarta ya mutu,
a irin zaman da sukeyi Zainab ta samu ciki har ta haihu, haihuwarta ita ta kara daraja ta a idon iyayenshi da shi kanshi,
sannu sannu ya fara fitar da Suwaiba a cikin ranshi, saboda samun zuri'a da ya farayi.
Saida Zainab ta jera mishi 'ya'ya Mata uku a karancin tsakani (gwarne ) cikin shekara hudun aurensu,
Reemah ce Babba,
sai Radiya
Sai Raudha,
a lokacin da take da cikin na hudu ne Muntari ya saduda ya mika mata ragamar rayuwarshi,
domin yasan yanzu indai za'a kirashi to itace ta biyun da za'a kira a rayuwarshi....
Ita kuwa suwaiba baiwar Allah ta zama baiwa ta gidi,
komai na gidan ita takeyi,
babu makarantar islamiyya, babu fita cikin gari,
iyakarta shagon buzu Adamu mai gadin jikin gidansu,
duk irin kyawun da ta ke dashi ya disashe,
rayuwar dai yinta kawai takeyi saboda Allah a hakan yaso ya ganta,
kullum saidai tayita yi mishi Godiya da bai daura mata ciwo ba....
Leemah kuwa ta zama yar gayu sosai,
university take zuwa Abu zaria,
babu abinda zatace tana dauka a makaranta,
ita dai kawai ta shiga gayu,
yau ta tsaya da wannan gobe wancen,
Baffa daga yayi niyyar yi mata magana Ma'u zata hanashi,
takan ce in ba'a barta taje makaranta ba ina zata samu mijin aure,
dole badan yaso ba ya barta tayi abin da taga dama..
"Bani omo malam Ado, !
dauko mata kullin bulan omo biyar yayi yace "jeki kiyi amfani dashi, na bar miki kudin ki siya silifas naga naki ya tsinke,
murmushi tayi tace "nagode Adamu,
"ba komai suwaiba kedai ki daina yawo ba takalmi,
gyada mishi kai tayi ta wuce cikin gida,
kallo ya bita dashi hade da girgiza kai cike da tausayawa,
duk wannan abun da sukayi a idon Baffa wanda yazo shiga da mota gida,
wani abu ya darsu a ranshi ya shiga gida yayi parking...
"Kanason 'yata Suwaiba?
Daburcewa Adamu yayi da yaji tambayar yace "a'a Alhaji,
ai tafi karfina,
in ba cutarwa ba ta yaya zan auri mace cikin gata alhali ni din ba kowa bane,
dariya Baffa yayi yace "in dai kanajin zaka iya zama da ita to zan aura maka ita,
washe baki Adamu yayi yace "suwaiba mace ce mai kawaici da hakuri Alhaji,
waye zai kita a matsayin mata, bana tunanin akwaishi,
murmushin farin ciki Baffa yayi yace "kaje ka shirya,
rana ita yau zan daura muku aure,
godiya sosai Adamu ya tsuguna yayi ma Baffa sannan ya wuce cikin gidan da yake gadi dan sanar dasu....
Koda ya fada ma Suwaiba nan take ta amince saboda a ganinta gara taje tayi bauta mai dalili, domin ta gaji da aikin jakin da takeyi....
Ranar da aka daura auren duk wani masoyin Suwaiba saida yayi mata bakin cikin karewa da kaskantaccen mutum irin Adamu mai gadi,
shi kuwa Muntari gani yakeyi Hakkinshi ne ke bibiyarta shiyasa ta dade batayi auren ba a karshe ta auri mai gadi...
Rayuwa mai cike da jin dadi da rufin asiri daidai gwargwado sukeyi,
gidan da ya dade yana tari ya siya mai dauke da daki biyu da kitchen nan aka kaita,
sosai take jin dadin zama dashi dan dama sun saba,
shekararsu biyar da aure ta samu cikin Hafeez bayan ta fidda rai,
lokacin Zainab Mummy ta haifi yarta Raudha,
dakatar da haihuwar tayi ta hanyar allura saboda ita a ganinta in dai zata cigaba da haihuwa tofa tabbas mata zata haifa,
wannan jinin zuri'ar mahaifinta ne kamar yadda suka canfa,
a lokacin da aka haifi Hafeez ba karamin girgiza mummy tayi ba, ta dinga tambayar suwaiba yadda akayi ta samu namiji a haihuwar farko wanda saidai tajishi a gari ba'a zuri'arsu ba,
ko da ta tambayeta saidai tayi murmushi tace "daga Allah ne,
tun daga haihuwar Hafeez abubuwa suka fara dan ja baya saboda mai gidan da Adamu ke gadi ya bar garin,
jikin gidanshi ya manna shagonshi da babu isassun kaya a ciki,
dama da albashin shi yake cika shagon yayi hidimar gida,
babu wanda a cikin yan uwanta yake taimaka musu, a ganinta basai ta fito ta fada ba sun san bata dashi...
Shekarar Reemah 15 ta tafi karatun gaba da secondary sokoto,
hazakar ta tasa aka dinga promoting dinta har Allah ya kaita jami'a, anan ne ta hadu da Gaddafi dan 400l,
sanadiyar haduwarsu saboda ya kasance hazikin da ake ji dashi a engineering department,
ko wani irin science course ya iya, kuma yana koya musu dan su biyashi ya samu na siyan hand out,
zuwan Reemah ne yasa suka shaku,
itace siyan hand out da komai nashi,
shiyasa baya kasa a gwiwa gurin kowa mata karatu,
ko da ya gama makaranta ya fito da first class babu wanda ya lura dashi bare yayi yunkurin bashi aiki,
ajiye takardunshi yayi ya dawo cikin school yana hada tutorial dan a dinga biyanshi,
tausayinshi yasa Reemah tayi ma Daddy magana har ya amshi takardunshi ya samar mishi babban aiki a lagos,
tun daga lokacin kauna mai karfi ta kullu a tsakaninsu har ta kaisu ga aure...
A shekarar Farko Allah ya azurta ta da ciki,,
lokacin Mummy ta fidda rai da haihuwa saboda dadewar da tayi, bata san akwai dan makale a tare da ita ba,
Tsirar Haihuwar su kwana tara ne,
domin Reemah ta haihu da kwana tara Mummy ma ta haihu, wannan abun ga mutanen "Da", bawani abun kunya bane,
murnar Samun Musaddiq ba a gurin mummy bane kadai,
har da kakanninshi da babanshi da ya dauki dukkan so ya daura mishi, gata babu irin wacce (Mukhtar) Hilal da Musaddiq basu gani ba, babu tafiyar da Daddy zaiyi ba tare dasu ba..
Kamar yan biyu haka suka taso, kansu daya, kayansu iri daya, kamanni ne kadai suka banbanta shi Hilal fari ne musaddiq kuma Baki ne irin bakin barebari,
gasu da jikin girma Masha Allah, komawar su Reema Cypros ne ya raba su, amma kafin nan koda yaushe suna yare.....
Bangaren Halima kuwa tunda tayi karyar makaranta sun tura ta china karatu shikenan su Goggo suka hau suka zauna ba tare da bincike ba,
yawon barikinta ta tafi yi da kuma neman kudi,
saida ta zama hamshakiyar kanta sannan ta waiwayi gida bayan shudaddun shekaru,
ko da ta dawo saida ta gyara gidansu dan acewarta bazata iya zama a irin gidan ba,
Sana'arta ta business ta cigaba dayi tunda dai yanzu ta gama rikewa tasan babu wanda zaizo yace zai aureta,
abu daya gareta wanda za'a yabeta dashi
shine duk irin duniyancin ta bata yarda da karunwanci ba saboda shegen kyankyami gareta,
shekaru da dama bayan dawowarta ta hadu da wani mayaudarin yaro mai tsantsar *SIHRUL KALAM*
a take ya baibayeta ta fada tarkon kaunarshi,
bata tsaya dogon bincike ba ta yarda ya aureta, hatta sadaki ita ta biya mishi saboda shaukin samun wanda ya furta mata kalmar so...