Sashe 113
Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 2 min read
Tsaye Daddy yayi ya kasa tabuka komai saboda bashi da karfin yin wani abu domin yayi iya kokarinshi ya fahimtar da ďàn nashi ba komai kake so kake samu ba,
bazai iya tunkararsa ba a yanzu ya riga ya sare da rayuwar danshi,
yasan zaiyi matukar wahala ya rayu..
ganin Daddy ya kasa cewa komai yasa su Anty Reemah sake sakin wani kukan,
ita kuwa Husnah kiran wayar Hafeez da Papy takeyi tana ihu tana kiran sunan Musaddiq,
Da sauri Taheer yayi gurin suka haďu da Hilal suna kokawar tare,
wani hauri ya kaiwa Hilal a ciki wanda sam baisan yayi ba ma,
ya riga yaci alwashin aikatawa shiyasa yasa ďaya daga cikin abokansu siyo mishi ba tare da yasan abun da zaiyi dashi ba,
sannan abun da idonshi ya gane mishi daga sama shi ya sake tunzura zuciyarshi ya tabbatarwa kanshi babu fashi sai ya aikata abun da yayi niyya...
Rike ciki Hilal yayi ya kasa tashi aka bar shi da Taheer da ya matse hannunshi koda kuwa kwalbar zata tsaga dukkan hannunsu,
ba tare da ankara ba Taheer yaji nashi ta bayan hannun,
a gigice ya saki hannun wanda hakan ya bawa Musaddiq damar ďaga kwalbar da sauri,
ihuu dakin ya dauka suna rokarshi da Allah da annabi,
Juyawa Daddy yayi ya bar ďakin yana mai kuka cikin zuciyarsa na irin tarbiyar da kowanne cikin 'ya'yansa suka samu,
ya sadakar ďan da yafi kowa kauna cikin yayanshi yau zai kauracewa ganinshi,
ya barshi ya aikata abun da yake so domin kuwa ko ya hanashi sai ya aikata tunda tun tasowarshi bai nemi abu ya rasa ba sai wannan..
A hanzarce Nadeeyah ta haye gadon da zai sadata da daidai hannunshi ta sanya iya karfinta ta kabe hannun haďe da daukeshi da lafiyayyun mari har biyu sannan tayi mishi wata iriyar runguma wacce bin umurni ne daga zuciyarta,
Tsittt dakin yayi kamar babu wani mahaluki da yake rayuwa a cikinsa,
daddadar muryar Nadeeyah kaďai ake ji wacce take fitar da ita cikin raunannen kuka.......
Mrs Tijjani Shattimah........
bazai iya tunkararsa ba a yanzu ya riga ya sare da rayuwar danshi,
yasan zaiyi matukar wahala ya rayu..
ganin Daddy ya kasa cewa komai yasa su Anty Reemah sake sakin wani kukan,
ita kuwa Husnah kiran wayar Hafeez da Papy takeyi tana ihu tana kiran sunan Musaddiq,
Da sauri Taheer yayi gurin suka haďu da Hilal suna kokawar tare,
wani hauri ya kaiwa Hilal a ciki wanda sam baisan yayi ba ma,
ya riga yaci alwashin aikatawa shiyasa yasa ďaya daga cikin abokansu siyo mishi ba tare da yasan abun da zaiyi dashi ba,
sannan abun da idonshi ya gane mishi daga sama shi ya sake tunzura zuciyarshi ya tabbatarwa kanshi babu fashi sai ya aikata abun da yayi niyya...
Rike ciki Hilal yayi ya kasa tashi aka bar shi da Taheer da ya matse hannunshi koda kuwa kwalbar zata tsaga dukkan hannunsu,
ba tare da ankara ba Taheer yaji nashi ta bayan hannun,
a gigice ya saki hannun wanda hakan ya bawa Musaddiq damar ďaga kwalbar da sauri,
ihuu dakin ya dauka suna rokarshi da Allah da annabi,
Juyawa Daddy yayi ya bar ďakin yana mai kuka cikin zuciyarsa na irin tarbiyar da kowanne cikin 'ya'yansa suka samu,
ya sadakar ďan da yafi kowa kauna cikin yayanshi yau zai kauracewa ganinshi,
ya barshi ya aikata abun da yake so domin kuwa ko ya hanashi sai ya aikata tunda tun tasowarshi bai nemi abu ya rasa ba sai wannan..
A hanzarce Nadeeyah ta haye gadon da zai sadata da daidai hannunshi ta sanya iya karfinta ta kabe hannun haďe da daukeshi da lafiyayyun mari har biyu sannan tayi mishi wata iriyar runguma wacce bin umurni ne daga zuciyarta,
Tsittt dakin yayi kamar babu wani mahaluki da yake rayuwa a cikinsa,
daddadar muryar Nadeeyah kaďai ake ji wacce take fitar da ita cikin raunannen kuka.......
Mrs Tijjani Shattimah........