← Book details Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 46 OF 113

Sashe 46

Zumuncin Mu A Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

kalle kalle ta shiga yi suka hada ido da Hafeez ya gyada mata kai yana murmushi,

mikewa tayi ta isa gabanshi tana mai mamakin kamannin,

tsugunawa tazo yi yayi saurin dagota ya rungumeta,

kukan da yake kokarin boyewa yaki boyuwa saida ya zubda su,

Damke Hannun Hilal dake yunkurin zuwa gurin Husnah tayi tace "Babanta ne fa,
twins din Mama Suwaiba,

cikin rashin fahimta yace "what, ba Baffa yace ya mutu ba,

Baffa dake zaune ya jiyo Hilal yace
"muma duk haka muka dauka Muntari,
ashe yana nan da ranshi,

kaddarar da ta boye mana shi ita ta sake hadamu dashi,

kallon Nadeeyah da ta kasa sakin jiki har lokacin Baffa yayi yace

"saki jikinki,
wannan uwa yake a gurinki, haka uba,
domin tare suka zo duniya da Mahaifiyarki,

kallonshi tayi sosai dan ta gasgata maganarshi,

tun daga hannayenshi har kafarshi saida ta kare musu kallon,

kyawawan yatsun kafarshi da ya zamto irin na Mamma da nata shi ya tabbatar mata da maganar Baffa,

wata irin runguma ta sake yi mishi tana kuka sosai a zuciyarta tana jero alhamdulillah,

ta kusa minti uku a jikinshi tana tunano rayuwar da sukayi da Mamma,

ji takeyi kamar dawo da ita Allah yayi cikin wata suffar,

saukowa a jikin Mami Ruwaidah tayi ta kama hijab din Nadeeyah tace

"let my Papy be,

karki bata mishi kaya da hawayenki,

Papy na baya son kuka,

dagashi tayi ta fara shafa fuskar Ruwaidah hade da rungumeta,

duk rashin son mutanen Ruwaidah ta kasa nuna shi ga Nadeeyah,

sai ma ce mata da tayi, "ki daina kuka mana,
na fada miki Papy baya son kuka,

ko so kikeyi yasa Yaya Jamal ya daura ki a bayan *OBENIZA*

Dariya Hafeez da Jamal suka saki dan sunsan ta da mugun tsoron obeniza,

share hawaye Nadeeyah tayi tace "nayi shuru,

hannu Ruwaida tasa a gefen kumatunta ta share mata wasu hawayen tace

"you are very beautifull,

Yaya Jamal batayi kama da *MALEEKA SAHEEB* ba,

kaga har one dimple din,

kallon ta yayi yaga tabbas akwai kamanni saidai Maleeka akwai wayewar larabawa yan drama sosai a tare da ita,

kaunar da sukeyi wa films dinta ya sanya kowa a gidan saninta...

Masallaci suka tafi dan yin sallar Magriba,

matan kuma duk sukayi a cikin daki,

Badar kuwa dakin mummy taje ta kwanta dan jikinta yayi tsami sosai,

har lokacin zubar hawaye takeyi tana kara jin tsanar Nadeeyah wacce take jin kamar da tsanar aka haifeta..

fada sosai Mummy tayi mata dan ta tsorata sosai bata san hukuncin da Daddy zai yanke a kanta ba...

Magana ce a bakin Papy amma kunya ta hanashi furta ta,

a yadda yake ji yanzu baijin zai iya koda kwana daya baisa duk su ukun a ido ba,

harda Zainab da ya ga hotonta tamkar shi ya haifeta dan babu inda ta barshi,

kallon Daddy yayi yace

"Alhaji mun gode fa,
gaskiya samun mutum irinka a wannan zamanin sai an tona,

ni inaga jibi zan koma Gombe,

nace --- ko --am ko---

dariya sosai Daddy yayi dan ya gano manufarshi,

kace ko zaka iya tafiya Nadeeyah ko?

Cike da jin kunya Papy yayi dariya yace

"kunya ta hana ni fadi,

Daddy yayi saurin cewa "na lura da hakan,

amma fa bazan baka ba ya fadi cike da zolaya,

Dariya Papy yayi yace

"ai yarka ce, ka fini iko da ita,

amma dan Allah ina rokon alfarmar tazo mana hutun wata daya,

cike da farin cikin girmamashi da akayi Daddy yace

"watanni ma Proff,

kar ka damu sun kusa zana jarabawar waec,
daga ta zana zata zo tayi maka hutu har sai ka kaji da ita,

"inaa bazamu gaji ba Anni ta fadi tana dariya,
tace "Allah ya kaimu lokacin,

Da sauri Hilal yace
"Daddy ayi mata transfer kawai tayi waec din acan,
gara ta dan zauna a can ta samu nutusuwar zana jarabawa,

"Bata da nutsuwa ne anan?
Baffa ya jeho mishi tambayar,

"a'a ina nufin zata ji dadin ganin su,
kuma zata fi yin karatu sosai acan,

Anty Raly da harbo jirginshi tace "babu inda zata,
bamu gaji da ganinta ba,
tayi zamanta har sanda Daddy yace,

badan Raliya ta girmeshi ba,
da babu abinda zai hana bai zageta ba,

murmushi tayi hade da mishi gwalon babu yadda zaiyi da ita,

ba yadda zaiyi haka ya hakura,
yasa ma ranshi zai tsoratar da ita sosai akan kula samari musamman Taheer da yayi mishi muguwar tsana a ganin farko...

Sai gurin tara da rabi su Papy suka bar gidan,

babu yadda ba'ayi Ruwaidah ta zauna ba taki,
duk da dan zaman da sukayi ta fara sabawa da Nadeeyah da Husna...

Nadeeyah ta kira wannan ranar da ranar farin ciki,

tabbas ta yarda in alheri zai doso ka sai ka hadu da bacin rai mai tarin yawa,

kwana tayi tana hamdala tana godewa Allah......

A daren Daddy ya yanke hukucin bazai cigaba da zama da Badariyya a gidanshi ba,

domin kuwa zata bata mishi zuciyar ya',

babu irin hakurin da Mummy bata bashi ba ya kekashe kasa yaki hakura kuma ya hada yi ma Badariyya gori sosai badan baya santa ba, sai dan ta hankalta ta dawo cikin hankalinta,

Wannan gori na rashin asali da yayi ma Badariyya,
ba karamin tsayawa a ran Mummy da Badar din yayi ba,

Ranar da Nadeeyah tayi kwanan farin ciki,
a ranar Badariyya kwana tayi kuka tana saka mugayen abubuwan da zatayi ma Nadeeyah......

Mrs Tijjani Shattima....
[24/03 9:36 PM] Ummu Abdul 2: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 4⃣3⃣
By *Aysha Ya'u kurah*

Da sassafe Mummy ta sa Husnah da Nadeeyah suje su roki Daddy akan ya bar Badar ta zauna a gidan,

ko da suka je dakin a bakin gado suka sameshi yana duba laptop dinshi,

gaisheshi sukayi suka hada baki suka ce

"Daddy dan Allah kayi hakuri ka kyale Badariyya,

Nadeeyah tace "sharrin shaidan ne Daddy,
baya wuce kan kowa,
in shaa Allahu zata canza,
kayi hakuri dan Allah,

glass din idonshi ya cire yace

"zanyi hakuri saboda darajar ki,

ke aka batawa kuma ke kika bada hakuri,

babu yadda zanyi tunda kin hakura ni ma dole in hakura,

amma sai na karya rantsuwata,
taje gidan Goggo tayi wata daya,

Mikewa sukayi suna godiya suka fita daga dakin,

Mummy da ta gama jinsu ta wuce dakin su Badar tace ta shirya zata kaita gidan Goggo tayi kwana biyu har Daddy ya huce,

kwallar da ta ciko idonta tayi saurin mayarwa,
ta mike sukuku ta fara fito da kayanta,

fita Mummy tayi dan bazata iya Kallon kayan tausayin nan ba,

karfe goma daidai bayan sun gama karyawa ta fito da akwatinta ta fitar waje,

shi kanshi Daddy saida ya dan tausaya mata saboda ta zama kamar jininshi,

halayyarta ce sam baya so tun tana karama,
shiyasa ko kadan baya bi ta kanta,

Har mota Husnah ta rakata itama tausayinta ya cika ta dan bata saba zaman ko ina ba sai gida,

ko gidajen su Anty Radiya bata zuwa da kwana saidai da yini,

bare gidan Goggo, ko toilet kadai ya ishi Badar....

A hanya Badar ta kalli mummy dake tuki tace "Mummy alfarma nake so kiyi min,

"ina jinki,

ta amsa idonta na kallon titi,

juyowa tayi tana kallon Mummy sosai tace

"Mummy aure nake son ayi min?

Kirrrrrr.....

Mummy ta taka birki ta kalleta tace
"aure?

Wani irin aure kuma,?

kukan munafurci ta fara kirkirowa tace

"Aure dai Mummy wanda akeyi,

dan Allah kuyi min aure,

sake tada motar Mummy tayi tace "to sai ki turo mijin da zaki aura tunda ke kika zabi hakan da kanki,

Abun da take jira dama kenan tayi saurin cewa
"ni bana tsayawa da saurayi,

ke zaki samo min Mummy,

dariya Mummy tayi tace
"yarinta hoo,

to karki damu bari in nutsu zan duba cikin ya'yan kawayena,

cikin sauri ta tari hanzarinta tace
"a'a Mummy,

gara dai ki nemo min a family,

kinga a gida ne kadai zanyi aure hankalin kowa ya kwanta,

Tsayar dasu traffic yayi Mummy tace "to Badariyya ina muke da aukin maza a family,

ko Hafeez kike so?

Allah ya kyauta tayi saurin fadi tana tofar da miyau waje,

to shi kadai ne sai Hilal da yake danki,

sai kuma
*MUSADDIQ*
Badar ta karshe da sauri,

Mummy ina son yaya Musaddiq, dan Allah ayi mana aure cikin gaggawa plsss,

faduwar gabar da tashin hankalin da Mummy ta shiga ba mai misaltuwa bane,

bata kara kallon Badar ba ta cigaba da tukinta,

magiya sosai Badar takeyi mata amma Mummy ko kallonta batayi ba bare tasan tana yi,

suna shiga gidan Mummy tasa Rilwanu daukar akwatin Badar..

Bayan Mummy tabi tana tambayarta dalilin da yasa bata san Musaddiq ya aureta,

a daidai gurin da zai sadasu da tsakar gidan Mummy tace

"kar in sake jin kin maimata maganar nan, bare har wani yaji!!

Tana kaiwa nan tayi Sallama ta fada cikin gidan,

Da gudu Badar tabi bayanta kamar zatayi kuka,

Mummy ta san sarai Badariyya naci gareta,

bata gama tunanin ba taji Badar na cewa pls Mummy,

a harzuke Mummy ta juya ta kalleta tace

"bani hankalinki nan,
aure ya haramta tsakaninki da Musaddiq,

Dariyar takaici Badar tayi tace "Haramta?

Menene ya haramta shi,
naga we are cousins saidai in baki son farin ciki na,

Buge bakinta Mummy tayi da karfi hade da cewa "bance karki kara min maganar nan ba,

Zafin buge bakin da zafin ganin zata rasa masoyinta yasata sakin wani irin Kuka,

Inda take Goggo tayo tana tambayar dalilin kukanta,

bata amsa ta ba ta cigaba da kukanta,

Mummy ce ta tsuguna a gabanta zata fara rarrashi,

kafin tayi magana ta katseta...

"Cikin kuka mai cin rai tace menene ya haramta aurena da Yaya Musaddiq Mummy,
menene shi,

a iya sanina bake kika haifeni ba,

nasan babu abin da zai haramta aurena dashi saidai in kema so kikeyi ki min gori akan asalina kamar yadda Daddy yayi m----

tassss..

mummy ta dauke ta da mari,
itama kukan ne ya subuce mata ta rungumota tace

"Allah ne ya haramta shi Badar,

Asalinki bazai taba zame min abin gori ba saboda ke din makwafi biyu gareki a gurina,

na diya da kuma kanwa,

ke kadai ce jinin yar uwata wacce nake gani inji dadi,

ban damu da ya kikazo duniya ba nidai nasan ina ganinki a matsayin LEEMAH,
Chapter 46 · 0% Book details