← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 99 OF 114

Sashe 99

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A hankali ya tura qofar sashen nasu ya sanya kai tana biye dashi,sanyi da qamshin dake falon ya cika hancinsa ya haifar masa da wata nutsuwa ta musamman,suna isa falon ya aje jakar hannunshi ba tare daya saketa ba,idanunta ta daga ta dubi qwayar idanunshi,ta sauya kala hakanan kana dubansu kasan an tono wani abu dake zuciyarshi,sai ta zame hannyenta cikin sauri ya rungumoshi ta baya,kusan a tare suka sauke ajiyar zuciya shi da ita,bacin ran daya tabashi sai taji duka babu dadi,bai kamata daga dawowarsa yaci karo da wata matsala ba,ya kamata zuwa yanzu ya samu hutu da kulawa da kuma dukkan wani kwanciyar hankali daya kamata,bata taba ganin bacin rai a fuskarshi kamar haka ba,bata taba ganin fadanshi kamar yau ba,da alama wannan gyambon dake zuciyarshi ne aka taba,sai taji zuciyarta ta karye,hawaye suka biyo kuncinta,wanda sukayi nasarar taba jikinsa,idanunshi na lumshe ya sanya hannunshi ya dawo da ita gabanshi,ya bude hannayensa ya sakata cikin faffadan qirjinsa ya maida hannayenshi ya kulleta gam,muryarshi can qasa yace
"Meye abun kuka?"
"Bai kamata ace wannan ne abu na farko da zaka tarar ba bayan ka dauki wani lokaci baka gida" ta furta cikin sanyinta da muryarta data bayyana kukanta qarara,tattausan tafin hannunshi ya sanya ya soma goge mata fuska,har a lokacin tana jikinsa
"Abu mafi ciwo shine abinda sukayi miki,me yasa kika tsaya saurarensu da banxayen maganganunsu?,me yasa bakiyu umarnin an fitar miki dasu daga gidanki ba?,ke din ba sa'arsu bace,darajarki da tasu ba daya bace.."
"Kayi haqur....." Ta fada cikin raunin murya da zuciya gaba daya,saidai bai barta ta qarashe furucin nata ba ya hade bakinshi da nata cikin wani irin zafin nama da ba zatan da bata taba tsammata ba.

A hankali ya zare bakinsa kana ya dan dafe kanshi
"Ya salam" ya furta cikin matuqar sanyi,da hanzari ta dubeshi duk da sanyin da jikinta yayi matuqa
"Me ya faru,ya khalip...." Ta kasa qarasawa tana dubanshi,dubanta yayi suka hada idani,duk da yadda kanshi ke sarawa amma hakan bai hanashi tuno yanayin daya shiga ba,idanu daya ya kashe mata kafin yace
"Kaina"
"Sannu am sorry,ka zauna pls" ta fada tana nuna mishi kujera hannunta daya riqe da nashi hannun,sai ya kalle hannayen nasu dake cikin na juna,ya daga yakai bakinsa yayi kissing kafin ya saki a hankali ya koma saman daya daga cikin kujerun ya zauna,tausayinshi take ji,ciwon kan da su suka zama silarshi,gashi kuma basu qyaleshi ba suna haddasa tashinsa lokaci zuwa lokaci,sunkuyawa tayi a nutse ta dauki jakarshi daya aje a wajen ta nufi bedroom dinsu.

Minti uku kafin ta fito ta sameshi idanunsa a rufe
"Ga ruwa can ko watsa ko zaka ji dadin jikinka" a hankali ya bude idanun nashi ya warasu a kanta,sun qara girma hakanan sun sauya launi,sai taji sun mata nauyi da kwarjini da yawa,kanta ta dan dauke tana basarwa,kunya na lullubeta sakamakon tunawa da tayi da abinda ya faru daxu
"Yau garin akwai zafi,hadarine tun jiya kuma ruwa bai sauka b...." Bata qarasa ba ta jita cikin jikinshi,saitayi sak kunya na addabarta,bakinsa yakai saitin kunnenta
"Ki shirya kayanki kafin na fito" a hankali ya saketa yana takawa zuwa cikn dakin gadon yana jin yadda kanshi ke sarawa,yasan mawuyacine idan baiyi jiyya yau zuwa gobe ba,yayin daya barta nan tsaye tana saqe saqen me yake nufi?,watsar da wannan tunanin tayi ta shiga kitchen dinsu cikin hanzari ta soma sama masa abinda zai saka a cikinsa mai sauqi da dad'i.

Har ta kammala komai ta shirya bata ji motsi ko fitowarsa ba,duk sai ta kasa zama,saboda haka ta shirya komai ta tura qofar dakin duk da yadda zuciyarta ke gargadarta.

Zaune yake daure da towel,hannunshi daya dafe da kanshi,yayin da daya hannun yake amsa waya,yanayin yadda yake amsar wayar ya tabbatar mata ranshi a bace yake,magana ta qarshe yayi ya katse kiran,sai ya sake kiran wata number,haidar ya kira yace su dawo gida shida mus'ab,sannan ya sake kiran wani layin shima yayi magana ta 'yan sakanni ya sauke wayar a kunnensa,kashe wayar yayi gaba daya ya ajeta gefanshi,idanunsa suka sauka akanta,ya saki qaramar ajiyar zuciya yana jin bacin ranshi yana zaganyewa,idanunsa ya lumshe cikin ranshi yana addu'ar Allah ya sanya ta zama sanyin idaniya a gareshi,ta fahimceshi ta soshi cikin qanqanin lokaci kamar ko fiye da yadda yake sonta
"Uwaishah!" Ya kirata cikin taushin nan dake kasheta,kasa amsa mishi tayi da.baki saida idanu,wanda hakan ya masa tasiri matuqa
"Taimaka min..." Sai.yayi mata nuni da ma'ajiyar kayanshi,ta fahimci me yake nufi,saboda haka ta miqe a nutse zuwa wajen shi kuma ya bita da kallo,kayan data sanya din sun amsheta sun burgeshi qwarai,sun fidda duk wata qira tata,wani azababben kishi daya sake sanya kanshi sarawa yaji ya saukar masa,saiya dafe kan nashi,har ta dauko kayan tazo gefanshi ta aje masa,ta juya da niyyar fita yace da.ita sanda ya.miqe ya ware kayan zai sanya
"Karki motsa ko ina,samu waje ki zauna" hakanan ta zauna inda ta tashi,ta dan kauda idonta gefe don kada ta kalleshi,ya fahimceta sarai,sai yaci gaba da sanya kayanshi har ya kammala,

Wata jaka ya janyo gabanshi ya soma hada wasu kaya cikin wata jaka,kayan abinci ta aje tana murza tafin hannunta
"Ga abinci nan" ta furta cikin sanyi da nutsuwa,kallonta yayi da idanun nan nasa dake mata kwarjini matuqa
"Ki shirya abinda zaki shirya nan da minti biyar" kamar zata tamnayeshi sai kuma ta fasa,koma meye ta sani bazai cutar sa ita ba,saita qarasa a hankali ta amshi jakar da yake saka kayayyakin a ciki taci gaba da sanya mishi,gefe daya ya koma ya zauna kawai yana binta da kallo ta qasan ido,duk wani motsinta yana biye da ita,duk da ciwon kan dake matsa mishi kadan kadan amma sai yake jin dadin kallonta fiye da tunani.

Bayan ta kammala.itama ta debi 'yan qananun abubuwan da take da buqata ta zuba a tata jakar,sai data gama tsaf ya juyo da niyyar sanar masa taga ita yake kalla
"Na gama" ta fadi tana neman wajen zama,saiya ciro wayarshi tana ji ya kira sunan mus'ab da haidar da alama da daya daga cikinsu yake sake magana,bayan ya gama saiya kashe wayar ya aje,yaci gaba da kallonta cikin zuciyarshi yana wassafa yadda zai dasa mata sonshi da qaunarshi mai tafiya da hankali da kuma ruhi,ba'a dauki dogon lokaci ba suka jiyo knocking,saiya miqe a hankali cikin mutuwar jiki ya nufi qofar fita yana cewa
"Ki sanya mayafinki ki taho" hijabi ta sanya saman kayan jikinta,ta dauki jakar hannunta sannan ta fito falon,suna tsaye su uku,haidar mus'ab da shi khaliphan yana miqa musu key
"Kada yarinyar da kuka sake bari ta zauna cikin gidan nan har anni ta dawo,ku kulle ko ina zanyi magana da securities din gidan"
"Toh yaya" haidar ya fada yana karbar muqullin
"Mus'ab shiga ciki ka daukon jaka ka sameni a mota" ya fada yana yin gaba tana biye da shi.

Motoci biyu ne tsaye suna jiransu,da kanshi ya bude mata mazaunin baya kamar yadda ya dinga mata wancan karon,ta shiga shima yabi bayanta,mus'ab ya sanya kayan a motar ya rufe sannna ya zagayo ya musu sallama bayan ya miqo musu kwandon abincin da ayshan ta hada wanda baici ba,bata sani ba koshi yace ya dauko din,driver yaja motar suka fita daga gidan.

Shuru motar ta dauka,idanunshi na rufe da alama ciwon kan ke takura mishi,duk sai taji bata ji dadi ba,ta dokanta ta ganshi sai gashi yazo cikin bahagon yanayi
"Sannu" ta furta cikin nuna damuwa da kulawa,idanunsa da suka qara girma ya ware a kanta,murmushi ya sakar mata wanda ya sake sanyata cikin rudu,hannunshi yakai ya dora saman nata hannun sai ya maida idanun nashi yadda suke,yana jin yadda laushin fatarta da dumin jikinta ke ratsa shi

Tafiya ce da bata wuce ta minti ashirin ba suka shigo cikin wata unguwa,a ido kawai ya isa yasa ka gane kyau da tsari da kuma yanayin wadata da jama'ar unguwar keda,sai takejin kamar tasan unguwar kota taba ganinta,a hankali motocin suka ci gaba da tafiya har xuwa qofar wani katafaren gida daya tilastata daga kai ta kalleshi,horn daya akayi qofar gidan ta wangale,sai a sannan taga yayi mata kama da gidanta da aka fara kawota.

A harabar aje motoci sukayi parking
"Zauna ina zuwa" ya fada yana ficewa,ta cikin motar tana iya hango abinda ke faruwa,kayan da sukazo dasu aka shiga dasu ciki har kayan abincinsu,tsahon minti biyar sannan ya dawo ya mata izinin fita,wannan karon hannunshi cikin nata suka dinga takawa zuwa cikin gidan,suna tafiya tana sake gane gidan dukda ba wani shahararren kallo tayi masa ba tun a wancan lokacin.

Kwandon abincin dake aje a falon ya sunkuya zai dauka tayi saurin dauka da azama,suka hada ido tadan basar sukaci gaba da tafiya zuwa wani sashe na daban wanda batasan dashi ba cikin gidan,idanu ta ware tana kallon ko ina,bai saki hannunta ba sai da suka dangana da wani bedroom wanda yafi kyau a kirashi da aljannar duniya,idanunta basu taba tozalin ganin dakin bacci mai kyau da aka qawatashi ba irin haka
"Barkanki da dawowa gidanki" ya fada yana shigewa toilet dake cikin dakin,tilas bayan ta gama kalle kallenta ta aje kwandon daura da ita ta samu waje ta zauna kan wata kujera dake can nahiya guda ta dakin saboda yalwar da dakin yake dashi.

Bai jima ba ya fito daure da alwala,tana lura da komai yake yana yine cikin juriya,wani saqo dake cikin dakim shimfide da abun sallah ya shiga ya tada sallah da alama shafa'i da wuturi xaiyi,don tuni sunyi magariba da isha'i a gida.

Ya jima saman abun sallar yana addu'a sannan ya shafa,ya taso cikin nutsuwa zuwa inda take zaune,gefan gadon ya samu ya zauna yana fuskantarta idanunshi akanta.
54
Chapter 99 · 0% Book details