Sashe 16
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tausayin ayshan ya hana zuciyar aliya sukuni,haka ta dinga share qwalla itama,itakanta mamakin wannan lamari take wanda bama ita ba,ayshan ma baki daya batasan daga inda ya somo ba,sai data gama don kanta sannan ta goge fuskarta aliyan na lallashinta da kalamai masu dadi cike da qauna da tausayawa
A gajiye ya koma gida a ranar,hakan ya sanya hatta da abincinsa a dakinsa yaci,hakanan tsakanin amal da zeenart ba wadda ya baiwa damar ganinsa,wanka kawai yayi yayi dai dai qasan carfet yana cin abinci,qwaqwalwarsa cike take da lissafe lissafen ayyukan dake jiransa gobe da kuma cikin satin,a matuqar gajiye ya jawo briefcase dinsa don ya ciro system dinsa,sunyi da wani abokin kasuwancinsa da zasu fara harkar fita da wasu samfurin duwatsu masu daraja zuwa china zasu qarasa maganarsu a lokacin.
Har ya kammala cin abincin amma yana kan system din,sai dayaji bacci na rinjayarsa sannan ya kashe yana zuba hamma,ya bude brieafcase din ya maidata,inda ya aje kudi ya bude ya soma zarasu,don sunyi magana da haidar zai aikashi gidan kawunsu dake da buqatar kayan abinci,dubu dayan ce ta fado,cikin mamaki ya saka hannu ya dagata yana kallo,don har ga Allah ya mance da ita,a hankali ya tuno inda ya sameta,murmushi ya saki yana tuna abinda ya faru,shi kansa abun ya qayatar da shi,tamkar a majigin film,wai shine aka ci kwala ana tuhuma da cin bashin naira dari biyar
"Ya Allah" ya fada yana maida bayansa jikin kujera ya jingina,yadda komai ya faru yana dawo masa fes kamar yanzu abun ke faruwa
"Ita din wacece?" Ya tambayi kanshi,baisan ko wace ba,amma abinda tayin ya burgeshi,hakan yana nuna tana da zuciya mai kyau,ta gefe daya tsiwar asma'u da dagiyarta yana dan burgeshi,yanayin son ajinta,adonta,yana son mace mai ado bawai kwalliya ba,to ita ya fuskanci duka ta hada,a hankali bacci barawo ya saceshi a yadda yake zaunen.
Kiran sallar farko ya farka kaman yadda ya saba,sosai wuyanshi ya riqe saboda yanayin kwanciyar da yayi,da addu'a a bakinsa ya shiga bandako,wanka ya soma sannan ya daura alwala,jallabiyya ya zira bayan ya wadata jikinsa da tsadajje kuma daddadan turarensa mai sanyin kwantar da hankali,idanunsa ya lumshe yana sheqar qamshin turaren yana tuna masa da wata rayuwa can baya,rayuwar da tazo ta wuce musu tamkar a mafarki,dalili biyu yasa yake amfani da turaren lokaci lokaci,na farko yana son qamshinsa,na biyu kuma dukan daya taba ci dalilin turaren a hannun yaya ibrahim,yaya ibrahim din da a yanzu shine gatansa,rayuwa na bashi tsoro,yanayin yadda rayuwa ke garawa tana qara sashi jin tsoron Allah kadaitashi da kuma imani da shi,da ire iren wannan tunanin ya tada sallar nafila kafin zuwan lokacin asubah
.
A kullum babu wata rana da zata zo ta wuce khalipha baiyi ire iren wannan tunanin ba,wani abu ne daya shafi rayuwarsa,abu ne daya tana rayuwarsa ya kuma shiga cikin tarihinta.
Baccin da yaso komawa bayan sallar asubar bai samu ba ya hau net yana rage ayyukan dake gabanshi,qarfe takwas ya fito daga wanka,yana tsane jikinsa da towel kira ya shigo wayarsa,ya qarasa yana duba mai kiran,ramla ce,dauke kanshi yayi kamar bai ganin kiran,yasan tatsuniyar gizo bata wuce ta qoqi,yasan bai wuce ta gaya masa cewa zata zo ba,abinda shi kuma baiso kenan,matsalar daya anni....baisan mai yasa ba....anni nada zuciyar mantuwa da yafiya,ta fishi sanin yaran su su waye suba wajensu suda iyayensu,amma tanayi kamar ta manta koma bata sani ba kwata kwata baki daya,suna zuwa su zauna mata suyu mata hidima,bayan yasan kowacce akwai manufarta cikin zuciya,shikam baijin zai manta ba kuma don bai yafe ba,a'ah..sam,amma iyaye daban suke,duk wani abu daya taba illata ko jirkita duniyar jin dadinsu baijin dan halak zai manta da hakan,dalili kenan daya sanya daga shi har haidar da salim ba wata qwaqwqwarar jituwa ko shaquwa a tsakaninsu da dukka yaran,baiga kuwa dalilin da zai saka ya zabesu a matsayin matan aure ba.
Kiran nata na katsewa kiran P.A dinshi ya shigo,a ladabce ya gaidashi shi kuma ya amsa a mutunce,nan yake sanar masa yau nefa tafiyar
"Wacce kenan haris?
" yallabai south africa din,na tura maka komai jiya ta email dinka da watsapp amma naga kaman baka gansu ba"kanshi ya dafe yana ambatar sunan Allah,shaf ya manta baki daya,don har yau yana da agender tare asma'u a capterian makarantarsu,amma dole ya aje komao saboda tafiyar nada muhimmanci
"Qarfe nawa ne tafiyar?"
"Jirgin qarfe daya ne sir"
"Is ok....ba damuwa" ya fadi yana katse wayar.
A nutse ya shirya cikin qananun kaya da sukai matuqar fidda sigarsa,sun masa kyau sosai,slippers ya saka ya fito izuwa sashin anninsa.
Ko ina agyare yake tsaf yana fidda qamshin turaren wuta na icce tamkar ba safiya ba,manyan abubuwa da yake jinjinawa anninsa da shi kenan,yake ganin da wuya ya samu mace wadda keda kaso daya cikin ukun halayenta,tsanani ko wuya,samu da talauci basu taba sanya annin nashi qazanta ba dai dai da qwayar zarra.
Tamkar ba safiya ba haka falon yake,kai baka ce ana zama cikinsa ba,dakinta ya wuce kai tsaye,a falonta dake manne da dakin gadonta ya sameta,wanda ita da iyalinta kawai ke zama a can,tsaf ya sameta kamar kullum,sanye da atamfar super riga da zani plain,dinkin jikinta yayi dai dai da shekarunta ya kuma yi mata kyau sosai,hannunta riqe da cup na tea na tangaran tana shan dafaffen shayin na'a na'a,yayin da daya hannun nata ke riqe da casbaha tana ja,qamshin falon nata daban da wanda ya baro,cikin fara'a ta aje kofin hannunta a gefe tana masa maraba da zuwa,cike da qauna ya isa gefanta ya zauna gabanta yana lanqwashe qafafunsa
"Barka da safiya anni...."
"Barka kadai muhammadu.....mun tashi lpy?"
"Lafiya lau,ya qarfin jiki?"
"Mun godewa Allah"
"To Allah ya qara lafiya da tsahon kwana mai amfani"
"Amin don isar annabi da alqur'ani....hala yau ba zaka fita bane"
"Zan fita anni....amma sai wajen azahar haka...inasu haidar ne?"
"Salim dai bai jima da ficewa motsa jiki ba,haidar kuwa kasan yana can yana bacci" sumarshi ya shafa sannan yace
"Mtswee....ya kamata na maidasu kamfani hakanan anni...zaman hutun ya isa haka"
"Ya kamata kam...nima ina shirin tuna maka....".
Amal ce tayi sallama ta shigo falon cikin dinkin doguwar rigar atamfa,tayi kwalliya a fuskarta tamkar ba safiya ba,ta laqanci khalipha sosai,me yakeso meye baya so,kanta a qasa cikin nuna yanayin jin kunya ta qaraso,khalipha ta soma gaidawa wanda hakan sam bai masa ba sannan ta gaida anni,jima kadan tace
" me xaka ci ya khalipha"son samu yace babu komai,amma annin ta hanashi hakan,ko baya sha'awa tace ya karba,don kada ya sosa ran dan uwanshi musulmi yaga kaman ya gwasaleshi
"Bani tea mara madara"
"Kawai?" Ta tambaya cikin salo,kai ya kada mata,sai ta miqe ta fice
"Muhammadu ya maganar da mukayi abincin da za'a kai gidan kawunka?"kai ya kada idanunsa na kallon qasa yace
"Anni....anni keta daban ce....kin manta komai kenan?" Murmushi tayi mai dauke da ma'anoni da dama sannan tace
"Muhammadu...duk wanda Allah ya doraka a kanshi ka riga ka fishi kenan har abada baida yadda zaiyi....sannan rama alkhairi gamai cuta ba illa ne ba.....baida amfani a lokacin daka tserewa wani abu ka dinga qoqari da fadi tashin tunawa da shi,da kuma maida hannun agogo baya...rayuwa idan ta wuce ta wuce kenan har abada,ka kalli gaba...ka kumayi qoqarin gina gaban...ka manta baya...zuciya mai yafiya ita Allah yakeso yake maraba da ita,zuciya mai manta sharri,zuciyar dake manta alkhairi itace abar neman tsari,koda yaushe ka zama mai manta sharri,mai saka cuta da alkhairi ina fata ka fahimta"
"Na fahimta anni....madalla da samun uwa irinki...koda yaushe ina godewa Allah daya bamu ke a matsayin uwa....dai dai da rana daya baki taba umartarmu da yin wani abu ba dai dai ba komai tsanani komai wuya"ya fadi yana gyada kai
"Burin uwa ta gari muhammadu ko yaushe ta dora diyanta kan tafarkin tsira duniya da lahira"
"Haka ne....yau za'a kai in sha Allahu,zan baiwa haidar ya kai masa"
"Allah ya albarkaceka kai da 'yan uwanka duniya da lahira....ya jiqan mahaifinku"
"Amin summa amin anni",ya jima suna hira shida ita har haidar da salim suka shigo suka samesu a haka,baibar wajenta ba sai da sha daya na safiya tayi,yana matuqar jin dadin zama da mahaifiyar tasa,macace mai hikima dattako da sanin ya kamata,idan ka zauna da ita ko yaya saika amfana ko ka qaru da wani abu mai muhimmanci da baka sanshi ba.
A dan gurguje ya shirya cikin shigar suits,wanda kallo daya ya isar sanar maka da awanne aji take,yana cikin gyara tie din wuyanshi gaban madubi idanunsa suka sauka kan vivo dinshi dake aje gefan madubi,murmushi ya subuce masa sanda ya tuna agender dinsu da haduwarsu ta qarshe da asma'u,dariyar data dinga masa shida wayar tana masa kallon wani shashasha gaula,tuni ya gama gane inda ta dosa,saidai game din da suke bugawa shida ita hakanan ke burgeshi tare da bashi qawa,yakan raya a ransa tunda har take tsaiwa suyi magana koda ba mai dadi bace watan wata rana zata saurareshi,zata fuskance shi,za kuma ta zama tashi,hakanan yayi sha'awar kiranta,sai ya kunna wayar yana ci gaba da shiryawa tare da jiran ta kawo.
Yana takawa harabar gidan wayar na ringing alamun tana shiga bayan yayi sallama da anni,yaranshi suka bude qofar motocin suna jiran qarasowarshi,ganin haka ya dakata daga dan nesa kadan,ta daga wayar saidai bata amsa ba,hakan ke alamta ta gane cewa shine
"Assalamu alaikum ranki ya dade"
"Ya akayi yaron oga?" Ta fada cikin isgili tana dariya dariya,baki daya ta daukeshi kaman wani abun wasa a gareta,don tasan cewa babu hadin kifi da kaska,babu abinda ya hada kashi da fura,sam tafiyarsu ba daya bace,hanyar jirgi, mota bata isa tabi ba,murmushi ya saki,kafin yace komai tace
"Naga alama kai kam da gaske kake.....tunda har haka ne....kazo ka sameni ina son ganinka" sosai maganar ta bashi mamaki,saidai baiji komai ba,cikin salo yace da ita
"To babu damuwa,saidai yanzu haka oga ya aikeni ne,ya turani wani waje,aqalla zanyi sati biyu haka,idan na dawo zan iya zuwa?"
"Baka da case" tace da shi tana katse wayar,kashe wayar yayi baki daya yana dan nazari,murmushi yake kadan kadan,daya daga cikin yaranshi nazir ya qaraso ya amsa ya mata waje.
A gajiye ya koma gida a ranar,hakan ya sanya hatta da abincinsa a dakinsa yaci,hakanan tsakanin amal da zeenart ba wadda ya baiwa damar ganinsa,wanka kawai yayi yayi dai dai qasan carfet yana cin abinci,qwaqwalwarsa cike take da lissafe lissafen ayyukan dake jiransa gobe da kuma cikin satin,a matuqar gajiye ya jawo briefcase dinsa don ya ciro system dinsa,sunyi da wani abokin kasuwancinsa da zasu fara harkar fita da wasu samfurin duwatsu masu daraja zuwa china zasu qarasa maganarsu a lokacin.
Har ya kammala cin abincin amma yana kan system din,sai dayaji bacci na rinjayarsa sannan ya kashe yana zuba hamma,ya bude brieafcase din ya maidata,inda ya aje kudi ya bude ya soma zarasu,don sunyi magana da haidar zai aikashi gidan kawunsu dake da buqatar kayan abinci,dubu dayan ce ta fado,cikin mamaki ya saka hannu ya dagata yana kallo,don har ga Allah ya mance da ita,a hankali ya tuno inda ya sameta,murmushi ya saki yana tuna abinda ya faru,shi kansa abun ya qayatar da shi,tamkar a majigin film,wai shine aka ci kwala ana tuhuma da cin bashin naira dari biyar
"Ya Allah" ya fada yana maida bayansa jikin kujera ya jingina,yadda komai ya faru yana dawo masa fes kamar yanzu abun ke faruwa
"Ita din wacece?" Ya tambayi kanshi,baisan ko wace ba,amma abinda tayin ya burgeshi,hakan yana nuna tana da zuciya mai kyau,ta gefe daya tsiwar asma'u da dagiyarta yana dan burgeshi,yanayin son ajinta,adonta,yana son mace mai ado bawai kwalliya ba,to ita ya fuskanci duka ta hada,a hankali bacci barawo ya saceshi a yadda yake zaunen.
Kiran sallar farko ya farka kaman yadda ya saba,sosai wuyanshi ya riqe saboda yanayin kwanciyar da yayi,da addu'a a bakinsa ya shiga bandako,wanka ya soma sannan ya daura alwala,jallabiyya ya zira bayan ya wadata jikinsa da tsadajje kuma daddadan turarensa mai sanyin kwantar da hankali,idanunsa ya lumshe yana sheqar qamshin turaren yana tuna masa da wata rayuwa can baya,rayuwar da tazo ta wuce musu tamkar a mafarki,dalili biyu yasa yake amfani da turaren lokaci lokaci,na farko yana son qamshinsa,na biyu kuma dukan daya taba ci dalilin turaren a hannun yaya ibrahim,yaya ibrahim din da a yanzu shine gatansa,rayuwa na bashi tsoro,yanayin yadda rayuwa ke garawa tana qara sashi jin tsoron Allah kadaitashi da kuma imani da shi,da ire iren wannan tunanin ya tada sallar nafila kafin zuwan lokacin asubah
.
A kullum babu wata rana da zata zo ta wuce khalipha baiyi ire iren wannan tunanin ba,wani abu ne daya shafi rayuwarsa,abu ne daya tana rayuwarsa ya kuma shiga cikin tarihinta.
Baccin da yaso komawa bayan sallar asubar bai samu ba ya hau net yana rage ayyukan dake gabanshi,qarfe takwas ya fito daga wanka,yana tsane jikinsa da towel kira ya shigo wayarsa,ya qarasa yana duba mai kiran,ramla ce,dauke kanshi yayi kamar bai ganin kiran,yasan tatsuniyar gizo bata wuce ta qoqi,yasan bai wuce ta gaya masa cewa zata zo ba,abinda shi kuma baiso kenan,matsalar daya anni....baisan mai yasa ba....anni nada zuciyar mantuwa da yafiya,ta fishi sanin yaran su su waye suba wajensu suda iyayensu,amma tanayi kamar ta manta koma bata sani ba kwata kwata baki daya,suna zuwa su zauna mata suyu mata hidima,bayan yasan kowacce akwai manufarta cikin zuciya,shikam baijin zai manta ba kuma don bai yafe ba,a'ah..sam,amma iyaye daban suke,duk wani abu daya taba illata ko jirkita duniyar jin dadinsu baijin dan halak zai manta da hakan,dalili kenan daya sanya daga shi har haidar da salim ba wata qwaqwqwarar jituwa ko shaquwa a tsakaninsu da dukka yaran,baiga kuwa dalilin da zai saka ya zabesu a matsayin matan aure ba.
Kiran nata na katsewa kiran P.A dinshi ya shigo,a ladabce ya gaidashi shi kuma ya amsa a mutunce,nan yake sanar masa yau nefa tafiyar
"Wacce kenan haris?
" yallabai south africa din,na tura maka komai jiya ta email dinka da watsapp amma naga kaman baka gansu ba"kanshi ya dafe yana ambatar sunan Allah,shaf ya manta baki daya,don har yau yana da agender tare asma'u a capterian makarantarsu,amma dole ya aje komao saboda tafiyar nada muhimmanci
"Qarfe nawa ne tafiyar?"
"Jirgin qarfe daya ne sir"
"Is ok....ba damuwa" ya fadi yana katse wayar.
A nutse ya shirya cikin qananun kaya da sukai matuqar fidda sigarsa,sun masa kyau sosai,slippers ya saka ya fito izuwa sashin anninsa.
Ko ina agyare yake tsaf yana fidda qamshin turaren wuta na icce tamkar ba safiya ba,manyan abubuwa da yake jinjinawa anninsa da shi kenan,yake ganin da wuya ya samu mace wadda keda kaso daya cikin ukun halayenta,tsanani ko wuya,samu da talauci basu taba sanya annin nashi qazanta ba dai dai da qwayar zarra.
Tamkar ba safiya ba haka falon yake,kai baka ce ana zama cikinsa ba,dakinta ya wuce kai tsaye,a falonta dake manne da dakin gadonta ya sameta,wanda ita da iyalinta kawai ke zama a can,tsaf ya sameta kamar kullum,sanye da atamfar super riga da zani plain,dinkin jikinta yayi dai dai da shekarunta ya kuma yi mata kyau sosai,hannunta riqe da cup na tea na tangaran tana shan dafaffen shayin na'a na'a,yayin da daya hannun nata ke riqe da casbaha tana ja,qamshin falon nata daban da wanda ya baro,cikin fara'a ta aje kofin hannunta a gefe tana masa maraba da zuwa,cike da qauna ya isa gefanta ya zauna gabanta yana lanqwashe qafafunsa
"Barka da safiya anni...."
"Barka kadai muhammadu.....mun tashi lpy?"
"Lafiya lau,ya qarfin jiki?"
"Mun godewa Allah"
"To Allah ya qara lafiya da tsahon kwana mai amfani"
"Amin don isar annabi da alqur'ani....hala yau ba zaka fita bane"
"Zan fita anni....amma sai wajen azahar haka...inasu haidar ne?"
"Salim dai bai jima da ficewa motsa jiki ba,haidar kuwa kasan yana can yana bacci" sumarshi ya shafa sannan yace
"Mtswee....ya kamata na maidasu kamfani hakanan anni...zaman hutun ya isa haka"
"Ya kamata kam...nima ina shirin tuna maka....".
Amal ce tayi sallama ta shigo falon cikin dinkin doguwar rigar atamfa,tayi kwalliya a fuskarta tamkar ba safiya ba,ta laqanci khalipha sosai,me yakeso meye baya so,kanta a qasa cikin nuna yanayin jin kunya ta qaraso,khalipha ta soma gaidawa wanda hakan sam bai masa ba sannan ta gaida anni,jima kadan tace
" me xaka ci ya khalipha"son samu yace babu komai,amma annin ta hanashi hakan,ko baya sha'awa tace ya karba,don kada ya sosa ran dan uwanshi musulmi yaga kaman ya gwasaleshi
"Bani tea mara madara"
"Kawai?" Ta tambaya cikin salo,kai ya kada mata,sai ta miqe ta fice
"Muhammadu ya maganar da mukayi abincin da za'a kai gidan kawunka?"kai ya kada idanunsa na kallon qasa yace
"Anni....anni keta daban ce....kin manta komai kenan?" Murmushi tayi mai dauke da ma'anoni da dama sannan tace
"Muhammadu...duk wanda Allah ya doraka a kanshi ka riga ka fishi kenan har abada baida yadda zaiyi....sannan rama alkhairi gamai cuta ba illa ne ba.....baida amfani a lokacin daka tserewa wani abu ka dinga qoqari da fadi tashin tunawa da shi,da kuma maida hannun agogo baya...rayuwa idan ta wuce ta wuce kenan har abada,ka kalli gaba...ka kumayi qoqarin gina gaban...ka manta baya...zuciya mai yafiya ita Allah yakeso yake maraba da ita,zuciya mai manta sharri,zuciyar dake manta alkhairi itace abar neman tsari,koda yaushe ka zama mai manta sharri,mai saka cuta da alkhairi ina fata ka fahimta"
"Na fahimta anni....madalla da samun uwa irinki...koda yaushe ina godewa Allah daya bamu ke a matsayin uwa....dai dai da rana daya baki taba umartarmu da yin wani abu ba dai dai ba komai tsanani komai wuya"ya fadi yana gyada kai
"Burin uwa ta gari muhammadu ko yaushe ta dora diyanta kan tafarkin tsira duniya da lahira"
"Haka ne....yau za'a kai in sha Allahu,zan baiwa haidar ya kai masa"
"Allah ya albarkaceka kai da 'yan uwanka duniya da lahira....ya jiqan mahaifinku"
"Amin summa amin anni",ya jima suna hira shida ita har haidar da salim suka shigo suka samesu a haka,baibar wajenta ba sai da sha daya na safiya tayi,yana matuqar jin dadin zama da mahaifiyar tasa,macace mai hikima dattako da sanin ya kamata,idan ka zauna da ita ko yaya saika amfana ko ka qaru da wani abu mai muhimmanci da baka sanshi ba.
A dan gurguje ya shirya cikin shigar suits,wanda kallo daya ya isar sanar maka da awanne aji take,yana cikin gyara tie din wuyanshi gaban madubi idanunsa suka sauka kan vivo dinshi dake aje gefan madubi,murmushi ya subuce masa sanda ya tuna agender dinsu da haduwarsu ta qarshe da asma'u,dariyar data dinga masa shida wayar tana masa kallon wani shashasha gaula,tuni ya gama gane inda ta dosa,saidai game din da suke bugawa shida ita hakanan ke burgeshi tare da bashi qawa,yakan raya a ransa tunda har take tsaiwa suyi magana koda ba mai dadi bace watan wata rana zata saurareshi,zata fuskance shi,za kuma ta zama tashi,hakanan yayi sha'awar kiranta,sai ya kunna wayar yana ci gaba da shiryawa tare da jiran ta kawo.
Yana takawa harabar gidan wayar na ringing alamun tana shiga bayan yayi sallama da anni,yaranshi suka bude qofar motocin suna jiran qarasowarshi,ganin haka ya dakata daga dan nesa kadan,ta daga wayar saidai bata amsa ba,hakan ke alamta ta gane cewa shine
"Assalamu alaikum ranki ya dade"
"Ya akayi yaron oga?" Ta fada cikin isgili tana dariya dariya,baki daya ta daukeshi kaman wani abun wasa a gareta,don tasan cewa babu hadin kifi da kaska,babu abinda ya hada kashi da fura,sam tafiyarsu ba daya bace,hanyar jirgi, mota bata isa tabi ba,murmushi ya saki,kafin yace komai tace
"Naga alama kai kam da gaske kake.....tunda har haka ne....kazo ka sameni ina son ganinka" sosai maganar ta bashi mamaki,saidai baiji komai ba,cikin salo yace da ita
"To babu damuwa,saidai yanzu haka oga ya aikeni ne,ya turani wani waje,aqalla zanyi sati biyu haka,idan na dawo zan iya zuwa?"
"Baka da case" tace da shi tana katse wayar,kashe wayar yayi baki daya yana dan nazari,murmushi yake kadan kadan,daya daga cikin yaranshi nazir ya qaraso ya amsa ya mata waje.