Sashe 38
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Qarfe biyar na yammaci yana zaune falon daddyn cikin shigar yadi wanda aka fi kira da mamar ruwan bula mai haske,cikin mutunta juna suka gaisa shi da daddyn,ya dan bawa khaliphan space ya kurbi lemo duk da bamai yawa ya sha ba sannan yace
"Malam muhammadu....ya gida ya hidimomi" yana dan shafar kansa yace
"Alhmdlh daddy komai lafiya" zamanshi ya gyara bayan yayi gyaran murya
"Nasan zaka yi mamakin kiran ka da nayi ko"
"Hakane" khalipha ya amsa
"Ba wani abu bane babba yasa na kira ka ba....ammm kasan cewa tun ba yau ba na daukeka kaman matsayin d'a a gareni...to haka yake har yanzu,musamman da zaka auri diya ta...inaso nayi maka kyauta ne kamar yadda mahaifi zai yiwa dansa" ya saurara da maganar yana ciro wasu kudi daga gefan inda yake zaune,rafa ce ta 'yan dubu dubu guda goma ya aje a gaban khaliphan
"Ga wannan.....ka karba kayi amfani da su....duk wani abu da kasan baka samu ka qarasa ba kayi da sh,ka gaya muhallinku da dan abinda zakuci" can qasan xuciyarsa qina da mutuncin daddyn yake sake gani,tabbas ya kai maqura wajen nuna talaucinsa,hakan kuma bai sanya daddyn kai tsaye yace bazai bashi aure ba,saidai kamar yana son taimaka masa ne a fakaice ba tare daya furta ba,yasan mai yiwuwa labarin gidan aka zo aka bashi.....ko kuma ita ayshan talaucin taga ya mata yawa ta soma kokwanto?,kaman daddy yasan tunanin da yake yace da shi
"Tunanin me kakeyi?....kar kayi shakka ko kokwanton karba...babu wanda yasan na baka wannan kudin ko munyi maganar da kai,daga ni saikai sai Allahn daya haliccemu,karka damu ni na baka ba tambaya kayi ba,kuma har abada qimarka na nan a ido na" boyayyar ajiyat zuciya ya saki sannan yace
"Na gode na gode daddy qwarai da karamcinka na batun yau ba,Allah ya saka maka da mafificin alkhairinsa...amma daddy... Am sorry to say bazan iya karbar wadan nan kudaden ba,zanyi dukkan abinda ya dace iyakacin iyawata da yardar Allah daga iya abinda Allah ya horemin....don Allah kar kace saina karba daddy..." Kai yake gyadawa cike da mamaki da alfahari da wadatar zuci irin ta khaliphan wadda ya santa ba tun yau ba,lallai akwai wadatar zuci mai yawa tattare da shi,hakanan daddyn ya sanya hannu ya janye kudin yana cewa
"Shikenan...Allah ya taimaka yayi jagora....yayi albarka a zamanku"
"Amin ya Allah...na gode daddy" ya fada yana miqewa sukai sallama,yayin da daddy ya bishi da kallo,har ga Allah yaso ace ya karbi kudin ko muhallin da ayshan zata zauna ya gyara musu,saboda yayi yaqinin mutumin da bai karbi kudi ba ko gida ya bashi bazai karba ba,yaso ace ya karbi kudin ma sai yayi dabarar da zai bashi gida kudin yayi wata sabgar da ita,ajiyar zuciya yayi cikin zuciyarsa yana jin bari qurar bikin auren ta lafa dole ya inganta rayuwarsu bazai qyalesu a haka ba.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Saura sati daya bikin a yadda aka tsara aliya tazo ta tasata a gaba zasu je gidansu za'a soma mata gyaran jiki
"Don Allah sashin ki bar wannan zancan,meye wani gyaran jiki don Allah?....ni kunya ma kike bani wallahi"
"Kya gama jin kunyarki ki miqe mu tafi...."
"Don Allah sashen ki barni...."
"Idan kika sake wata maganar Allah ni dake ne...ki shirya kawai" hakanan ta miqe ta shiga bayi wanka ba don tana so ba.
Tana shiryawa aliya na mata mitar tana maida kanta koma baya,har sai da ayshan ta juyo yana dan bata fuska a shagwabe kaman qaramar yarinya,wanda ta riga data saba kusan dabi'arta haka lokaci zuwa lokaci
"To kuma don Allah sashin ba ya riga ya wuce ba gashi ina shiryawa...."
"Oho dai...ina gaya miki ne donma gobe kar kice zakimin musu....don sati za'ayi ana yi"
"Haba kaman wata kaya"
"Whatever...." Aliya ta fada tana watsa hannu.
Tsaf ta shirya ta saka hijabinta sannan suka fito,ta shiga dakin mummy ta sanar mata
"Saikin dawo" kawai ta fadi ba tare data damu da yaya abun zai gudana ko waye zai biya ba.
Suna harabar gidan zasu fice khalipha ya fito daga wajen daddy,zuba ido aliya tayi taga reaction na kowannensu,wucewa ayshan tayi kamar zatayi da sauri aliya ta damqi hannunta ta tsaidata,dai dai sanda khaliphan ya qaraso wajen,duk da yana dan gaggawa ya wuce saboda ya baro baqi a tahir amma saiya rage saurinsa sanda ya iso wajensu
"Ango kasha qamshi..." Aliya ta fada cikin salom tsokana,ya fahimci tana da sauqin kai da barkwanci,hakan ya sanya yayi murmushi
"Qawar amarya...ina zaku haka?"
"Gyaran jiki....da qyar na jajibo wannan amaryar taka" ta fada tana yima aysha da kanta ke qasa dariya
"Wai haka...?" Ya tambaya yana dan kallonta a fakaice
"Ina yini" ta gaisheshi a maimakon bashi amsa,ya fuskanci tana da hanyoyi da dama da take guntule zance idan bata son tsawaitarsa,shima din yana da abinyi hakan ya sanya ya kawo qarshen tsaiwar tasu
"Gashi kuma yayan naki gurgu ne babu abun hawa da.na kaiku"
"Babu komai ango....zamu qarasa a napep babu nisa daga nan" hannunsa ya sanya cikin aljihun wandonshi ya soma zaro kudi,cikin hanzari ya maidasu bayan ya duba yawansu,Allah yasa basu gani ba
Daya aljihun ya sake saka hannunsa,'yan dari biyar biyar ne hade da 'yan dari bibbiyu,baisan adadinsu ba,yana son ya qirga nawa ne amma ya kasa kasancewar bai saba hakan ba,miqa musu yayi
"Ga wannan kyayi wani abu da shi.....saidai fa haquri angon bashi da komai talaka ne" dariya aliya tayi ta sanya hannu zata amsa,ta daya bangaren aysha ta riqe hannunta,saidai bata kula da ta amsa din tana cewa
"Ba komai...Allah ya amfana wannan din"
"Amin...." Ya fada yana yabawa nagartar qawancen aliyan da aysha.
Shi ya soma yin gaba,aysha ta dubi aliya
"Me yasa zaki karba aliya....yanzun haka kudinsa fa kenan?" Murmushi ya saki sanda ya jiyo abinda ayshan ke fada,wani lokaci halayyarta na masa kamanceceniya da halayyar hajar....wata halitta mafi soyuwa a garesu da bazasu taba mantawa da ita ba,kusan yanayinsu da halayyarsu na gogayya da juna,da wannan tunani ya qarasa ficewa daga gidan ba tare daya ji qarshen muhawarar tasu ba.
"To meye don na karba din.....ya kamata ko yaya fa yasan zaiyi aure ne,za'a bashi mace kuma budurwa,bawai ya aureki kaman an bashi sadaka ba" kai aysha ta kada ta soma takawa sai aliyan tabi bayanta
"Har kullum aliya bana son ki dinga sani ina jin ni dinma kamar kowa nake bayan ba hakan yake ba"
"Ni kuma na gaji da maimaita miki wannan karatun na kema kamar kowa kike,da dama ma kin fisu a wajen Allah"kanta itama take girgizawa,tausayin aysha na rinjayar zuciyarta,ko sai yaushe zata yarda itama 'yace kamar kowa?,sai yaushe zata sake tayi rayuwa yadda kowacce mace take?,oho...Allah masani...wannan itace amsar da aliya ta baiwa kanta,haka suka dinga tafiya tamkar kurame.
Ganin ayshan nason motso damuwarta wadda zata iya shafar wuninsu na yau,sai aliya ta qara sauri ta jera da ita tana sako mata zancan makaranta da yadda result dinsu ya kaya,hakan sai ya sanyayar da zuciyar aysha,suka ci gaba da tattaunawa,har ta zabi su taka a qafa tunda wajen ba wani nisa bane can da shi,aliya bata musa ba ta biye mata suka dinga takawa a qasa suna hirarsu
"waccan 'yar qarunar naga kaman bata wani damu da carry overn data samu ba ta aure take....naji labarin ta samu c.o ko?duk da ba'a gaya min ba don kada nayi sharhi...to sai nayi,zancan duniya kuma bai buya" Aliya ta fada tana qunshe dariyarta,don ita hakan yayi mata dadi,ko banza asma'u zatasan da cewa duk inda kakai ga zama wani a duniya dole kayi lacking wani abu a rayuwarka ko kai waye.
"Malam muhammadu....ya gida ya hidimomi" yana dan shafar kansa yace
"Alhmdlh daddy komai lafiya" zamanshi ya gyara bayan yayi gyaran murya
"Nasan zaka yi mamakin kiran ka da nayi ko"
"Hakane" khalipha ya amsa
"Ba wani abu bane babba yasa na kira ka ba....ammm kasan cewa tun ba yau ba na daukeka kaman matsayin d'a a gareni...to haka yake har yanzu,musamman da zaka auri diya ta...inaso nayi maka kyauta ne kamar yadda mahaifi zai yiwa dansa" ya saurara da maganar yana ciro wasu kudi daga gefan inda yake zaune,rafa ce ta 'yan dubu dubu guda goma ya aje a gaban khaliphan
"Ga wannan.....ka karba kayi amfani da su....duk wani abu da kasan baka samu ka qarasa ba kayi da sh,ka gaya muhallinku da dan abinda zakuci" can qasan xuciyarsa qina da mutuncin daddyn yake sake gani,tabbas ya kai maqura wajen nuna talaucinsa,hakan kuma bai sanya daddyn kai tsaye yace bazai bashi aure ba,saidai kamar yana son taimaka masa ne a fakaice ba tare daya furta ba,yasan mai yiwuwa labarin gidan aka zo aka bashi.....ko kuma ita ayshan talaucin taga ya mata yawa ta soma kokwanto?,kaman daddy yasan tunanin da yake yace da shi
"Tunanin me kakeyi?....kar kayi shakka ko kokwanton karba...babu wanda yasan na baka wannan kudin ko munyi maganar da kai,daga ni saikai sai Allahn daya haliccemu,karka damu ni na baka ba tambaya kayi ba,kuma har abada qimarka na nan a ido na" boyayyar ajiyat zuciya ya saki sannan yace
"Na gode na gode daddy qwarai da karamcinka na batun yau ba,Allah ya saka maka da mafificin alkhairinsa...amma daddy... Am sorry to say bazan iya karbar wadan nan kudaden ba,zanyi dukkan abinda ya dace iyakacin iyawata da yardar Allah daga iya abinda Allah ya horemin....don Allah kar kace saina karba daddy..." Kai yake gyadawa cike da mamaki da alfahari da wadatar zuci irin ta khaliphan wadda ya santa ba tun yau ba,lallai akwai wadatar zuci mai yawa tattare da shi,hakanan daddyn ya sanya hannu ya janye kudin yana cewa
"Shikenan...Allah ya taimaka yayi jagora....yayi albarka a zamanku"
"Amin ya Allah...na gode daddy" ya fada yana miqewa sukai sallama,yayin da daddy ya bishi da kallo,har ga Allah yaso ace ya karbi kudin ko muhallin da ayshan zata zauna ya gyara musu,saboda yayi yaqinin mutumin da bai karbi kudi ba ko gida ya bashi bazai karba ba,yaso ace ya karbi kudin ma sai yayi dabarar da zai bashi gida kudin yayi wata sabgar da ita,ajiyar zuciya yayi cikin zuciyarsa yana jin bari qurar bikin auren ta lafa dole ya inganta rayuwarsu bazai qyalesu a haka ba.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Saura sati daya bikin a yadda aka tsara aliya tazo ta tasata a gaba zasu je gidansu za'a soma mata gyaran jiki
"Don Allah sashin ki bar wannan zancan,meye wani gyaran jiki don Allah?....ni kunya ma kike bani wallahi"
"Kya gama jin kunyarki ki miqe mu tafi...."
"Don Allah sashen ki barni...."
"Idan kika sake wata maganar Allah ni dake ne...ki shirya kawai" hakanan ta miqe ta shiga bayi wanka ba don tana so ba.
Tana shiryawa aliya na mata mitar tana maida kanta koma baya,har sai da ayshan ta juyo yana dan bata fuska a shagwabe kaman qaramar yarinya,wanda ta riga data saba kusan dabi'arta haka lokaci zuwa lokaci
"To kuma don Allah sashin ba ya riga ya wuce ba gashi ina shiryawa...."
"Oho dai...ina gaya miki ne donma gobe kar kice zakimin musu....don sati za'ayi ana yi"
"Haba kaman wata kaya"
"Whatever...." Aliya ta fada tana watsa hannu.
Tsaf ta shirya ta saka hijabinta sannan suka fito,ta shiga dakin mummy ta sanar mata
"Saikin dawo" kawai ta fadi ba tare data damu da yaya abun zai gudana ko waye zai biya ba.
Suna harabar gidan zasu fice khalipha ya fito daga wajen daddy,zuba ido aliya tayi taga reaction na kowannensu,wucewa ayshan tayi kamar zatayi da sauri aliya ta damqi hannunta ta tsaidata,dai dai sanda khaliphan ya qaraso wajen,duk da yana dan gaggawa ya wuce saboda ya baro baqi a tahir amma saiya rage saurinsa sanda ya iso wajensu
"Ango kasha qamshi..." Aliya ta fada cikin salom tsokana,ya fahimci tana da sauqin kai da barkwanci,hakan ya sanya yayi murmushi
"Qawar amarya...ina zaku haka?"
"Gyaran jiki....da qyar na jajibo wannan amaryar taka" ta fada tana yima aysha da kanta ke qasa dariya
"Wai haka...?" Ya tambaya yana dan kallonta a fakaice
"Ina yini" ta gaisheshi a maimakon bashi amsa,ya fuskanci tana da hanyoyi da dama da take guntule zance idan bata son tsawaitarsa,shima din yana da abinyi hakan ya sanya ya kawo qarshen tsaiwar tasu
"Gashi kuma yayan naki gurgu ne babu abun hawa da.na kaiku"
"Babu komai ango....zamu qarasa a napep babu nisa daga nan" hannunsa ya sanya cikin aljihun wandonshi ya soma zaro kudi,cikin hanzari ya maidasu bayan ya duba yawansu,Allah yasa basu gani ba
Daya aljihun ya sake saka hannunsa,'yan dari biyar biyar ne hade da 'yan dari bibbiyu,baisan adadinsu ba,yana son ya qirga nawa ne amma ya kasa kasancewar bai saba hakan ba,miqa musu yayi
"Ga wannan kyayi wani abu da shi.....saidai fa haquri angon bashi da komai talaka ne" dariya aliya tayi ta sanya hannu zata amsa,ta daya bangaren aysha ta riqe hannunta,saidai bata kula da ta amsa din tana cewa
"Ba komai...Allah ya amfana wannan din"
"Amin...." Ya fada yana yabawa nagartar qawancen aliyan da aysha.
Shi ya soma yin gaba,aysha ta dubi aliya
"Me yasa zaki karba aliya....yanzun haka kudinsa fa kenan?" Murmushi ya saki sanda ya jiyo abinda ayshan ke fada,wani lokaci halayyarta na masa kamanceceniya da halayyar hajar....wata halitta mafi soyuwa a garesu da bazasu taba mantawa da ita ba,kusan yanayinsu da halayyarsu na gogayya da juna,da wannan tunani ya qarasa ficewa daga gidan ba tare daya ji qarshen muhawarar tasu ba.
"To meye don na karba din.....ya kamata ko yaya fa yasan zaiyi aure ne,za'a bashi mace kuma budurwa,bawai ya aureki kaman an bashi sadaka ba" kai aysha ta kada ta soma takawa sai aliyan tabi bayanta
"Har kullum aliya bana son ki dinga sani ina jin ni dinma kamar kowa nake bayan ba hakan yake ba"
"Ni kuma na gaji da maimaita miki wannan karatun na kema kamar kowa kike,da dama ma kin fisu a wajen Allah"kanta itama take girgizawa,tausayin aysha na rinjayar zuciyarta,ko sai yaushe zata yarda itama 'yace kamar kowa?,sai yaushe zata sake tayi rayuwa yadda kowacce mace take?,oho...Allah masani...wannan itace amsar da aliya ta baiwa kanta,haka suka dinga tafiya tamkar kurame.
Ganin ayshan nason motso damuwarta wadda zata iya shafar wuninsu na yau,sai aliya ta qara sauri ta jera da ita tana sako mata zancan makaranta da yadda result dinsu ya kaya,hakan sai ya sanyayar da zuciyar aysha,suka ci gaba da tattaunawa,har ta zabi su taka a qafa tunda wajen ba wani nisa bane can da shi,aliya bata musa ba ta biye mata suka dinga takawa a qasa suna hirarsu
"waccan 'yar qarunar naga kaman bata wani damu da carry overn data samu ba ta aure take....naji labarin ta samu c.o ko?duk da ba'a gaya min ba don kada nayi sharhi...to sai nayi,zancan duniya kuma bai buya" Aliya ta fada tana qunshe dariyarta,don ita hakan yayi mata dadi,ko banza asma'u zatasan da cewa duk inda kakai ga zama wani a duniya dole kayi lacking wani abu a rayuwarka ko kai waye.