← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 114

Sashe 17

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Murmushi take bayan ta kashe wayar,babbar aminiyarta husna ta dubeta tana mata wani irin kallo
"Asma me kike nufi ne wai?,mutuncinki kikeson zubarwa kome?,mace irinki maisu hamid su hisham me zaki da wanda ke qarqashin gashin wani....haba asma" dariya ta saki tana duban husna
"Husna...husna...shi yasa nake sonki...tunaninmu daya,ra'ayunmu daya,saidai a wannan karon abinda na hasaso daban da naki,kinsan meke faruwa ne?" Ta fada tana gyara zamanta tare da fuskantar husna sosai
"Saikin fada" ta ambata tana duban asma'un sheqeqe
"Wannam guy din ya hadu tako ina....Allah ya masa baiwar kyau da qira....abu guda ya nakasheshi....bai mallaki hatimin da zai sanyashi mallakar zuciyata ba....amma kowanne mutum da ranarsa.....muhammad namiji ne da zaki shiga da shi kowanne waje da maza masu aji da jin su wasu ne ki kuma kankarowa kanki qima da mutunci....abu daya ne kawai,ki sama masa suttura ki bashi abun hawa duk sanda zai rakaki wani waje...." Kai husna take kadawa
"Maganarki haka take....amma asma'u,gani daya nayi masa naga kaman bazai biyu miki yadda kikeso,a ido kawai tsayayyen namiji ne,yana da wani irin kwarjini da cika ido,anya asma?" Dariya ta saki tana kada key din motarta dake hannunta
"Husnaaaa....kudi sune qarshen zance kin manta?" Murmushi ta saka tana gyada kai tare da gamsuwa da bayanan asma'u,ita kanta ya burgeta qwarai,saidai ba ajinsu bane shi saboda bai mallaki abinda za'a nuna shi ba.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶

Cikin sati biyun ya nemi duk wata hanya da zai dinga tuna mata da shi,batasan ya akai ba,batasan yadda ya samu number dinta ba,sai kiranshi da take samu babu qaqqautawa,bata iya wulaqanta mutum ba kaf rayuwarta,don itama bata saka kanta a lissafin mutane masu daraja ba,bugu da qari alfarma ya nema a wajenta,hakan ya sanya bata qin daga wayarshi koda na zata ce komai ba,ba zata iya cewa komai game da shi ba,don a yanzun zuciyarta tana jin kamar bata mutum ba,batajin zata karbi wani abu da ake kira soyayya,soyayyar da taje jin bata a duniyarmu,bata jin gaske ce,don bata taba dandanata ba bare ta adar da komai a cikinta.

🧣🧣 *DAURIN BOYE*🧣🧣

*NA*

*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*

HASKE WRITERS ASSO

(Home of expert and perfect writers)

12

Qarfe daya da rabi na rana suka fito daga babban meeting na duka ma'aikatan kamfanin nasa,kai tsaye shida motocinsa suka wuce katafaren gidan abinci na purple palace da yake cin abinci don suci abincin rana,tafiyar minti sha biyar ce tsakanin kamfanin nasu da wajen suka isa sukai parking,tuni nazir ya bude mishi qofa,yana shirin fitowa vivo dinsa dake can gefan set din da yake zaune ta hau qara,shaf ya mance da ita,ya waiwayo yana dubanta,yasan mutum daya ne zaya kira asma'u,ita dince,wayar ya daga ya kara a kunnensa
"Kana ta wajen ina?"ta fada kai tsaye ba tare data damu da yin sallama ba
"Ina wajen aiki"
"Ohk....kazo purple palace restaurant ka sameni" ta fadi kanta tsaye kaman wani yaronta sannan ta kashe wayar,wayar ya sauke daga kunnensa,daya daga cikin yaranshi ya kira da hannu,qarasowa yayi cikin girmamawa ya masa nuni daya matso,cikin kunne ya masa magana ta mintina,kai ya gyada ya wuce zuwa cikin wajen cin abinci,minti biyu ya dawo ya sanar masa da abinda ya aikashi yi,kai ya gyada,sake kiran daya daga cikin yaran nasa yayi ya sukai magana,cikin mintuna sai gashi ya dawo riqe da baqar leda ya bashi,ya amsa,sannan a nutse ya soma cire suits dinshi na saman guda biyu ya bar ta ciki,takalmin qafarshi ya sauya zuwa mai sauqin kudi bayan ya kira daya daga cikin yaran shi ya dauko masa cikin boot din daya daga cikin motocin nasu,eye glasses dinsa ya cire ya kashe wayoyinsa ya ajjiye ya dauki vivo din ya riqe a hannunsa hadi da cire agogon hannunsa shima ya aje sannan ya fito daga motar,da kallo suka bishi,suna yunqurin binsa ya tsaidasu
"Ku janye motocin nesa kadan da nan wajen,karku biyoni ina dawowa"
"Yes sir" dukkansu suka ce,a nutse suka janye motocin suka musu muhalli a wajen da zasu iya ganoshi.

Ita daya ce zaune kan teburin cin abincin tana danne dannen waya, tasha ado cikin gown ruwan bula,ta yane kanta da mayafi ruwan powder mai turuwa,fuskarta sanye da sun glasses daya kusa mamaye fuskarta,da sallama ya qarasa wajen,hannunsa guda zube a aljihunsa,dayan riqe da baqar ledar,kai ta daga tana amsa sallama,ya mata kyau a idanunta sosai,saidai har yanzu bata gaza ganin aibunsa ba
"Kin yini lafiya ranki ya dade"
"Lafiya lau....zauna magana zamuyi" ba musu yaja kujerar da hannu daya sannan ya zauna,ya hade yatsunsa waje daya ya zuba mata idanunsa bayan ya aje ledar a tsakaninsu,kafin wani a cikinsu yace komai daya daga cikin waitress din wajen ta qaraso riqe da purple din leda mai tambarin gidan cin abincin ta miqawa asma'u ta amsa
"Kana kusa kenan dama?"
"Eh....naje wani aike ne na oga nan kusa"
"Yayi yaron oga...."
"Ga wannan,naga ni a hanya ne na miki tsaraba" ya fada yana miqa mata ledar,janta tayi gabanta sannan ta bude,abinda ta gani ciki ya bata takaici fuska a yamutse ta dubeshi
"Meye wannan?"
"D'ata,yalo,guava"takaicin daya qumeta shi ya hanata magana
"dauki muje" ta fadi tana nuna masa ledar da ma'aikaciyar wajen ta kawo tana miqewa bayan ta masa nuni da ledar da aka kawo mata,dariya ce taso subuce masa,sai kawai ya dauki ledar ya bita.

Nasiru shi ya soma tahowa da sauri da niyyar amsar ledar hannusa bayan ya hango fitowarsu,cikin zafin nama ya sanya hannunshi ta baya ya dakatar da shi,hakan ya sanya suka tsaya cak suna kallonsu har suka isa motar asma'un,ta masa izinin ya shiga itama ta shiga sannan ta tada motar.

Shiru ne ya ratsa motar jin hakan ya sanyashi cewa
"Ina zamuje ne?,kar oga ya nemi ni fa"
"Karka sake kawo min irin wancan tarkacen...ko na maka kama da maicin irinsu?" Dasauri ya sauya yanayin fuskarsa ganin ta waiwayo inda yake zaune,ya ragewa fuskar tasa kwarjini da tsare gidan da yayi
"Kayan marmari ne fa"
"Irin naku na talakawa?" Ta fada kai tsaye,cik yaji kalmar ta caki zuciyarsa,an taba gaya masa makamanciyarta cikin wani yanayi can baya daya kasa barin ransa,shiru yayi ya lula wata tsohuwar duniya,hakan ya wanzar da shiru a tsakaninsu har suka iso inda suka niyyaci zuwa.

Qaton botique ne wanda da alamu ke nuna na manyan yara ne,kai tsaye wajen suturun maza ta nufa tana dubawa yana biye da ita,bata masa magana ba,ita da kanta ta dinga zabar t.shirt zuwa trousers masu matsakaitan kudi tana miqa masa hadi da cewa ya duba ya gani,dariya ya dinga yi shi kadai yana biye da ita,duk abinda ta miqo cewa kawai yake yayi,yana yi yana duba price din kowanne riga da wando,a qalla ya manta yaushe rabon daya saka kaya masu wannan farashin,shi yake zabar kayan da yake so da kanshi,saidai ba cikin ire iren wadan nan qananun batique din ba.

Kaya ne kala biyar takalmi qafa biyu,kai tsaye wajen biya suka nufa aka mata total ta cire ta biya,jimillar dubu ashirin,yana biye da ita da kayan har zuwa cikin mota,dubanshi tayi kafin tace
"Ka fara amfani da wadan nan,ranar juma'a ka zabi daya daga ciki ka sanya,zaka rakani wata dinner"
"Ayyah...kinsan oga baya barina inje nan da can,sannan ni kaina bana yawon dare" wani kallo tayi masa
"Ka hadu ta halittar da Allah ya maka,saidai ka kwafsa tako ina,yaushe zan iya zaman aure da kai tabdi" ta fada cikin zuciyarta,amma a fili sai tace
"Kaman kai kace baka son yawon dare...sometimes idan kana wani abun kaman baki karatu ba" ta fadi cikin mamaki,murmushi kawai yayi yana dauke kansa,itama bata sake magana ba ta tada motar tana wani tsare gida suka tafi,saidai tana wassafa yadda zata dinga shiga da shi ne manyan gurare,cikin abokai da sauran 'yan uwa ko don ta kankarowa kanta mutunci wajen abokan takun saqa

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶

Har qarfe shida na safe tana saman abun sallah bata koma baccinta ba,saboda breakfsat da zata shirya na asma'u.

Shida da minti goma ta nufi kitchen din,saidai yau sabanin ko yaushe tun kafin ta qarasa ta jiyo kwarafniya a kitchen din

Lauratu ta taras mai aikin mummy,a mutunce suka gaisa,akwai zaman mutunci da girmama juna tsakaninta da duka yan aikin gidan sabanin asma'u
"Yau kinyi sammako lauratu"
"Wallahi,alhaji ne yace amin magana,mu sama masa tuwon acca da safen shi zaici" murmushi aysha tayi,tasan daddy yana sane baisa an gaya mata ba,tasan yayi hakanne don kawai ta huta
"Idan kin gama hada komai ki barmin zan dafa" aysha tace da lauratu
"Kai...aikin bazai miki yawa ba....bakya gajiya da girki?"
"Girkin daddy ne fa lauratu ko kin manta"
"Af....anyi haka fa,na manta ba'a shiga tsakaninku" dariya sukai baki daya kowa ya kama nashi aikin.

Na asma'u ta fara kaiwa dining saboda taji yau zata fita makaranta da wuri,tun sanda asma'u ta soma cin abincin asma'u taqi abincin duka masu aikin gidan,sautari ayshan itake girkin ta dama na gidan wasu lokutan,bata taba gajiya ko nuna damuwarta ba

Zuwa goma ta gama na daddy shima,ta shirya komai tsaf ta diba zuwa saman dining ta shirya a can,tana niyyar barin wajen taji shigowarsa

A ladabce ta qarasa ta gaidashi ya amsa mata sannan ta gaida mummy sa'adah da suka fito tare
"Ke suka barwa girkin indo?" Cewar daddy yana murmushi,murmushin itama kawai tayi
"Sannu indo bakya gajiya,Allah yayi albarka kinji"
"Amin daddy" ta fada cikin jin dadi,don har ga Allah tana jin dadi idan ya sanya mata albarka,tana jin albarkarsa tamkar ta mahaifinta da ba zata iya tuna yaushe da yaushe ya saka mata ita ba.

Tana tsaka da shiryawa bayan tayi wanka wayarta ta dauki ringing,a nutse ta duba sai taga ahmad ne,ta danji dadi kadan tunda ko babu komai zai debe mata kewa,wata rayuwa ta taso ta kadaici tun da can zuwa yanzu,duk da cewa gidansu na can cike yake da jama'a amma ita kusan ita daya take rayuwarta,ba qawa ba aboki ba masoyi,sai daga baya qawa qwaya tak ta shigo rayuwarta.
Chapter 17 · 0% Book details