Sashe 82
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Saida khalipha ya gama bayaninsa kaf sannan alhj idris yace
"To nidai bana jin akwai abinda zan iyayi gaskiya,don tuni na miqawa yakubu haqqin kula da wajen,baiga dacewar ya daukeka ba shi yasa bai daukeka ba,saboda haka sai kayi haquri" shuru khalipha yayi ba tare da yace komai ba
"Ka tashi kaje" ya fada yana nuna masa hanya,tsam ya miqe ya fice daga falon,yana gab da ficewa a gidan yarinyar gidan daya taras dasu a falo ita da mahaifiyarta ta qwalo masa kira,tsayawa yayi cak
"Abba yace kazo" kaman baxai koma din ba,amma yadda yarinyar ta tsaya tana kallonshi yasa yajuya yabi bayanta.
"Binta tace a barka,basu damai share share ya tafi jinyar babanshi,idan kanaso zaka iya karbar aikin nasa kafi ya dawo sai a san yadda za'ayi,za'a dinga baka albashi a wata dubu biyar,sai abincin rana dana dare amma fa ba kullum ba zaka yi?" Kai ya jinjina saboda kudin koda baikai hakan ba zai iyayi,matuqar zai samu abinda zai kaiwa 'yan uwa da mahaifiyarsa.
Sanda ya koma gida yake baiwa anni labarin yadda sukayi taji dadi koba komai zai samu abinda zai riqesu,saidai kuma wani bangare na zuciyarta suya yake mata sosai,ace yau idriss shi zai dauki dan sa'id boyi boyin gida?,sa'id a sanda yana raye numfashi ne kawai baiyi musu ba,shine cinsu shansu suturarsu da duk wani kasuwanci da sukeyi,uwa uba sune suka kwashe duk wata dukiya ta sa'id din da sunan bashin banki yaci,ba ita ba hatta da khalipha sun sani sa'id din tunkan yayi bunqasar da yayi mutum ne mai tsoron bashi koda na naira biyar ne kuwa,balle har yakai kanshi banki ya karbi dukiyarsu.
Aikin da akace khaliphan zaiyu sai yatadda yaci uban hakan,gida ne mai matuqar girma wanda mahaifinsa ne ya ginawa idriss din dab da zai rasu mai dauke da dakuna da sassa sassa ginin zamani,shi zai share gidan komai girmansa,idan ta kama ma har dakin ibrahim dansa namiji tilo da yake gwadawa gata khaliphan ne zai shiga ya share,wani lokaci hatta da falon gidan hajiya binta saita hada masa da shi,baya ga haka idan i rahim ya bushi iska saiya hado masa kayansa yace ya wanke masa,haka aike lokuta mafiya yawa shike musu,dukka wadan nan hidimomin cikin kudinsa ne,bawai wani albashi na daban aka qara masa ba.
A qalla khalipha sai daya shekara uku yana wannan bautar gidan yayan mahaifinsa,cikin gidan da mahaifin nasa shiya gina masa shi,a qafa yake zuwa a qafa yake dawowa,aninci kuwa sai a debi kusan kwana hudu ba'a bashi na rana ba bare dare,duk ranar da aka bashin kuwa bawai ci yake ba,yana hadewa ne idan ya tashi tafiya ya kaiwa qannensa,wani lokaci idan yaga aikinnyi akan hanya yakan tsaya ya karba yayi kafin ya qarasa gida dinsu samu abun batarwa kafin wata ya cika a bashi albashinsa,don shi kanshi albashin idan alhj idris yaso sai wani watan ya shiga yayinkwanaki goma sha bai bashi ba,ya dinga kuma qananun maganganu shi daya yana fadin dadin ya yiwa khalipha yawa,ga cinyarwa gashi ana biyanshi kudi?,shi ai ya cancanci ma ayi masa jinjina sabida yayi abinda dukka sauran 'yan uwanshi suka kasa,khalipha bai taba daga kai ya dubeshi koya tanka mishi ba,yakanyi qoqarin danne fushinsa sarai duk sanda wani abu mara dadi ya faru,suna cin albarkacin anni data roqeshi kada ya yarda ko sau daya ya biyesu ayi wani abu mara dadi,dalilin barin gidan ya fara samo asali ne daga sanda jama'ar gidan haj binta da ibrahim suka soma qorafin ana musu dauke dauke,kusan kullum Allah ne dakullum sai anyi cigiyar an nemi abu an rasa.
Rabon za'ayi ranar da khalipha ya shiga dakin dakin ibrahim yi masa shara,khalipha tun asali mutum me maison ado da qamshi,kwalliya na burgeshi qwarai,dalili daya sanya koya ya samu kudi bai rasa siyiwa hajar abun kwalliya na mata koda jambaki ne kuwa dan naira hamsin,koda shi bai saka ba ita ta saka,to ibrahim ba laifi akwai qwalisa da ado,duk sanda yayi kwalliya khalioha kan kalleshi,yana tuna sanda mahaifinsu keda rai,duk juma'ar duniya sababbin kaya suke sakawa,wani lokacima anko suke da babanshi,akwai wani turare da ibrahim din ke amfani dashi,kalipha na matuqar son qamshin turaren,ranar yaje yi masa shara saiya dauka ya fesa sau daya a jikinsa,yana shirin ajewa ibrahim ya shigo dakin,nan ya soma cuccusawa ma khalipha ashar yana fadin ashe shine barawon gidansu,ya gaya mishi don ubanshi mai ya dauka
"Babu abinda na dauka maka sai turare dana fesa,wanda shima nasan nayi kuskure kuma kayi haquri don Allah" khaliphan ya fada tunda yasan laifinsa ne,kafewa ibrahim yayi yace bai yarda ba sai khalipha ya tube ya dubashi
"Bazqiyiwu ba tunda na rantse maka ban dauka ba ban dauka ba,dana dauka din kai tsaye zan gaya maka na dauka,don nafi tsorin mahaliccina fiye dakai"
"Ni kake gayawa ba tsorona kake ba,kayimin sata ka dinga gayamin baka tsoro na?" Saifa ibrahim ya rufe khalipha da duka,a sannan ya girmeshi hakanan khaliphan ya rame ibrahim ya fushi gabaran jiki,hakan shi ya baiwa ubrahim damar yiwa khalipha duka bana wasa ba,ya gwara kanshi da bango sosai wanda yayi sanadiyyar sunewarshi,bai farfado ba sai a asibiti,tunda ya samu sauqi aka sallemshi ya koma gida,duk sanda ya tuno da abin yana qona mishi rai,sharrin sata abu ne ba qarami ba,amma anni tace ya barsu da Allah,ta kuma yi masa fadan fesa masa turaren da yayi,ta gaya masa shine silar komai,dabai fesa ba da duk hakan bata faru ba,wannan shine silar abinda ya gadarwa khalipha cuwon kai mai tsanani da yake shan wuya duk sanda ya tasarmasa har kwanan gobe.
sanda abun ya faru saura kwana biyu a biyashi albashinsa,kwana biyu na cika saiga kawu idris da albashin khaliphan,sunyi mamakin ganinshi don sunsan bata yadda za'ayi ya biyoshi da albashinsa,ilai kuwa bayan ya miqa albashin sai ya sassauta murya cikin murmushi,a lokacin khalipha na dakin annin yana kwance don bai gama murmurewa ba
"Wata magana nazo miki da ita mai muhimmanci aisha,wadda idan har kika amince da ita ni dake gaba daya kowa zai amfana"
"Inajinka,Allah yasa alkhairi" ta fada tana dubanshi a darare don ita har yanzu bata amince da zuwanshi ba
"Nace ba....me zai hana muyi aure ni dake,idan yaso saiki kwaso 'ya'yanki naci gaba da kuka dasu,'ya'yan sa'idu ai 'ya'yana ne" a zabure khalipha dake kwance ya miqe,cikin azama ya tashi tsaye ya fito falon
"Tashi ka fitar mana daga gida" kallonshi idris yayi
"Meyw haka khalipha?"
"Nace tashi ka fitar mana daga gida maciyin amana kawai,Allah ya tsare anni da aurenka har abada wallahi tafi qarfinka"
"Me kake haka khalipha?" Anni ta fada tana qoqarin tsawatar masa gajin yadda yataso haiqan kaman zai daki kawu idris,sam bai saurari zancan anni ba bai saurarawa kawu idris ba sai daya danganashi da gate din gidan sannan ya dawo,idanunshi kamar garwashin wuta haka suk a kada sukayi jajur,haka kawai ya kasa zaune ya kasa tsaye saboda bacin rai ya dinga kai kawo
"Anni,duk randa mutumin nan ya sake dawowa gidan nan saina nakasta shi" haka ya dinga fada saida annin ta tsawatar masa
"ka shiga hankalinka mana khalipha,ni din bansan me nake ba koko yaya?,idris ne fa na sanshi na kuma san halinshi da manufofinsa kaf tun kafin a haifeka" da qyar anni ta iya control dinsa,haka yake bai iya fushi ba,ya kuma qaro zafin zuciya sanadiyyar tsangwama da rashin kirki da azabar da suka dinga gwada masa da 'yan uwanshi.
Tun daga ranar bai sake waiwayarsu ba kamar sauran,su kadai suke rayuwarsu,su kadai suke fadi tashinsu,su kade suke cin wahalarsu,wataran subsamu wataran suyi kwana biyu uku basu samu ba.
Wata biyu da zuwan kawu idris da wannan maganar hajar ta soma wani irin ciwon ciki mai tsanani,idan ta fara wani lokaci har suma take,anyi gwaje gwaje ya tabbatar da appendixs ne kuma saidai ayi aiki,kasancewar babu babu kuma mai basu haka suka haqura suka zubawa sarautar Allah ido,haka hajar ta dinga fama,yau lafiya gobe babu,idan ciwon ya tasar mata kamar ba zata kai ba,ba wanda yasan halin da suke ciki ballantana ya nuna kulawarshi.
Idan ajali yayi kira ko babu ciwo aje,safiyar wata laraba ciwon ya tasarwa hajar sosai,a lokacin khalipha ya fita wajen nema musu abinda zasuci,don wayewar garin basu tashi da qwayar hatsi da zasu iya sanyawa a bakinsu ba,haidar ne ya dinga yawon nemanshi duk wajen da yasan za'a sameshi,da qyar ya samoshi wajen wani fili da ake kwashe bolar ciki za'a soma gini,khalipha na cikin masu kwashe sharar,a gigice ya tafi wajen ogan nasu ya masa bayanin halin da ake ciki,ya lissafa iya kai nawa khaliphan yayi aka biyashi,ya tausaya masa har qari yayi masa akai suka taho gida tare da haidar,kafin su qarasa tuni hajar ta galabaita ta fita hayyacinta,abun ya tsoratar da khalipha sosai don bata taba irin haka ba duk ciwon da take,nan suka kwasheta sai asibiti,a canma dan abunuwan da suka saya gwaje gwaje da sauransu duk sun cinye dan kudin daya riqo,duk da cewa asibitin gwamnati ne amma sunan a baki ne,kusan komai talaka shike ma kansa,duk abubuwan daya kamata gwamantin tayi ta saki.
Daga bisani likitan ya shaida musu cewa tilas a gaggauta yi mata aiki nan da awa ashirin da hudu,idan ba haka ba komai zai iya faruwa da ita.
"To nidai bana jin akwai abinda zan iyayi gaskiya,don tuni na miqawa yakubu haqqin kula da wajen,baiga dacewar ya daukeka ba shi yasa bai daukeka ba,saboda haka sai kayi haquri" shuru khalipha yayi ba tare da yace komai ba
"Ka tashi kaje" ya fada yana nuna masa hanya,tsam ya miqe ya fice daga falon,yana gab da ficewa a gidan yarinyar gidan daya taras dasu a falo ita da mahaifiyarta ta qwalo masa kira,tsayawa yayi cak
"Abba yace kazo" kaman baxai koma din ba,amma yadda yarinyar ta tsaya tana kallonshi yasa yajuya yabi bayanta.
"Binta tace a barka,basu damai share share ya tafi jinyar babanshi,idan kanaso zaka iya karbar aikin nasa kafi ya dawo sai a san yadda za'ayi,za'a dinga baka albashi a wata dubu biyar,sai abincin rana dana dare amma fa ba kullum ba zaka yi?" Kai ya jinjina saboda kudin koda baikai hakan ba zai iyayi,matuqar zai samu abinda zai kaiwa 'yan uwa da mahaifiyarsa.
Sanda ya koma gida yake baiwa anni labarin yadda sukayi taji dadi koba komai zai samu abinda zai riqesu,saidai kuma wani bangare na zuciyarta suya yake mata sosai,ace yau idriss shi zai dauki dan sa'id boyi boyin gida?,sa'id a sanda yana raye numfashi ne kawai baiyi musu ba,shine cinsu shansu suturarsu da duk wani kasuwanci da sukeyi,uwa uba sune suka kwashe duk wata dukiya ta sa'id din da sunan bashin banki yaci,ba ita ba hatta da khalipha sun sani sa'id din tunkan yayi bunqasar da yayi mutum ne mai tsoron bashi koda na naira biyar ne kuwa,balle har yakai kanshi banki ya karbi dukiyarsu.
Aikin da akace khaliphan zaiyu sai yatadda yaci uban hakan,gida ne mai matuqar girma wanda mahaifinsa ne ya ginawa idriss din dab da zai rasu mai dauke da dakuna da sassa sassa ginin zamani,shi zai share gidan komai girmansa,idan ta kama ma har dakin ibrahim dansa namiji tilo da yake gwadawa gata khaliphan ne zai shiga ya share,wani lokaci hatta da falon gidan hajiya binta saita hada masa da shi,baya ga haka idan i rahim ya bushi iska saiya hado masa kayansa yace ya wanke masa,haka aike lokuta mafiya yawa shike musu,dukka wadan nan hidimomin cikin kudinsa ne,bawai wani albashi na daban aka qara masa ba.
A qalla khalipha sai daya shekara uku yana wannan bautar gidan yayan mahaifinsa,cikin gidan da mahaifin nasa shiya gina masa shi,a qafa yake zuwa a qafa yake dawowa,aninci kuwa sai a debi kusan kwana hudu ba'a bashi na rana ba bare dare,duk ranar da aka bashin kuwa bawai ci yake ba,yana hadewa ne idan ya tashi tafiya ya kaiwa qannensa,wani lokaci idan yaga aikinnyi akan hanya yakan tsaya ya karba yayi kafin ya qarasa gida dinsu samu abun batarwa kafin wata ya cika a bashi albashinsa,don shi kanshi albashin idan alhj idris yaso sai wani watan ya shiga yayinkwanaki goma sha bai bashi ba,ya dinga kuma qananun maganganu shi daya yana fadin dadin ya yiwa khalipha yawa,ga cinyarwa gashi ana biyanshi kudi?,shi ai ya cancanci ma ayi masa jinjina sabida yayi abinda dukka sauran 'yan uwanshi suka kasa,khalipha bai taba daga kai ya dubeshi koya tanka mishi ba,yakanyi qoqarin danne fushinsa sarai duk sanda wani abu mara dadi ya faru,suna cin albarkacin anni data roqeshi kada ya yarda ko sau daya ya biyesu ayi wani abu mara dadi,dalilin barin gidan ya fara samo asali ne daga sanda jama'ar gidan haj binta da ibrahim suka soma qorafin ana musu dauke dauke,kusan kullum Allah ne dakullum sai anyi cigiyar an nemi abu an rasa.
Rabon za'ayi ranar da khalipha ya shiga dakin dakin ibrahim yi masa shara,khalipha tun asali mutum me maison ado da qamshi,kwalliya na burgeshi qwarai,dalili daya sanya koya ya samu kudi bai rasa siyiwa hajar abun kwalliya na mata koda jambaki ne kuwa dan naira hamsin,koda shi bai saka ba ita ta saka,to ibrahim ba laifi akwai qwalisa da ado,duk sanda yayi kwalliya khalioha kan kalleshi,yana tuna sanda mahaifinsu keda rai,duk juma'ar duniya sababbin kaya suke sakawa,wani lokacima anko suke da babanshi,akwai wani turare da ibrahim din ke amfani dashi,kalipha na matuqar son qamshin turaren,ranar yaje yi masa shara saiya dauka ya fesa sau daya a jikinsa,yana shirin ajewa ibrahim ya shigo dakin,nan ya soma cuccusawa ma khalipha ashar yana fadin ashe shine barawon gidansu,ya gaya mishi don ubanshi mai ya dauka
"Babu abinda na dauka maka sai turare dana fesa,wanda shima nasan nayi kuskure kuma kayi haquri don Allah" khaliphan ya fada tunda yasan laifinsa ne,kafewa ibrahim yayi yace bai yarda ba sai khalipha ya tube ya dubashi
"Bazqiyiwu ba tunda na rantse maka ban dauka ba ban dauka ba,dana dauka din kai tsaye zan gaya maka na dauka,don nafi tsorin mahaliccina fiye dakai"
"Ni kake gayawa ba tsorona kake ba,kayimin sata ka dinga gayamin baka tsoro na?" Saifa ibrahim ya rufe khalipha da duka,a sannan ya girmeshi hakanan khaliphan ya rame ibrahim ya fushi gabaran jiki,hakan shi ya baiwa ubrahim damar yiwa khalipha duka bana wasa ba,ya gwara kanshi da bango sosai wanda yayi sanadiyyar sunewarshi,bai farfado ba sai a asibiti,tunda ya samu sauqi aka sallemshi ya koma gida,duk sanda ya tuno da abin yana qona mishi rai,sharrin sata abu ne ba qarami ba,amma anni tace ya barsu da Allah,ta kuma yi masa fadan fesa masa turaren da yayi,ta gaya masa shine silar komai,dabai fesa ba da duk hakan bata faru ba,wannan shine silar abinda ya gadarwa khalipha cuwon kai mai tsanani da yake shan wuya duk sanda ya tasarmasa har kwanan gobe.
sanda abun ya faru saura kwana biyu a biyashi albashinsa,kwana biyu na cika saiga kawu idris da albashin khaliphan,sunyi mamakin ganinshi don sunsan bata yadda za'ayi ya biyoshi da albashinsa,ilai kuwa bayan ya miqa albashin sai ya sassauta murya cikin murmushi,a lokacin khalipha na dakin annin yana kwance don bai gama murmurewa ba
"Wata magana nazo miki da ita mai muhimmanci aisha,wadda idan har kika amince da ita ni dake gaba daya kowa zai amfana"
"Inajinka,Allah yasa alkhairi" ta fada tana dubanshi a darare don ita har yanzu bata amince da zuwanshi ba
"Nace ba....me zai hana muyi aure ni dake,idan yaso saiki kwaso 'ya'yanki naci gaba da kuka dasu,'ya'yan sa'idu ai 'ya'yana ne" a zabure khalipha dake kwance ya miqe,cikin azama ya tashi tsaye ya fito falon
"Tashi ka fitar mana daga gida" kallonshi idris yayi
"Meyw haka khalipha?"
"Nace tashi ka fitar mana daga gida maciyin amana kawai,Allah ya tsare anni da aurenka har abada wallahi tafi qarfinka"
"Me kake haka khalipha?" Anni ta fada tana qoqarin tsawatar masa gajin yadda yataso haiqan kaman zai daki kawu idris,sam bai saurari zancan anni ba bai saurarawa kawu idris ba sai daya danganashi da gate din gidan sannan ya dawo,idanunshi kamar garwashin wuta haka suk a kada sukayi jajur,haka kawai ya kasa zaune ya kasa tsaye saboda bacin rai ya dinga kai kawo
"Anni,duk randa mutumin nan ya sake dawowa gidan nan saina nakasta shi" haka ya dinga fada saida annin ta tsawatar masa
"ka shiga hankalinka mana khalipha,ni din bansan me nake ba koko yaya?,idris ne fa na sanshi na kuma san halinshi da manufofinsa kaf tun kafin a haifeka" da qyar anni ta iya control dinsa,haka yake bai iya fushi ba,ya kuma qaro zafin zuciya sanadiyyar tsangwama da rashin kirki da azabar da suka dinga gwada masa da 'yan uwanshi.
Tun daga ranar bai sake waiwayarsu ba kamar sauran,su kadai suke rayuwarsu,su kadai suke fadi tashinsu,su kade suke cin wahalarsu,wataran subsamu wataran suyi kwana biyu uku basu samu ba.
Wata biyu da zuwan kawu idris da wannan maganar hajar ta soma wani irin ciwon ciki mai tsanani,idan ta fara wani lokaci har suma take,anyi gwaje gwaje ya tabbatar da appendixs ne kuma saidai ayi aiki,kasancewar babu babu kuma mai basu haka suka haqura suka zubawa sarautar Allah ido,haka hajar ta dinga fama,yau lafiya gobe babu,idan ciwon ya tasar mata kamar ba zata kai ba,ba wanda yasan halin da suke ciki ballantana ya nuna kulawarshi.
Idan ajali yayi kira ko babu ciwo aje,safiyar wata laraba ciwon ya tasarwa hajar sosai,a lokacin khalipha ya fita wajen nema musu abinda zasuci,don wayewar garin basu tashi da qwayar hatsi da zasu iya sanyawa a bakinsu ba,haidar ne ya dinga yawon nemanshi duk wajen da yasan za'a sameshi,da qyar ya samoshi wajen wani fili da ake kwashe bolar ciki za'a soma gini,khalipha na cikin masu kwashe sharar,a gigice ya tafi wajen ogan nasu ya masa bayanin halin da ake ciki,ya lissafa iya kai nawa khaliphan yayi aka biyashi,ya tausaya masa har qari yayi masa akai suka taho gida tare da haidar,kafin su qarasa tuni hajar ta galabaita ta fita hayyacinta,abun ya tsoratar da khalipha sosai don bata taba irin haka ba duk ciwon da take,nan suka kwasheta sai asibiti,a canma dan abunuwan da suka saya gwaje gwaje da sauransu duk sun cinye dan kudin daya riqo,duk da cewa asibitin gwamnati ne amma sunan a baki ne,kusan komai talaka shike ma kansa,duk abubuwan daya kamata gwamantin tayi ta saki.
Daga bisani likitan ya shaida musu cewa tilas a gaggauta yi mata aiki nan da awa ashirin da hudu,idan ba haka ba komai zai iya faruwa da ita.