← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 45 OF 114

Sashe 45

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hankalinmu bai dawo jikinmu ba sai sanda labarin wahalar da kike ciki ta riskemu,a sannan duka bakifi shejara hudu a amma yadda ake tafi dake tamkar wadda ta shekara goma,duk da tun sanda mahaifiyarki tabar gidan hankalin baffale kacokam ya koma kanki,kulawarsa duka tana gareki,a hankali sai ya soma bagarar dake kema,wanda mutane da yawa sunyi amannar an kawar da hankalin baffake ne daga kanki da mahaifiyarki,ba'a hayyacinsa yake aiwatar da komai ba,a sannan mukayi yunqurin karbowa naja 'yarta amma taci alwashin duk wanda ya taka gidanma babu ita babu shi har abada,a sannan baffa Allah ya masa rasuwa.

Hankalinmu bai sake tashi ba sai da kikayi wayo kika soma bibiyarta da kanki,amma wata iriyar tsana kyara da hantara ta dinga giftawa a tsakaninku,ba wanda bai mamakin wannan al'amari ba,har aka dinga zaton anya ba jinnu ne suka shiga jikin naja sukai amfani da abinda ya faru ba suka farraqaku,saidai daga baya muka fuskanci ras take bata da wata matsala,taja kunnen duk wani wamda yake ganin ya isa ya kawo daidaito kan lamarin,akwai wadanda sanadiyya daidaita lamarinku har yau babu jituwa tsakaninsu da mahaifiyarki,da tawa daga cikin 'yan uwa jin haushin abinda take miki yasa suka fita sabgarku gaba daya ke da ita,suna ganin kunfi kusa ai,duk yadda zasu soki basu kai ya uwar data haifeki ba.....to kinji indo...wannan shine sila kuma mafari"gwaggo asabe ta qarashe fada tana sauke numfashi.

Kuka sosai aysha takeyi,tausayin mahaifiyarta na ratsata sosai na irin wulaqanci da cin zarafin data fuskanta....yayin da wani bari na zuciyarta ke qalubalantar matakin data dauka akanta,ita meye laifinta,ba itace sila ba,ya akayi mahaifinta da mahaifiyarta qarshensu yazo da haka duk sa irin soyayyar da gwaggo asabe ke fadin sun yiwa junansu,anya kuwa batayi kuskuren amincewa da khalipha ba kan cewar zai mata riqo irin wanda yayanta ciki daya zai mata,zai bata family da zatayi farinciki da su,zai bata dama da 'yanci duk kalar wanda ya dace?,ga masoya yadda suka qare...ina ga ita da zatayi rayuwar alfarma a qarqashinsa,ina ga ita da take da tabbacin ba soyayya ce ta hadasu ba,ba itace jigo ba...tausayi ne da taimako da zaiyi ma rayuwarta.

mero ma dake gefe tayi mutuwar zaune tana juya lamarin,ba shakka tana iya tuna wasu abubuwa da suka dinga biyo baya,irin shige da ficen da faccalolin ummin suka dinga yi suna yada cewa aysha shegiya ce,wanda banda Allah nasom baiwar tasa da tuni ya bita,sai ubangiji ya dakushe hakan daga qwaqwale da bakunan al'umma cikin lokaci qanqani da soma yada qaryar.

Kuka take sosai,tana sake tilawar labarin cikin kwanyarta daya bayan daya,tana fidda kuskuren kowan kowa a ciki,sosai tsoron maza ya kamata,firgici lokaci guda ya shigeta,tana ganin wautarta da kuskurenta na aminta da zama da ahalin khalipha,da wanne ido zasu dauketa wanne kallo zasuyi mata,ashe tabon dake cikin rayuwarta ya wuce iya yanda ita take tunani?.

Sai data ci kukanta sosai ba wanda ya tsaidata a cikinsu,domin dukkaninsu sunsan ba abu bane mai sauqi kashe irin wannan wutar,ba kuma qaramin al'amari bane gyara barnar da tayi shekara da shekaru da afkuwa ko ace tana afkuwa ma,a hankali ta dinga baiwa kanta baki,ta dinga qoqarin tsaida hawayenta,da kumburarrun jajayen idanunta ta dubi gwaggo asabe
"Na gode qwarai gwaggo,na gode da fidda ni da kikayi daga duhu xuwa haske,na gode da kika budemin abinda na jima ina neman sani a kai,na gode da kika kwancemin DAURIN BOYE" tana kaiwa nan ta miqe ta shiga bandaki,alwalar sallar magariba ta daura wadda ta gabato sannan ta fito ta soma shirin salla
"Kici daga da addu'a indo...komai mai wucewa ne da yardar Allah" cewar mero dake duban aysha cike da tausayi,murmushi mai ciwo wanda kai tsaye za'a iya kiranshi dana yaqe ta saki sannan tace
"Na sani mero...kuma ina fata wataran hakan ya zama tarihi"
"Amin ya Allah" ta fada itama tana shiga bandakin don daura alwalar.

Tana saman abun sallarta bayan ta idar,tunaninta ya rarrabu kashi kashi,daga nan inda take tana iya jiyo hayaniyar 'yan biki wadanda ke shirin tafiya dinner din asma'u,wayarta da tayi qara ita ta yanke tunaninta,ta waiwaya ta jawota sannan ta daga ta kara a kunneta,aliya ce tayi sallama cikin tsokana,wannan karon ranta cunkushe yake shi yasa bata samu damar maida mata ba
"Gobe ne tafiya qauyen ko?" Aliyan ta tambayeta bayan sun gama gaisawa
"Ke da kika ce ba zaki ba?....." Ayshan ta tambayeta a sanyaye
"Haba sashen,ko mafarki kikayi nace haka zaki yarda?....wasa nake miki...ko ramin kurege kika shiga ai naa shiga,haushi kika bani da kika qi yarda ko dan jan lalle ayi miki,na rasa wacce iriyar amarya ce haka?"
"Ta buzuzu mana..." Ta bata amsa qaramin murmushi na subucewa daga kan lebanta,sanadiyyar tuna aurenta na fari da tayi,wanda ko wankan arziqi bata yi ba randa za'a kaita bare a kai ga wani gyaran jiki da lalle,gwara wannan ta samu gyaran jiki yadda ya kamata,lallen ma itace bata so ba,jin abinda ayshan ta fada yasa aliya bushewa da dariya
"Au dariya ma kike?.....ni son ganinki ma nake fa akwai maganar da zamuyi"
"Har kin sani zumudi....Allah yasa ta samu" karyar da kai ayshan kawai tayi tana tuna yadda al'amrin ya kasance,tana tuna ayanzu waye khalipha na ainihi...hakan ba qaramin fadar mata da gaba yake ba
"Ko na taho yanzu?" Aliya ta katse mata tunaninta ta hanyar tambayarta
"A'ah....ki barshi kawai...ki bari ma tattauna gobe idan zamu wuce takai"
"To Allah ya kaimu"
"Amin....ki gaida mama"
"Zataji wlh...ai ran daurin aure tare zasu taho takai din da abba"
"Kice mata karta wahalar da kanta...ba komai ma za'ayi ba acan din,kawai nima dai inason asan asalina da tushena...kuma nima na jaddawa kaina wace ni...kar duniya ta rudeni"
"Koke ba zakiyi komai ba mu zamuyi malama....sai da safe" ta fadi tana katse wayar,itama aje wayar tayi,batasan wani matsayi zata baiwa aliyar ba,batasan wanne irin qauna take mata ba,tasani kawai Allah shi ya hada qaunarsu,ba wai don tana da wani abu da za'a qaunaceta ko a sota dominshi ba.

Bata bar kan abun sallar ba sai datayi isha'i,zuwa sannan hayaniyar gidan ta ragu saboda 'yan biki yawancinsu sun tafi sai dai daiku,jifa jifa mero na janta da hira don ta saki jiki tana kuma hada musu kayansu da zasu juya gobe da safe,anty safiyya ce ta shigo da sallama dakin,fuskarta qunshe da fara'a cikin ankon lace wanda sukayi iya su hudu 'ya'yan mummy yayyen amarya,tayi kyau sosai kasancewarta gwanar ado ce da kwalliya,duban aysha tayi tadan bata fuska
"Haba aysha...ya na ganki zaune kuma?,dinner din fa,kowa fa ya wuce iya mu mukai saura" murmushi ta dan saki,ina ita ina wannan waje?,ko giyar wake aka bata tasha ai ta wartsake
"Bana dan jin dadi ne sosai anty....bazan iya zuwa ba...afwa don Allah"
"Ayyah me ya sameki?"
"Dan ciwon kai ne kadan...amma na sha magani ma nasan zai sauka in sha Allahu"
"Sannu Allah ya sawwaqe yasa kaffara...kin kusa tafiya gidanki ki huta baki daya in sha Allah....amma ki miqe ki daure ki saka kayan da akace zaku saka yau din saboda masu shigowa" dan tunani ta shiga kadan wanda tuni har anty safiyya ta dagota
"Karki cemin cikin kayan da daddy yayi muku ba'a kawo miki komai ba?...." Shuru ita dai tayi ba tare data amsa ba,juyawa tayi fuuu zata fice,da sauri ayshan ta cafko hannunta,tayi narai narai da fuska idanunta sukai qwalqwal kamar zata fidda hawaye,dama har yanzu zuciyar a karye take
"Don Allah anty safiyya ki bar zancan nan karki tada komai....kinga dai yau duka abubuwan da suka dinga faruwa...karki silar tashin wani abu kuma,kiyi haquri" cikin sanyin jiki take duban ayshan,tana da sanyin rai da kyakkyawar zuciya,tana da nagarta da dattako,tana mata kaykkyawan fatan tayi dace da abokin rayuwa mai irin halayenta
"Shikenan aysha..ubangiji yayi miki kyakkyawan sakamako....yasa kin dace har abada"
"Amin amin anty safiya" cewar mero,bata sake cewa komai ba ta juya ta fita ranta sam babu dadi,bata jin dadin wasu daga cikin halayen mummyn dana 'yan uwanta,batasan meye laifin yarinyar ba,bata da wani mummunan hali qwaya daya tak,kawai don Allah ya yita cikin jinsin talakawa?,kawai don Allah ya sallada zata zauna qasansu taci arziqin da basu suka baiwa kansu ba,Allah ne ya ara musu donsu tallafi bayinsa mabuqata,gashi cikin ikonsa da buwayarsa ya soma yi mata baiwa da kyauta daga cikin ni'imominsa,tana fatan nagartacce ne wanda zata huta ta manta dukkan wata wahala ta rayuwarta.
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*

*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_

*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_

*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_

*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_

*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_

*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300

*DB*

27

*Dimbin godiya a gareku masoyan da basu manta halacci da alkhairi*🙏🏽🙏🏽🙏🏽

_Alhamdulillah,wato haka rayuwa take,a duk sanda ka dage kan ka karya wani ko kaga bayanshi matuqar Allah na tare da shi aikin banza kake,matuqar zuciyarsa a tsarkake take zaiyi wuya kaci galaba a kanshi,koda dukka mutanen duniya aljanu da bil'adama masu taimaka maka ne wajen ganin durqushewar wani,a sanda ake fafutukar fidda litattafanmu kota halin qaqa,sai hakan ya zame mana tamkar wata silar alkhairi a garemu,a lokacin ne wasu jama'a ke ninka farashin da muka sanyawa kowanne littafi namu ninkin baninkin su sayeshi a haka saboda sanin daraja da mutuntuka,da kuma zuciyar da bata manta alkhairin mu a garesu a baya,DUKKAN GODIYA TA TABBATA GA ALLAH MADAUKAKIN SARKI_

Qarfe sha daya na dare ta fita da kwanukan da su baba asabe suka ci abinci,ta bari ne zuwa sannan tana zaton ba kowa falon,idan ma sun dawo daga wajen dinner din tana tsammanin kowa ya tafi makwancinsa,ganin yadda kitchen din yake a hautsine sai ta kasa tafiya ta barshi haka,ta tsaya tana kikkintsa shi tare da gyara abinda zai gyaru a sannan tunda dare ya riga yayi.
Chapter 45 · 0% Book details