← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 35 OF 114

Sashe 35

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Idan akwai paper da biro taimaka ki rubutamin nayi maza na wuce nakai masa saqon tunda taqi tashi"
"Mu gani" tace tana miqa hannunta,wayar ya miqa mata kamar yadda ta buqata,sai yaga ta bare batirin ta ciro layin dake kai,dama babu memory a ciki,wayarta ta bude ta cire nata layukan ta dora nashi ta kunnata ta tasheta sannan ta miqa masa
"Kayi amfani da wannan,zai iya kiranka kafin ka qarasa inda yake yaji a kashe,zai kuma ji dadi....me yiwuwa ka sabawa dokar aiki ka biyo ta inda ba wajen aikinka bane a lokacin aiki" mamaki fal saman fuskarsa yake duban wayar data miqo masa,bawai mamakin tsadar wayar ba,don ya jima rabon ma daya riqe waya mai qaramin kudi kamar ta,mamakin yadda ta bashi wayar kanta tsaye yake,baya manta sanda asma'u ta soma ganin wayar hannunsa,sanda ya bata wayar yace ta saka mishi numbers dinta,sai tada ci dariya sosai kafin tace
"Wai wannan waya ce?" Ya amsa mata da eh,ta bude baki kamar zata sake magana sai kuma ta fasa,ta miqa hannu a qyamace zata amshi wayar sai kuma ta fasa
"Karta bata min hannu da Allah,bari na karanto maka digits din" da toh ya amsa mata,ta dinga karanto masa yana sakawa,sai da ya gama lodawa sannan tace
"Pls duk sanda muke tare ka dinga qoqarin boye wayarka,kar daya daga cikin friends dina su gani ka zubar min da mutunci"

"Ke dame zakiyi amfani?" Ya katse tunaninsa ta hanyar tambayarta
"Karka damu dama ba wani abu nakeyi da ita ba,ina da qaramar nokia zan saka layina a ciki" hannu ya sake miqa wa yana cewa
"Kawo waccar to ko Allah zaisa ta gyaru" kai ta kada
"Karka damu.....akwai wanda zaizo anjima ya karba za'a gyara" sai ta soma takawa tana cewa
"Ka wuce karka yi laifi.....sai anjima ka gaida hajiya".

Ya dan jima a tsaye a wajen yana juya wayar a hannunsa kafin ya soma takawa yana barin layin zuwa layin da motocinsa ke jiransa,duk a tafiyar mamakin abinda tayi ne ya masa rakiya,ya dinga jujjuya halayyarta yana hadata data asma'u,bai manta ranar data ciro dubu daya guda ta bashi da niyyar biya masa bashi duk da batasan waye shi ba
"Irin wannan sharp sharp haka yau...."cewar mahmoud dake danne danne a system din dake saman cinyarsa
"ka manta ina kan hanyar aiken oga"ya fada yana murmushi sanda motocin suka soma dagawa suna barin layin zuwa saman kwalta,dariya mahmoud ya saki sosai sannan yace
"Allah ya shiryeka khalipha....Allah ya nuna min ranar da qaryarka zata qare" bai amsa mishi ba sai wayar data bashi daya zaro ya jefata inda yake ajiye ajiyensa cikin motar,yana shirin maida locker ya rufe sai ya cireta kuma daga ciki ya hadata da wasu dacument nashi da zaije gida da su.

Wayarshi ya dauka bai ko saurari zancan da mahmoud ba ya soma duba miscal din da ya tarar,sai daya gama sannan ya lalubi wata number mai dauke da sunan anty ruqayya akai,tana shiga aka daga ba tare da jinkiri ba
"Manya.....yanzu nake shirin nemanka ai" murmushi ya saki sannan yace
"To ya akayi....ya ake ciki?"
"Komai ya kammala,yaushe zaka shigo ka gani?"
"Ba lokaci anty....amma zan duba idan na samu chance zan shigo"
"To shikenan...ka cema anni inata kiran layinta bai zuwa"
"Annin?" Ya tambaya yana dan fiddo ido kaman yana gabanta
"Bari na dubata" ya sake fadi da sauri yana katse kiran,kai tsaye annin tashi ya kira,ba jimawa kuwa ta daga ,ajiyar zuciya ya saki har sai data jiyoshi
"Ya akayi khalipha?,lafiya dai ko?"
"Anty tace tayi kiranki bata sameki ba...." Murmushi ta saki mai dan sauti,tasan ya kira ne yaji da gaske ne ko kuma wani abu ne ya faru
"Sharrin qarfen nasara ne....amma wayar a kunne take"
"To alhamdulillah....sai na dawo"
"Allah ya tsare"
"Amin" ya amsa yana jin dadi har cikin ransa sannan ya aje wayar.

"Wai me aka shirya mana ne?" Mahmoud ya sake tambayarsa lokacin da yake laluben number jibril jagoran tafiyar tasu zai tura masa texs
"Name fa?"
"Biki mana....kana nufin ba zamu gwangwanje ba?" Wayar ya aje bayan ya gama tura masa inda zasu yana murmushi
"Kasan wani abu ne mahmoud?....yarinyar ba irin sauran 'yammata bace ba....tayi universty amma saika zaci 'yar secondry ce...akwai ciwo a rayuwarta da yake hanata sukuni....,saidai ina fata haka halayyarta take bawai plan bane....saboda mahaifiyata mahmoud bana son abinda zai taba mahaifiyata" kai mahmoud yake jinjinawa cikin nazari sannan yace
"Na yadda da kai khalipha....kana da zuciya da mu'amala mai kyau,in sha Allahu ubangiji bazai bari wani ya cutar da kai ba.....yanzu yaushe za'a kaini wajen amarya?"
"Zaka iya saka kayan gwanjo?"
"Kai....kai ina....bazan iya ba magana ta gaskiya,ina laifin cikin kaya na na lalubo mai sauqi sauqi" harara khalipha ya watsa masa
"Sai kasha zamanka...don dama koni bata gama sabawa da ni ba"
"Aurenku na bani mamaki.....karon farko da na taba ganin auren da akayi babu soyayya tsakanin ango da amaryar amma duka sun amince zasu zauna da juna" ya fada yana dariya dariya,murmushi ya saki khalipha idanunshi na kallon titi
"Kawai abinda na sani shine....zan aureta ne a matsayin taimako da kallonta da nake kaman qanwata dana rasa a baya,zan aureta don in canza mata family...zan aureta don in bata farincikin da iyaye ke baiwa 'ya'yansu koda ba duka ba nasan zata samu wani bangare daga wajen anni....ina mata kallon qanwa ne bawai matar aure ba...koda na aureta zan bata 'yancin rayuwa irin na budurwa....saidai zan tsare mata mutuncinta"
"Zai yuwu?" Mahmoud ya tambaya yana kallonshi
"In sha Allah" shima ya bashi amsa bayan ya waiwayo sun hada idanu,kafada.mahmoud ya daga bayan ya danyi nazari kadan sannan yace
"Well....Allah ya bada nasara" bai amsa masa ba saboda sun iso wajen da zasuje din,babban wajen siye da siyarwa ne wanda ba nau'in suturar da basa saidawa masu kyau da tsada na qasashe daban daban,a wajen dukka motocin sukai parking,suka dunguma zasu bishi ya dakatar da su sukayi gaba shi da mahmoud da jibril sai nasir.

"Khalipha....khalipha" yaji ana ambaton sunansa da sauri sanda yake gab da shiga wajen sautin kuma na sake matsowa inda yake,cak ya tsaya sannan ya waiwayo a nutse yana duban inda kiran ke fitowa,zulaihat ce ke takowa cikin sauri idanunta a kanshi tana qare masa kallo
"Ashe haka khaliphan yake?" Abinda take ayyanawa kenan a ranta,wani irin kyau da kwarjini na musamman taga yayi mata
"Lallai talauci masifa ne...ko siffarsa ka ara saiya sauya maka kamanni bare ya kamaka da gaske" ta sake fada sanda take qarasowa inda yake tsayen,tana qarewa motocinsa da suka faka a wajen kallo a dabarance,saidai ta makara,gwani ne wajen saurin karantar mutum wannan baiwa ce da Allah yayi masa,duk kuma wanda ya dan jima tare da shi yasan da hakan,da idanu ya yiwa su jibril alamar su shige,yayin da ya zuba mata narkakkun idanunshi hannayensa zube a aljihun wandonsa,idanunta ta dan kautar saboda kaifi da sukayi mata,kyau da kwarjininsa suka cikata,zuciyarta ta karye har cikin ruhinta tana jin haushin wautar data tafka,da tuni yanzu wannan nata ne,da tuni mallakinya ne inda ta iya mallakar kanta ta boye zalamarta
"Yanzu muhammad haka rayuwa take don Allah?" Ta fada bayan tayi namijin qoqarin tattara dukkan qarfin halin da take da shi,bai amsa ba yadai ci gaba da kafeta da ido,ganin baida alamun amsawa ta sake hada wasu kalaman duk da ta soma karaya saidai tana fatar haqanta ta cimma ruwa
"Ba wanda baya kuskure fa....kuma ni banyi da wata manufa ba...kawai dai kuskure aka samu" ta qarashe maganar cikin lanqwashe murya tana duban cikin idanunsa da wani salon kallo da take fatan ta tafi da hankalinsa,saidai ko gezau,mahmoud ya soma tabashi kadan yana son samun qarin haske ko kuma shi khaliphan yace wani abu,sai a sannan ya dauke idanunsa daga kanta,yana murmushi can qasan ranshi mamaki na sake rufeshi....yana kuma sake baiwa kansa yaqinin babu soyayyar gaskiya a doron duniya...idan ma akwai tayi da nisan da ba kowanne dan adam ke iya kamota ba,hannu ya dagawa mansur daya daga cikin yarashi,ya gane me yake nufi,saboda haka ya tako ya iso gabanshi da jakarshi ya budeta sannan ya miqa masa,hannu ya saka ya bude,kudi ne sabbi a miqe suka bayyana,bandir biyu ya ciro ya sannan yace masa ya rufe jakar,rufewar yayi sannan ya juya da ita ya bar wajen
"Sau daya dama take zuwar ma wani mutumin a rayuwa...kuma hakan ce ta faru da ke" hannunsa ya miqa a nutse ya soka mata kudin jikin jakar hannunta dake maqale a gwiwar hannu yana murmushi
"Ina fata wannan ya zama karo na qarshe da zaki nuna kin taba sanin khalipha a duk inda zaki ganshi....ki huta lafiya" ya fada yana juyawa mahmoud ya bishi a baya ba tare da yace komai ba.

Qwallar da suka cika idanunta sai a sannan suka silalo,kunya ta cikata na mutanen dake wucewa jifa jifa ta inda suke tsaye,gefe guda baqinciki da tarin takaici sun cikata...ba wannan take so ba.....muhammad takeso ya dawo yaci gaba da sonta kamar yadda suke a baya,ya kuma aureta burinta ya cika.

"Ban taba sonta ba.....da fari nagartar ta da na gani a fuska ita ta soma jana....ga zatona zamu dai daita daga baya na koyawa kaina yadda zan sota.....ashe ma tafiyar ba mai nisa bace" ya fada a taqaice wanda yasan ya isa amsa wa mahmoud,saqon ya isa kuwa,don ya gane daya daga cikin yammatan daya nuna yana so ne a baya,ba shakka ya tabbatar batasan waye khalipha,idan yabar abu ya barshi kenan har abada bai waiwayarsa,yana da sauqin kai tausayi da son jama'a,saidai baison yaudara da ha'inci,indai kana son tafiyarku da shi tayi tsaho tilas ka kiyaye wadan nan,sau tari idan ka karanceshi bai bai zaka daukeshi a mara kirki..kuma mutum mai tsauri da dokar tsiya,saidai yafi komai dadin zama da sauqin kai idan ka fahimceshi.

Bai wani jima a ciki ba,kaya ya zabarwa anni kamar yadda ya saba duk bayan wani dan lokaci,ya biya da kanshi kamar yadda bai yadda wani ya yiwa annin siyayya saishi ya dauko kayan da kanshi suna hira da mahmoud jifa jifa suja fito suka bar wajen.

*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*

*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_

*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_

*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_

*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_

*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
Chapter 35 · 0% Book details