Sashe 57
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kaman tafiyar kurame haka sukayi,ita aysha baqunta amal kishi har suka isa qofar part din nashi,amal na shirin juyawa aysha tayi qarfin halin cewa
"Ba zakiqaraso ba?" Idanu ta waro tana dubanta
"Ko da can ba'a shiga masa sashe any how ina ga yanzu?,sai da safe" ta fadi tana yin gaba,sai dataga wucewar amal din sannan ta tura qofar ta shiga tana tunani
"Komai nashi a tsare take sarkin tsari me da alama wannan mutumin" bashi a falon sai wasu jaridu dake zube gefe daya da alama dubasu ya gama yi ya tashi,daga can wani side din idanunta suka gamo mata qyallin wasu akwatuna,irin wanda ya bata dazu sak saidai su manyansa ne guda goma sha biyu,gefe daya ta samu ta zauna qasan carfet na tsahon minti talatin sannan aka turo qofar bedroom din aka fito,sanye yake da jallabiyya baqa sai zabga wani qamshin yake daban,dan tsaiwa yayi da ganinta a zaune,ya zaci anni ta riqeta kenan?,hannun rigarshi dake nade ya soma saukewa yana jin wani bawai,ya saba bararrajewarsa shi daya a sashensa ta yaya zai iya zama da wata,agogon dake maqale a bangon falon ya kalla,goma da arba'in sha daya saura kenan,din shirin kwanciya ma yake ya dawo cirar wayarsa ne
"Ammm..." Ya fada kana yayi shuru
"Inaga muje wajen anni ko akwao wani dakin spare ki kwana a can,zuwa lokacinda zanga ya za'ayi a gyara inda zaki zauna a nan" ya qarashe yana goge gargasar jikinsa dake jiqe da ruwa da qaramin towel.
Yana gaba tana baya har sashen anni,babu kowa a falon,sun kashe ma duka wutar falon alamun sun kwanta saishi ne ya kunna,saman anni suka haura kai tsaye har zuwa qofar dakinta yayi knocking,daga ciki ta bada izinin shigowa,tana zaune saman abun sallah da hijabi a jikinta,haka take duk dare bata wani barcin arziqi,tana raye darenta da salloli da addu'o'i ma yaranta da mai gidanta daya rasu,shi yasa yawanci take bacci tsakanin sha biyu na rana zuwa azahar haka hakadan,wanda irin wannan baccin sunna ne,annabi S A W yayi umarni da yinsa,yace saboda shaidan baya irin wannan baccin,yawanci hausawa muna kiransa da qailula,da ido ta bisu sannan daga bisani ta saukewa khalioha kallon baki daya,dai ya dan dirirce daga jisani ya tattara hankalinsa yace
"Anni...cewa nayi akwai sauran dakin da za'a ara mana zuwa sanda za'a gyara sashen nawa?" Wani irin kallo tayi masa kafin ta dauke kanta ta.mayar kan casbahar gabanta me dubu da take ja
"Babu,saidai wannan nawan da nake ciki"
"Subhanallah"ya fada a ransa cikin fargaba
"sai da safe"ya fada da sauri yana duban aysha tare dayi mata umarnin ta taso su tafi,batasan me yake faruwa ba itadai ta tashi ta bishi,a son ranta itama a samu inda zata kwanna a can,har su fita ta qwalo masa kira,shi kadai ya koma aysha ta jungina da makarin silver na matattakalar
"Daga yau karka sake yawon neman dakin da zaka aje matarka...karkayi kuskuran dako sau daya zata ji cikin ranta ita ba komai bace a cikin gidan nan,bata da cikakken matsuguni,bangarenka shine nata,shine cikakken 'yancinta,yanzu ba mallakinka bane"
"In sha Allahu anni" ya fada cikin nuna ladabi
"Tashi ka bani wuri sai da safe"
"Na gode" ya fada yana fita,suna tsaka da ficewa suka jiyo muryar rahama
"Yawon me angwaye suke haka alokacin daya kamata ace suna tsaka da morewa lokacinsu?" Ta tambayesu tana qarasowa cikin kayan bacci,dauke kai khalipha yayi ya juya baya kafin ya bata amsa
"Ina tunanin tsananin sa idonki ne ya hana kowanne saurayi tararki yace zai aureki sanoda yana gudun shegen qwaqwqwafinki" tilas ba don ya shirya ba yasa hannu ya damqo hannun aysha,ya hade yatsunsa da nata ya jawota yana fadin
"Sai da safe idan kin gama tambayoyin kya iya tafiya" sukayi gaba suka fice daga falon.
Bai saki hannunta ba duk da yadda wani abu ke ratsashi tun daga yatsanshi zuwa qwaqwalwarsa don yana gudun sa idon rahama,tsaf zata iya leqensu,sai da suka shiga falonshi ya maida muqullin ya rufe sannan ya zame hannunshi daga nata,wanda zuwa wannan tuni ta daskare a wajen,bata taba aikata hakan ba bata kuma tabajin irin hakan ba,tsoro da fargaba jikinta har dan rawa yake saboda tsoro da rashin sabo,guri ta samu ta zauna ba shiri zuciyarta na bugawa,tuni ya wuce bedroom sai ya tsaya ya rasa me zaiyi,tafin hannunsa ya duba kamar me neman amsa sannan ya hadashi da daya hannun nasa ya murza su sosai ko zai daina jin abinda yake ji idanunsa a lumshe yana furzar da iska mai dumi daga bakinsa,tsahon minti biyar yayi a haka sannan ya haura gadonshi ya ciro blanket da pillow qwaya biyu,yana jin bai kamata ita ta kwanta a falon ba saboda yadda anni ta nuna kulawa a kai shima ya kamata yayi komai saboda annin
"Ki shiga ki kwanta" yace da ita yana zube pillows din a qasa tare da shimfida blanket din kan kujera,kanta ta daga ta dubeshi,har ya gama shimfidar ya dora pillow bata motsa ba
"Nace ki shiga ciki ki kwanta" ji tayi hakan bai dace ba sam,karon farko data bude baki
"Babu komai zan kwanta a nan kai ka kwana a dakinka"
"Ba zaki iya ba"
"I can do it...ka manta,daa a tsakar gida nake kwana ma gaba daya kusa da turken dabbobi?" Ta fada qwalla ma shirin taruwa a idonta,sai ya daga kai kawai yana dubanta jin abinda ta fada,baisan me ya tuna mata da wannan rayuwar ba a dan tsukin nan,kawar da kallonshi yayi daga gareta sannan yace
"No,kiyi kaman yanda nace miki" zamanshi yayi saman daya kujerar yaja magazine din yana dubawa,wanda talla ne na wasu kamfanunuwa da sabbin gine gine ake masa,a nutse ta miqe ta nufi dakin gadon a karo na biyu,sai data shiga ta maida qofar ta tura ta yadda ta ganta,gadon ta qarewa kallo sosai,bata jin zata iya hawa gadon daba nata ba ta kwana bayan ta kori mai gadon zuwa falo,tana jin kamar tayi zalunci ne,bargo itama ta cira ta shimfida a qasan gadon ta saka pillow,tana dora kanta tunanin mahaifiyarta ya dawo mata sabo fil,'yan sa'o'in data yi da anni da khalipha tafa yadda uwa ke nuna qaunawa yaranta,taga yadda uwa ke zama wani abun alfahari a wajen yaranta,duka cikin abinda ya zama musabbabin faruwar komai bata ga laifinta ba ko qwaya daya,me yasa abun yafi shafarta fiye da kowa?,me yasa abun yafi illatata,sakamakon ya koma gareta duka da nauyin laifin daba ita ta aikata ba,bata bada shawarar kan kasancewar haka ba?,idanunta ta lumshe hawayen dake maqale a gashin idanunta ya sauko zuwa kuncinta.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Tunda ta idar da asuba idanunta biyu bata koma ba tana ta rabo ido cikin dakin nashi,ba abinda bai burgeta ba a dakin,komai sai data qare masa kallo kafin ta dauke kai,bata taba gasgata zata kwana a irin dakin ba a rayuwarta,qarfe takwas na safiya tayi karambanin shiga wanka,sanda ta fito taga wani qaramin akwatin da yafi na jiya girma a gefen gado,batasan ya akayi ya shigo dakin ba,amma koma.meye tana da buqatar kayan sawa,data bude komao da komai akwai a ciki,saidai sabanin na jiya wannan harda soson wanka water soap,brush da toothpaste,sai setin rollon,body spray powder da sauran tarkacen kwalliya da qamsasa jiki,mai ta shafa kawai da powder,sai jikinta data bude da turare saboda qaunarta da qamshi itama,kayan dake cikin akwatin ta buda tana dubawa,qarshe ta zari wata atamfa ta saka set da mayafinta da komai.
Ita kanta data tsaya a jikin mudubi sai taga kaman ya zira jiki da yawa,ba wata kwalliya tayi ba amma kyanta ya fito sosai,atamfar holland ce pink me adon fari da blue zanan manyan ganye,cikin ranta take tasbihi da godiya ga ubangijinta wanda yake sauya mata rayuwa daga wannan bigiren zuwa wani a sanda baka zata ba,maida komai muhallinsa tayi ta gyara dakin zuwa bedroom din sannan ta maida mayafinta ta fito.
Babu kowa a parlour din sai tarkacensa da kayan shimfidarsa na jiya,saidai tana iya jiyo motsi cikin daya daga cikin dakunan dake falon,wala'alla tayi tunanin yana ciki,gyare falon tayi tas har ta gama bata daina jiyo motsin ba,saboda haka ta bude qofar kawai tayi cikin gida,don yau batason wannan wunin waje guda,ita sam takura take tunda bata saba da shi ba.
Tana shiga falon anni tayi kacibus da daya daga cikin me share sharen gidan riqe da mopper,cikin girmamawa ta gaida aysha ta amsa tana jin kunyar yadda tayi matan tare da mamakin ta santa ne?
"Anni ta tashi?" Kai ta girgiza
"Ai sai goma da rabi sannan take saukowa qasa ayi karin safe idan ba yunwa kaji ba ko uzuri gareka" kai ta jinjina sannan ta tambayeta kitchen,jagora tayi mata zuwa kitchen din ta qofar ta nan cikin falon zuwa wani corridor na musamman inda kitchen din yake.
Mutum biyu ta tadda suna aikin abincin safe,suma gaidata sukayi cikin girmamawa ta amsa musu kaman waccan karon,sai taja kujera ta zauna tana kallon yadda suke gudanar da ayyukansu,take kewar gida ta taso mata,sabo turken wawa,da tuni i yanzu itama tana can tana tata sabgar,duk motsinsu tana biye da su,a nan taga kurakurai da dama daya kamata su gyarashi yayin girkinsu,saidai bata ce musu komai ba saboda tana ganin hakan bai kamata ba daga zuwanta a matsayinta na baquwa bazatayi musu shishshigi ba.
Tana nan zaune har suka gama komai,saidai duk abinda sukeyi suna yine cikin tsafta daya daga cikin abinda ya burgeta kenan,da alama sun horu da tsafta daga wajen anni,dawowa sukai suna gyara wajen da wanke kayan da sukayi amfani da shi,zata kama musu saida kowa ya zabura suna fiddo da ido
"Ki rufa mana asiri...inamu ina saka matar boss aiki,kiyi haquri don Allah" suka fada a marairaice,karo na farko da aka soma girmamata a rayuwarta,karon farko da aka nuna ita din mutum ce mai wata daraja ta daban,dariya suka so bata,lallai qaramin sani qunqumi,lallai basu san ita din wace ba da basu wani gigice haka ba.
"Ba zakiqaraso ba?" Idanu ta waro tana dubanta
"Ko da can ba'a shiga masa sashe any how ina ga yanzu?,sai da safe" ta fadi tana yin gaba,sai dataga wucewar amal din sannan ta tura qofar ta shiga tana tunani
"Komai nashi a tsare take sarkin tsari me da alama wannan mutumin" bashi a falon sai wasu jaridu dake zube gefe daya da alama dubasu ya gama yi ya tashi,daga can wani side din idanunta suka gamo mata qyallin wasu akwatuna,irin wanda ya bata dazu sak saidai su manyansa ne guda goma sha biyu,gefe daya ta samu ta zauna qasan carfet na tsahon minti talatin sannan aka turo qofar bedroom din aka fito,sanye yake da jallabiyya baqa sai zabga wani qamshin yake daban,dan tsaiwa yayi da ganinta a zaune,ya zaci anni ta riqeta kenan?,hannun rigarshi dake nade ya soma saukewa yana jin wani bawai,ya saba bararrajewarsa shi daya a sashensa ta yaya zai iya zama da wata,agogon dake maqale a bangon falon ya kalla,goma da arba'in sha daya saura kenan,din shirin kwanciya ma yake ya dawo cirar wayarsa ne
"Ammm..." Ya fada kana yayi shuru
"Inaga muje wajen anni ko akwao wani dakin spare ki kwana a can,zuwa lokacinda zanga ya za'ayi a gyara inda zaki zauna a nan" ya qarashe yana goge gargasar jikinsa dake jiqe da ruwa da qaramin towel.
Yana gaba tana baya har sashen anni,babu kowa a falon,sun kashe ma duka wutar falon alamun sun kwanta saishi ne ya kunna,saman anni suka haura kai tsaye har zuwa qofar dakinta yayi knocking,daga ciki ta bada izinin shigowa,tana zaune saman abun sallah da hijabi a jikinta,haka take duk dare bata wani barcin arziqi,tana raye darenta da salloli da addu'o'i ma yaranta da mai gidanta daya rasu,shi yasa yawanci take bacci tsakanin sha biyu na rana zuwa azahar haka hakadan,wanda irin wannan baccin sunna ne,annabi S A W yayi umarni da yinsa,yace saboda shaidan baya irin wannan baccin,yawanci hausawa muna kiransa da qailula,da ido ta bisu sannan daga bisani ta saukewa khalioha kallon baki daya,dai ya dan dirirce daga jisani ya tattara hankalinsa yace
"Anni...cewa nayi akwai sauran dakin da za'a ara mana zuwa sanda za'a gyara sashen nawa?" Wani irin kallo tayi masa kafin ta dauke kanta ta.mayar kan casbahar gabanta me dubu da take ja
"Babu,saidai wannan nawan da nake ciki"
"Subhanallah"ya fada a ransa cikin fargaba
"sai da safe"ya fada da sauri yana duban aysha tare dayi mata umarnin ta taso su tafi,batasan me yake faruwa ba itadai ta tashi ta bishi,a son ranta itama a samu inda zata kwanna a can,har su fita ta qwalo masa kira,shi kadai ya koma aysha ta jungina da makarin silver na matattakalar
"Daga yau karka sake yawon neman dakin da zaka aje matarka...karkayi kuskuran dako sau daya zata ji cikin ranta ita ba komai bace a cikin gidan nan,bata da cikakken matsuguni,bangarenka shine nata,shine cikakken 'yancinta,yanzu ba mallakinka bane"
"In sha Allahu anni" ya fada cikin nuna ladabi
"Tashi ka bani wuri sai da safe"
"Na gode" ya fada yana fita,suna tsaka da ficewa suka jiyo muryar rahama
"Yawon me angwaye suke haka alokacin daya kamata ace suna tsaka da morewa lokacinsu?" Ta tambayesu tana qarasowa cikin kayan bacci,dauke kai khalipha yayi ya juya baya kafin ya bata amsa
"Ina tunanin tsananin sa idonki ne ya hana kowanne saurayi tararki yace zai aureki sanoda yana gudun shegen qwaqwqwafinki" tilas ba don ya shirya ba yasa hannu ya damqo hannun aysha,ya hade yatsunsa da nata ya jawota yana fadin
"Sai da safe idan kin gama tambayoyin kya iya tafiya" sukayi gaba suka fice daga falon.
Bai saki hannunta ba duk da yadda wani abu ke ratsashi tun daga yatsanshi zuwa qwaqwalwarsa don yana gudun sa idon rahama,tsaf zata iya leqensu,sai da suka shiga falonshi ya maida muqullin ya rufe sannan ya zame hannunshi daga nata,wanda zuwa wannan tuni ta daskare a wajen,bata taba aikata hakan ba bata kuma tabajin irin hakan ba,tsoro da fargaba jikinta har dan rawa yake saboda tsoro da rashin sabo,guri ta samu ta zauna ba shiri zuciyarta na bugawa,tuni ya wuce bedroom sai ya tsaya ya rasa me zaiyi,tafin hannunsa ya duba kamar me neman amsa sannan ya hadashi da daya hannun nasa ya murza su sosai ko zai daina jin abinda yake ji idanunsa a lumshe yana furzar da iska mai dumi daga bakinsa,tsahon minti biyar yayi a haka sannan ya haura gadonshi ya ciro blanket da pillow qwaya biyu,yana jin bai kamata ita ta kwanta a falon ba saboda yadda anni ta nuna kulawa a kai shima ya kamata yayi komai saboda annin
"Ki shiga ki kwanta" yace da ita yana zube pillows din a qasa tare da shimfida blanket din kan kujera,kanta ta daga ta dubeshi,har ya gama shimfidar ya dora pillow bata motsa ba
"Nace ki shiga ciki ki kwanta" ji tayi hakan bai dace ba sam,karon farko data bude baki
"Babu komai zan kwanta a nan kai ka kwana a dakinka"
"Ba zaki iya ba"
"I can do it...ka manta,daa a tsakar gida nake kwana ma gaba daya kusa da turken dabbobi?" Ta fada qwalla ma shirin taruwa a idonta,sai ya daga kai kawai yana dubanta jin abinda ta fada,baisan me ya tuna mata da wannan rayuwar ba a dan tsukin nan,kawar da kallonshi yayi daga gareta sannan yace
"No,kiyi kaman yanda nace miki" zamanshi yayi saman daya kujerar yaja magazine din yana dubawa,wanda talla ne na wasu kamfanunuwa da sabbin gine gine ake masa,a nutse ta miqe ta nufi dakin gadon a karo na biyu,sai data shiga ta maida qofar ta tura ta yadda ta ganta,gadon ta qarewa kallo sosai,bata jin zata iya hawa gadon daba nata ba ta kwana bayan ta kori mai gadon zuwa falo,tana jin kamar tayi zalunci ne,bargo itama ta cira ta shimfida a qasan gadon ta saka pillow,tana dora kanta tunanin mahaifiyarta ya dawo mata sabo fil,'yan sa'o'in data yi da anni da khalipha tafa yadda uwa ke nuna qaunawa yaranta,taga yadda uwa ke zama wani abun alfahari a wajen yaranta,duka cikin abinda ya zama musabbabin faruwar komai bata ga laifinta ba ko qwaya daya,me yasa abun yafi shafarta fiye da kowa?,me yasa abun yafi illatata,sakamakon ya koma gareta duka da nauyin laifin daba ita ta aikata ba,bata bada shawarar kan kasancewar haka ba?,idanunta ta lumshe hawayen dake maqale a gashin idanunta ya sauko zuwa kuncinta.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Tunda ta idar da asuba idanunta biyu bata koma ba tana ta rabo ido cikin dakin nashi,ba abinda bai burgeta ba a dakin,komai sai data qare masa kallo kafin ta dauke kai,bata taba gasgata zata kwana a irin dakin ba a rayuwarta,qarfe takwas na safiya tayi karambanin shiga wanka,sanda ta fito taga wani qaramin akwatin da yafi na jiya girma a gefen gado,batasan ya akayi ya shigo dakin ba,amma koma.meye tana da buqatar kayan sawa,data bude komao da komai akwai a ciki,saidai sabanin na jiya wannan harda soson wanka water soap,brush da toothpaste,sai setin rollon,body spray powder da sauran tarkacen kwalliya da qamsasa jiki,mai ta shafa kawai da powder,sai jikinta data bude da turare saboda qaunarta da qamshi itama,kayan dake cikin akwatin ta buda tana dubawa,qarshe ta zari wata atamfa ta saka set da mayafinta da komai.
Ita kanta data tsaya a jikin mudubi sai taga kaman ya zira jiki da yawa,ba wata kwalliya tayi ba amma kyanta ya fito sosai,atamfar holland ce pink me adon fari da blue zanan manyan ganye,cikin ranta take tasbihi da godiya ga ubangijinta wanda yake sauya mata rayuwa daga wannan bigiren zuwa wani a sanda baka zata ba,maida komai muhallinsa tayi ta gyara dakin zuwa bedroom din sannan ta maida mayafinta ta fito.
Babu kowa a parlour din sai tarkacensa da kayan shimfidarsa na jiya,saidai tana iya jiyo motsi cikin daya daga cikin dakunan dake falon,wala'alla tayi tunanin yana ciki,gyare falon tayi tas har ta gama bata daina jiyo motsin ba,saboda haka ta bude qofar kawai tayi cikin gida,don yau batason wannan wunin waje guda,ita sam takura take tunda bata saba da shi ba.
Tana shiga falon anni tayi kacibus da daya daga cikin me share sharen gidan riqe da mopper,cikin girmamawa ta gaida aysha ta amsa tana jin kunyar yadda tayi matan tare da mamakin ta santa ne?
"Anni ta tashi?" Kai ta girgiza
"Ai sai goma da rabi sannan take saukowa qasa ayi karin safe idan ba yunwa kaji ba ko uzuri gareka" kai ta jinjina sannan ta tambayeta kitchen,jagora tayi mata zuwa kitchen din ta qofar ta nan cikin falon zuwa wani corridor na musamman inda kitchen din yake.
Mutum biyu ta tadda suna aikin abincin safe,suma gaidata sukayi cikin girmamawa ta amsa musu kaman waccan karon,sai taja kujera ta zauna tana kallon yadda suke gudanar da ayyukansu,take kewar gida ta taso mata,sabo turken wawa,da tuni i yanzu itama tana can tana tata sabgar,duk motsinsu tana biye da su,a nan taga kurakurai da dama daya kamata su gyarashi yayin girkinsu,saidai bata ce musu komai ba saboda tana ganin hakan bai kamata ba daga zuwanta a matsayinta na baquwa bazatayi musu shishshigi ba.
Tana nan zaune har suka gama komai,saidai duk abinda sukeyi suna yine cikin tsafta daya daga cikin abinda ya burgeta kenan,da alama sun horu da tsafta daga wajen anni,dawowa sukai suna gyara wajen da wanke kayan da sukayi amfani da shi,zata kama musu saida kowa ya zabura suna fiddo da ido
"Ki rufa mana asiri...inamu ina saka matar boss aiki,kiyi haquri don Allah" suka fada a marairaice,karo na farko da aka soma girmamata a rayuwarta,karon farko da aka nuna ita din mutum ce mai wata daraja ta daban,dariya suka so bata,lallai qaramin sani qunqumi,lallai basu san ita din wace ba da basu wani gigice haka ba.