Sashe 10
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana shirin zama gefan gadon inna yelwan qamshin turaren ya ziyarci hancinta,qamshi ne data san cewa ba irin wanda inna kulu ke amfani da shi bane,hakan ya sanya ta soma baza idonta cikin dakin,tashin farko jikinta ya soma rawa har ta kasa hayewa saman gadon qarfen mai tudu wanda ya sha katifa,ta zame baki daya zuwa qasan ledar dakin ta zube ragwaf cikin rawar jiki,umminta ce zaune kan kujera qwaya daya dakin,sanye take cikin wani legos lace mai kyau da tsada peach wanda aka yiwa dinkin buba qarama da plain zani,hannunta sanye da awarwaro da zobe,haka wuyanta da kunneta sanye da sarqa da dan kunne,tayi fresh tayi kyau fiye da yadda ta santa ma ashekarun baya,tunda aqalla yanzu ta kusa shekara biyar rabon data sanyata a idanunta,daurin dankwalinta dai dai da zamani,idanunta na kan wayarta qirar samsung torching dake hannunta tana shafawa,cikin rawar murya ta hada lafazin
"Ina wuni ummi...." Shiru taji kamar yadda ta zata,tamkar babu wata halitta a dakin bayan ita,ko motsi ummin bata yi ba bare ta saka ran amsawarta,kai ka rantse da Allah bata san akwai halitta cikin dakin ba
"Ummi bar....ka da yamma....an yini lpy?" Ta sake maimaitawa,saidai kaman waccan karon wannan karon ma ko motsi bata yiba bare ta amsa,abu guda ne ya banbanta yanayin shigowar 'yan matasan yara maza guda biyu a guje daya yana bin daya cikin dakin suka afka jikinta suna rigima kan wani abun wasa,sai sannan ta dagonta rungume wanda ya fado jikintan tana duban babban dake tsaye
"A'ah,a'ah abba yaya?,bana hanaku irin wannan guje gujen bane wai?"
"Ummi....."
"Kul na sake jin wannan sunan a bakinka"
"Mami nawa ne fa,ya bar nashina gida tun shekaran jiya da zamu taho na sakoshi cikin trolly na,shine yanzu ya dauke yace wai nashi ne"
"Shine zaka biyoshi haka?,bana son sakarcin banza...oya maza wuce daki kaje ka canza wadan nan kayan daka bata" ta fada tana ware masa idanu,haka nan ya juya ya fita yana cuno baki,shi kuma wanda ke jikintan yana ta dariya abinsa alamun ya samu nasara.
Idanunta ta maida kan basma daketa kallon aysha dake takure gefe guda kanta a qasa tana son yi mata magana amma tana shakkar ummin tasu,tsawa ta katsa mata
"Fice a gun,kar na sake ganin qafarki tsaye a wajen nan"
"Amma mami......"
"Ubanki nace....kama hannun yusra ku wuce daki ki gyara sauran kayanku da baki gama hadawa ba" kamar zata fashe da kuka haka basma matashiyar dake da shekara goma sha hudu ta kama hannun qanwarta dake da shekaru goma suka fice,sai data ga ficewarsu sannan ta daga yasir dake jikinta ta kama hannunshi suna niyyar ficewa a dakin,sai a sannan aysha ta daga kanta tana duban mahaifiyar tata da idanunta dake cike fal da qwalla,cikin rawar murya tace
"Ummi....ki yafemin don Allah duk abinda nayi miki...wanda na sani da wanda ban san......"
"Idan kika qara yimin magana Allah ya isa ban yafe ba" ta fada cikin tsawa sannan taja hannun yasir,cike da tsantsar tashin hankali ta bita da kallo qwalla na silalo mata suka ratse inna yelwa dake tsaye da kwano a hannunta
"Kuma ga naman naki binta"cewar innar
"samin a daki na" ta fada tana yin gaba,haka nan ta juya kuwa tabi bayanta.
Sanda ta dawo har aysha ta gama cin kukanta ta gode Allah,sai tuquqi da zuciyarta ke mata kadai,muryarta a shaqe suka gaisa da inna yelwa,ta kuma tambayeta jikin kawu ta sanar mata da sauqi,ko kadan bata tada zance abinda ya wakana tsakaninta da umminta ba,wannan ba shibe karo na farko ba da irin hakan ta taba faruwa ba,shi yasa sam aysha batayi mamaki ba,inna kulu na haka ne saboda ba ita ta haifi umminta ba?,koko tana haka ne saboda alkhairin da take samu daga wajen ummin nata kada ta yiwa kanta sanadi,saboda ta sani tsaf zata yanke duk wani alkhairi da take mata matuqar zaka shiga maganar data hada da ayshan,biyayya kusan duk wanda yaga yadda take mata za'a ce takewa binta,wanda hakan kusan kowa ke ganin bai rasa alaqa da abun duniya da take samu daga wajenta,zuciya da jikinta duka babu dadi hakan ya sanya bata iya tsaiwa taga dawowar kawu ba bare ta dubashi tayi sallama da inna yelwa da zummar ta dawo gobe.
Tana tafe tana share hawaye,sam bata ka biyo ta hanyar da jama'a suke wucewa sosai ba don bata da buqatar tsayawa tayi magana da kowa,kasancewar tunaninta bai tare da ita hakan shi ya bashi nasarar shan gabanta ba tare data lura ba,sai jan baya da tayi da sauri sabida ganin inuwar mutum a gabanta ta hasken farin wata,a nutse ta qare masa kallo haqoranshi a waje kamar yadda ta sansu yana washe mata baki shi a dole fara'a
"Indo matata.....yau a gari?" Kalma mafi muni data tsana taji ta kenan daga bakin dan ladin tun a shekarun baya zuwa yau,bata taba ganin dan akuya mara kunya irinsa ba,tun a baya neman tsari take da shi balle a yanzu da ta soma samun sa'ida da sauqin wahalar rayuwa,ta kuma san inda duniya ta dosa,bata iya amsa masa ba illa ce masa da tayi
"Dan matsa min malam na wuce sauri nake"
"Haba indo,yanzu fusabilillahi ke ba zaki haqura ki karbeni a matsayin miji ba kije ku zauna tare da 'yar uwarki,naga dai 'yar uwarki ce,abu shekara da shekaru amma kin kasa haqura,duk abinda na dinga yi miki sharrin shaidan ne da zuciya" bacin ransa da wanda ta qunso ya taso ya tokareta,cikin zafin nama da zafin zuciya ta kewayeshi fuu tayi gaba,binta yaci gaba da yi yana magiya saidai banza ma ta fishi a wajenta,don sam bata masa kallon mai hankali,ta sani cewa tsantsar kidahumanci da jahilci kadai sun isa su maidashi mahaukaci tuburan,bare ga shegiyar mai saurin tarwatsa rayuwar koma waye wato qwaya da yake afawa lokaci lokaci,bata taba zaton inda yana da cikakken hankali zai iya tararta ya dubi qwayar idonta ya mata magana ba,bai qyaleta ba sai da yaga shigarta cikin gida sannan ya haqura ya juya yana jin takaicin rasa indon da yayi,tana qiyasta yadda tayi kyau ta goge da tuni yana can yana mora,yanzu gashi yana can yana fama da ladidi.
*_WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER ( 08030811300)_*
*DAURIN BOYE*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
0⃣8⃣
Kebantaccen waje ne da yake ganawa da muhimman mutanensa,wanda a siffa yafi kama da lambu.
Waje ne mai kyau daya qawatu da shuke shuke da kujeru irin na kaba,daga gefe guda wani magangarar ruwa akayi mai kama da qorama,zakayi zaton ba cikin companyn yake ba saboda yadda aka tsarashi,kallo daya zaka ma wajen ka fuskanci dan qaramin taro aka gama yi a wajen,saboda yadda grass carfet din wajen ya baci da robobin kayan ci da na sha,khalipha na tsaye cikin mutanen wanda baqi ne daga qasar waje wanda zasuyi hadin gwiwa wajen bude wani kamfani,da sauri daya daga cikin yaranshi wanda ke riqe da wayoyinshi ya matso inda yake tsaye,ya tsaya daga bayanshi kadan cikin girmamawa
"Sir,ana kiranka" hannunshi kawai ya miqa ya amshi wayar yana ci gaba da magana da mr james,vivo dinsa ce yasan mai kiran koda bai duba ba,amma duk da haka saiya duba screen din,khadija ce kamar yadda ya zata,bai samu damar daga wayar ba har sai da suka kammala maganarsu da su mr james sukayi sallama da su suka shiga motocinsu suka fice daga companyn baki daya.
Da sauri daya daga cikin yaran ya sake matsowa da niyyar amsar wayar ya adana ta,daga masa hannu khalipha yayi sanda ya danna kiran khadija sannan yaja baya jikin wasu flowers da aka yiwa ado mai kyau
"Muhammad...ni kake qin dagawa waya?" Abinda ta soma fada kenan,kadan ya cije lips dinsa kana yace
"Afwa....ina wani uzuri ne....mun tashi lafiya?"sai data ja iska kafin ta amsa masa
"Lafiya lau.....ya ake ciki ne wai?,gaskiya jiran fa yayi yawa...har yau kana nufin kudin basu samu ba?" Danne bacin ranshi yayi cikin dakiya yace yana kada kai tare da tabbatarwa kansa itama khadijan ta fadi,bata kai labari ba,bata kuma cinye jarabawar ba
"Su naketa qoqarin hadawa basu samu ba....dubu goma ce kawai ta samu" can qasa yaji ta ja tsaki tana qunquni sannan tace
"Ka kawon dubu goman na toshe wata kafar,da babu gwara babu dadi"
"To shikenan"
"Kar ka wuce qarfe hudu saboda inason in fita"
"To babu damuwa" qit ta kashe wayar,ya cirata daga kunne yana kallonta gami da kada kai,har yau dai jiya iyau,dukkansu kaman tare aka haifesu tsabar kamanceceniyar hali,ya talaka yake wanda baida komai kafin ya samu macen aure a wannan zamanin?,ya talaka mara abun hannunsa yake kafin ya samu soyayyar gaskiya?,da wannan maganar zucin ya miqawa jibril wayar,ya amsa yana miqo masa daya daga cikin kebantattun wayoyin nashi wanda kira yake ta shigowa tun dazun,bai bashi bane ganin wata wayar yake amsawa,karba yayi ya kara a kunnesa kana ya soma takawa yana barin wajen,yana fita ma'aikata suka shigo suka soma kintsa wajen da kawar da duk wata dauda ko shara komai qanqantarta.
♦♦♦♦♦
Kusan jiran da ya saba yi mata na yau ya wuce na ko yaushe,bai damu sosai ba saboda maganar da yake cikin waya tun dazun ta dauke masa hankali,ya jima tsaye qofar gidan sanye da wani yadi mai sauqin kudi wanda aka yiwa dinkin riga iya gwiwarsa da gajeran hannu,irin yadikan nan ne da ake saidawa kan farashi mai sauqi,duk da haka yadin ya masa kyau saboda baiwar qira da Allah yayi masa,daga takalmin qafarsa har zuwa hularsa masu qaramin kudi ne duka baqaqe,mota uku ce ta masa rakiya saidai yau sun shigo har cikin layin,amma suna tsaye bayanshi qofar wani gida wanda a qalla daga gidan zuwa gidansu khadijan gidaje hudu ne a tsakanisu,waya ya daga ya kirata
"Gani nan" ta fada sannan ta kashe tana jan tsaki
"Kaman wani kudin arziqi ya kawo min,sai kyau iya kyau amma babu abokan tafiya,wannan da kyan da yake da shi da shine kudin shi kuma mummuna da da sauqi,kyau ba kudi ai wahala ce tunda ba dashi zaku rayu ba,ba kuma kyan zaka loqa a goshi kayi yawo da shi ba" ta fadi ita kadai tana mita sanda take gyara yafen mayafinta.
"Ina wuni ummi...." Shiru taji kamar yadda ta zata,tamkar babu wata halitta a dakin bayan ita,ko motsi ummin bata yi ba bare ta saka ran amsawarta,kai ka rantse da Allah bata san akwai halitta cikin dakin ba
"Ummi bar....ka da yamma....an yini lpy?" Ta sake maimaitawa,saidai kaman waccan karon wannan karon ma ko motsi bata yiba bare ta amsa,abu guda ne ya banbanta yanayin shigowar 'yan matasan yara maza guda biyu a guje daya yana bin daya cikin dakin suka afka jikinta suna rigima kan wani abun wasa,sai sannan ta dagonta rungume wanda ya fado jikintan tana duban babban dake tsaye
"A'ah,a'ah abba yaya?,bana hanaku irin wannan guje gujen bane wai?"
"Ummi....."
"Kul na sake jin wannan sunan a bakinka"
"Mami nawa ne fa,ya bar nashina gida tun shekaran jiya da zamu taho na sakoshi cikin trolly na,shine yanzu ya dauke yace wai nashi ne"
"Shine zaka biyoshi haka?,bana son sakarcin banza...oya maza wuce daki kaje ka canza wadan nan kayan daka bata" ta fada tana ware masa idanu,haka nan ya juya ya fita yana cuno baki,shi kuma wanda ke jikintan yana ta dariya abinsa alamun ya samu nasara.
Idanunta ta maida kan basma daketa kallon aysha dake takure gefe guda kanta a qasa tana son yi mata magana amma tana shakkar ummin tasu,tsawa ta katsa mata
"Fice a gun,kar na sake ganin qafarki tsaye a wajen nan"
"Amma mami......"
"Ubanki nace....kama hannun yusra ku wuce daki ki gyara sauran kayanku da baki gama hadawa ba" kamar zata fashe da kuka haka basma matashiyar dake da shekara goma sha hudu ta kama hannun qanwarta dake da shekaru goma suka fice,sai data ga ficewarsu sannan ta daga yasir dake jikinta ta kama hannunshi suna niyyar ficewa a dakin,sai a sannan aysha ta daga kanta tana duban mahaifiyar tata da idanunta dake cike fal da qwalla,cikin rawar murya tace
"Ummi....ki yafemin don Allah duk abinda nayi miki...wanda na sani da wanda ban san......"
"Idan kika qara yimin magana Allah ya isa ban yafe ba" ta fada cikin tsawa sannan taja hannun yasir,cike da tsantsar tashin hankali ta bita da kallo qwalla na silalo mata suka ratse inna yelwa dake tsaye da kwano a hannunta
"Kuma ga naman naki binta"cewar innar
"samin a daki na" ta fada tana yin gaba,haka nan ta juya kuwa tabi bayanta.
Sanda ta dawo har aysha ta gama cin kukanta ta gode Allah,sai tuquqi da zuciyarta ke mata kadai,muryarta a shaqe suka gaisa da inna yelwa,ta kuma tambayeta jikin kawu ta sanar mata da sauqi,ko kadan bata tada zance abinda ya wakana tsakaninta da umminta ba,wannan ba shibe karo na farko ba da irin hakan ta taba faruwa ba,shi yasa sam aysha batayi mamaki ba,inna kulu na haka ne saboda ba ita ta haifi umminta ba?,koko tana haka ne saboda alkhairin da take samu daga wajen ummin nata kada ta yiwa kanta sanadi,saboda ta sani tsaf zata yanke duk wani alkhairi da take mata matuqar zaka shiga maganar data hada da ayshan,biyayya kusan duk wanda yaga yadda take mata za'a ce takewa binta,wanda hakan kusan kowa ke ganin bai rasa alaqa da abun duniya da take samu daga wajenta,zuciya da jikinta duka babu dadi hakan ya sanya bata iya tsaiwa taga dawowar kawu ba bare ta dubashi tayi sallama da inna yelwa da zummar ta dawo gobe.
Tana tafe tana share hawaye,sam bata ka biyo ta hanyar da jama'a suke wucewa sosai ba don bata da buqatar tsayawa tayi magana da kowa,kasancewar tunaninta bai tare da ita hakan shi ya bashi nasarar shan gabanta ba tare data lura ba,sai jan baya da tayi da sauri sabida ganin inuwar mutum a gabanta ta hasken farin wata,a nutse ta qare masa kallo haqoranshi a waje kamar yadda ta sansu yana washe mata baki shi a dole fara'a
"Indo matata.....yau a gari?" Kalma mafi muni data tsana taji ta kenan daga bakin dan ladin tun a shekarun baya zuwa yau,bata taba ganin dan akuya mara kunya irinsa ba,tun a baya neman tsari take da shi balle a yanzu da ta soma samun sa'ida da sauqin wahalar rayuwa,ta kuma san inda duniya ta dosa,bata iya amsa masa ba illa ce masa da tayi
"Dan matsa min malam na wuce sauri nake"
"Haba indo,yanzu fusabilillahi ke ba zaki haqura ki karbeni a matsayin miji ba kije ku zauna tare da 'yar uwarki,naga dai 'yar uwarki ce,abu shekara da shekaru amma kin kasa haqura,duk abinda na dinga yi miki sharrin shaidan ne da zuciya" bacin ransa da wanda ta qunso ya taso ya tokareta,cikin zafin nama da zafin zuciya ta kewayeshi fuu tayi gaba,binta yaci gaba da yi yana magiya saidai banza ma ta fishi a wajenta,don sam bata masa kallon mai hankali,ta sani cewa tsantsar kidahumanci da jahilci kadai sun isa su maidashi mahaukaci tuburan,bare ga shegiyar mai saurin tarwatsa rayuwar koma waye wato qwaya da yake afawa lokaci lokaci,bata taba zaton inda yana da cikakken hankali zai iya tararta ya dubi qwayar idonta ya mata magana ba,bai qyaleta ba sai da yaga shigarta cikin gida sannan ya haqura ya juya yana jin takaicin rasa indon da yayi,tana qiyasta yadda tayi kyau ta goge da tuni yana can yana mora,yanzu gashi yana can yana fama da ladidi.
*_WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER ( 08030811300)_*
*DAURIN BOYE*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
0⃣8⃣
Kebantaccen waje ne da yake ganawa da muhimman mutanensa,wanda a siffa yafi kama da lambu.
Waje ne mai kyau daya qawatu da shuke shuke da kujeru irin na kaba,daga gefe guda wani magangarar ruwa akayi mai kama da qorama,zakayi zaton ba cikin companyn yake ba saboda yadda aka tsarashi,kallo daya zaka ma wajen ka fuskanci dan qaramin taro aka gama yi a wajen,saboda yadda grass carfet din wajen ya baci da robobin kayan ci da na sha,khalipha na tsaye cikin mutanen wanda baqi ne daga qasar waje wanda zasuyi hadin gwiwa wajen bude wani kamfani,da sauri daya daga cikin yaranshi wanda ke riqe da wayoyinshi ya matso inda yake tsaye,ya tsaya daga bayanshi kadan cikin girmamawa
"Sir,ana kiranka" hannunshi kawai ya miqa ya amshi wayar yana ci gaba da magana da mr james,vivo dinsa ce yasan mai kiran koda bai duba ba,amma duk da haka saiya duba screen din,khadija ce kamar yadda ya zata,bai samu damar daga wayar ba har sai da suka kammala maganarsu da su mr james sukayi sallama da su suka shiga motocinsu suka fice daga companyn baki daya.
Da sauri daya daga cikin yaran ya sake matsowa da niyyar amsar wayar ya adana ta,daga masa hannu khalipha yayi sanda ya danna kiran khadija sannan yaja baya jikin wasu flowers da aka yiwa ado mai kyau
"Muhammad...ni kake qin dagawa waya?" Abinda ta soma fada kenan,kadan ya cije lips dinsa kana yace
"Afwa....ina wani uzuri ne....mun tashi lafiya?"sai data ja iska kafin ta amsa masa
"Lafiya lau.....ya ake ciki ne wai?,gaskiya jiran fa yayi yawa...har yau kana nufin kudin basu samu ba?" Danne bacin ranshi yayi cikin dakiya yace yana kada kai tare da tabbatarwa kansa itama khadijan ta fadi,bata kai labari ba,bata kuma cinye jarabawar ba
"Su naketa qoqarin hadawa basu samu ba....dubu goma ce kawai ta samu" can qasa yaji ta ja tsaki tana qunquni sannan tace
"Ka kawon dubu goman na toshe wata kafar,da babu gwara babu dadi"
"To shikenan"
"Kar ka wuce qarfe hudu saboda inason in fita"
"To babu damuwa" qit ta kashe wayar,ya cirata daga kunne yana kallonta gami da kada kai,har yau dai jiya iyau,dukkansu kaman tare aka haifesu tsabar kamanceceniyar hali,ya talaka yake wanda baida komai kafin ya samu macen aure a wannan zamanin?,ya talaka mara abun hannunsa yake kafin ya samu soyayyar gaskiya?,da wannan maganar zucin ya miqawa jibril wayar,ya amsa yana miqo masa daya daga cikin kebantattun wayoyin nashi wanda kira yake ta shigowa tun dazun,bai bashi bane ganin wata wayar yake amsawa,karba yayi ya kara a kunnesa kana ya soma takawa yana barin wajen,yana fita ma'aikata suka shigo suka soma kintsa wajen da kawar da duk wata dauda ko shara komai qanqantarta.
♦♦♦♦♦
Kusan jiran da ya saba yi mata na yau ya wuce na ko yaushe,bai damu sosai ba saboda maganar da yake cikin waya tun dazun ta dauke masa hankali,ya jima tsaye qofar gidan sanye da wani yadi mai sauqin kudi wanda aka yiwa dinkin riga iya gwiwarsa da gajeran hannu,irin yadikan nan ne da ake saidawa kan farashi mai sauqi,duk da haka yadin ya masa kyau saboda baiwar qira da Allah yayi masa,daga takalmin qafarsa har zuwa hularsa masu qaramin kudi ne duka baqaqe,mota uku ce ta masa rakiya saidai yau sun shigo har cikin layin,amma suna tsaye bayanshi qofar wani gida wanda a qalla daga gidan zuwa gidansu khadijan gidaje hudu ne a tsakanisu,waya ya daga ya kirata
"Gani nan" ta fada sannan ta kashe tana jan tsaki
"Kaman wani kudin arziqi ya kawo min,sai kyau iya kyau amma babu abokan tafiya,wannan da kyan da yake da shi da shine kudin shi kuma mummuna da da sauqi,kyau ba kudi ai wahala ce tunda ba dashi zaku rayu ba,ba kuma kyan zaka loqa a goshi kayi yawo da shi ba" ta fadi ita kadai tana mita sanda take gyara yafen mayafinta.