Sashe 42
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mummy ce ta turo qofar dakin dai dai sanda aysha ke wannan dariyar,dubanta mummy tayi sai ranta ya quntata,tana tunanin tasan komai da hadin bakinta yaron ya lullubesu,ta ayyana a ranta yanzu haka tana dariyar farinciki ne da samun nasara,idanun aysha ya sauka kan mummy sai ta miqawa mero wayarta tana miqewa cikin nutsuwa tace
"Me kike da buqata mummy,da kinyi magana sai nazo basai kinzo da kanki ba" kai ta girgiza ranta na baci,a zatonta tana bacin rai ne saboda aysha sun rufeta,saidai abinda bata sani ba shine tana bacin rai ne saboda ayshan ta samu daukaka da muhallin da autarta bata samu ba,hassada kecin ranta ba tare data farga ba
"Wannan ai yafi qarfin kizo saidai ni nazo da kaina....godiya na taso takanas nayi miki,wato duk zaman da mukeyi dake da yadda muka riqeki ashe ke ba haka bane cikin ranki,kallon maqiyiyarki kikemin,kallon abokiyar adawarki abokiyar gabarki wadda bata son cin gabanki kike min,har ku hada baki da yaron nan ku rufe mana komai sai munje ganin jeranki sannan mu gani,kinsan mai arziqi ne baki gaya mana ba,amma ya zowa a sma'u a wanda baida komai saboda wani baqin nufi dake ranshi,ko ba komai da munsan waye ya bayyana kanshi xamuyi duk shirin daya dace yadda ba za'a ji kunya ba,to na gode da sakayyar da kika yimin Allah ya saka da alkhairi" ta juya tana shirin fita,iya qololuwar tashin hankali aysha ta shige shi,dama ita gwanar hawaye nan da nan ruwan hawaye ya soma layi a fuskarta,bata gane kan me mummyn ke magana ba,me take nufi ne ?batasan sanda ta isa gaban mummy ba ta tareta cikin kuka tana fadin
"Wallahi mummy ba mai kudi bane...talaka ne shima kamata,idan da mai kudi ne anty asma'u ita zata soma sanin hakan,tunda ita ta hadani da shi,ta hanyarta komai ya tabbata har kawo yau...ki tambayeta kiji" ta qarasa fada muryarta na sarqewa
"Ke dalla matsa....dake da asma'un dukanku lusarai ne...kada ma asma'un taji labari.....kunsan waye muhammad abdulhakim mai goro?,kunsan wanne irin arziqi ke gareshi,dukanku baku sani ba,cikin 'yan sa'o'in aka gayan wayeshi,aisha kin nunan iyakata kuma ina godiya" ta qarasa fada tana kewayeta gami da ficewa daga dakin.
Kuka aysha ta saki har sai da gwaggo asabe sake zaune tana kallon ikon Allah ita da mero suka taso suka riqeta gami da zaunar da ita,tsoro ne fal cikin zuciyarta,ta yaya zata shiga familynsa bayan ya soma dayi mata qarya?,a hakan zai roqeta?,a hakan zai cika alqawarin daya dauka,tana tsoro,tana tsoron faruwar wani abu,don me zai yaudareta,akanme zai ninketa yazo mata da siffar daba tashi bace,yanzu gashi ya hadata da mummyn,ya hadata da mutanen da suka zauna da ita da dadi babu dadi,ba kamar danginta da suka kasa zama da ita ba saboda wani banzan dalilinsu maras tushe wanda baici ace ya shafi rayuwarta ba.
"Ohni sadiya..wai wannan wane irin lamari ne haka yake faruwa?,indo wadanne irin mutanene haka kike zaune da su?,tunda muka zo daga wannan sai wancan?" Cewar gwaggo cikin bacin rai da tashin hankali.
Miqewa tayi tsaye ta dubi su mero
"Ina zuwa" ta fada kawai kana ta fice,da hijabin data idar da sallar azahar a jikinta don haka bata da buqatar sanya wani abun.
Parlourn daddy ta nufa kai tsaye,tayi qoqarin daidaita nutsuwarta sannan tayi sallama ta kutsa kai,su biyu ne zaune a falon shi da anty safiyya,da alama wata magana suka gama tattaunawa ko suke kan tattaunawar,dukkansu shuru sukayi ganin shigowarta falon,kai tsaye ta isa gaban daddy ta duqa tana hawaye
"Daddy don Allah ka kirashi ki bashi haquri ka gaya masa ka fasa bashi aurena,daddy bazan aureshi ba,bazan iya zama cikinsu ba" anty safiyya zatayi magana ya dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu sannan ya maida hankalinsa wajen aishan
"Saboda me?" Ya tambayeta
"Daddy....yazo min da siffar daba tasa ba,ya yaudareni daddy,wannan ha'inci ne daddy,a haka zanje na zauna da su?" Kasa daurewa safiyya tayi sai data furta
"Aisha,anso kashe rayuwarki ne Allah ya raya ta,an hadaki dashi saboda ana tsammanin bashi da komai Allah sai ya kaiki hannun mai komai din,wannan kadai bai isa ki godewa Allah ba?,wannan abun da kike fada tamkar butulcewa Allah fa kikeso kiyi"da hanzari ta daga kai tana kallon anty safiyya,akwai wani abu,akwai wani data sani kenan game da yadda auren ya qullu?
"Aisha" daddy ya kira sunanta bayan ya dakatar da safiyya
"Me yasa baki gayamin tun farko yadda abun yake ba kika ja bakinki kika yi shuru,kina zaton da an tafi a haka na hadaki aure da shi Allah bazai kamamu ba mu duka?"fada sosai daddy ya dinga yi irin wanda bai taba yi ba,alama ranshi ya baci sosai,kuka ta dinga yi tana bashi haquri,yace sam nauyin bakinta baiyi masa ba,haquri ta bashi da alqawarin ba zata sake ba,daga bisani ya kwantar mata da hankali da bata labarin farkon sanin daya soma yiwa khalipha a rayuwarsa.
"na sanshi can shekarun baya masu yawa ta sanadin faduwar jakar kudadena,kudade ne masu yawa wanda banda kudaden akwai muhimman takarduna harda na kamfani na,sosai na shiga tashin hankali a sannan,saboda matuqar kudaden suka bace a sannan tsaf zan iya shiga talauci bana wasa ba,cikin ikon Allah kwanaki uku da faruwar haka aka kira wayar kamfani na akace ni ake nema kan kudina dana yar,nayi murna sosai na buqaci inda zanje mu hadu da wanda ya tsinci kudin,ba bata lokaci ya bani adress din gidansu,yace nayi haquri,yana da wani uzuri ne da baya barinsa ya fita daga gida da da kansa zai kawomin,nikam a sannan kota kan hakan baibi ba,saboda ko a qafa yace min na tafi wata qasar na amso zuwa zanyi
Sanda na isa gidansu nayi matuqar mamaki,gashi dai gida har gida irin ginin masu kudi da wadata na sannan amma kana masa kallon farko zakasan babu da talauci ta tasamma yi masa raga raga,mamaki na bai sake qaruwa ba sai dana shiga na tadda matashin dan shekara ashirin na jiyyar mahaifiyarsa magashiyyan rai a hannun Allah da qannenshi maza guda biyu,kana kallonsu kasan kuka suka gamayi dukansu,sanda na amshi kudin na tambayeshi nawa yakeso ga mamakina sai yace min babu komai,alfarma daya yake da buqata na biya kudin aikin mahaifiyarsa ta rabu da zafi da radadin ciwon da take fama da shi,na zaci zai buqaci sama da haka,amma sai yace min buqatarsa kenan,matsanancin ciwon suger take fama da shi wanda shi har takai ga ya taba mata qoda za'a mata aiki.
Muna tsaka da wannan maganar saiga 'yan sanda katsama kanmu,miqewa naga khaliohan yayi yayin da suka yo kanshi kamar kura ta samu nama syka cukuikuyeshi,yayin da yajeta rantsuwa yana fadin bashi bane,matashi dake bayansu yana cewa
"Karku saurara masa,qarya yake ku dakeshi"ni na miqe na musu magana,sannan na tambayi ba'asi,nan dan samdan yace ana tuhumarshi ne da yiwa yarinyar wan babanshi fyade,kuka yake sosai a sannan yana rantsewa da duk abinda yasan me girma ne kan bashi bane,yanayin nagartar yaron ya sakamin tantama kan zancan,naja daya daga cikin 'yan sandan waje nace ya gayamin gaskiyar magana,na masa alqawarin kudade mai tsoka,nan yace ba shakka bashi bane,amma alhj idris da yaronshi ibrahim su suka biyasu kan kada au saurara idan sunzo su kamashi,daga nan su kaishi kotu ma birsin sukeso yayi,don ya matsa kan maganar gadonsu,a take na gaya masa sunana sai yayi sororo,na kira sauran 'yan sandan na sallamesu duka da wani abu,nan ibrahim yahau min hauka,nace koya wuce kona makashi kotu kan ya yiwa khalipha qazafi,haka ya wuce don kada allura ta tono garma,kuka sosai ya dinga yi mahaifiyarsa dake kwance tana tayashi,haka qannensa maza guda biyu,a sannan naso jin labarin rayuwarsu amma sai naga bashi yafi muhimmanci ba,lafiyar mahaifiyarsa itace gaba,muka je asibitin na biya duk wani abun da za'a buqata a aikin,hatta da abincin da ita da su zasu ci,cikin nasara akayi aikin aka gama lpy ta kuma samu sauqi,ina da niyya da shirin taimakon rayuwarsu tafiyar gaggawa ta sameni russia,wanda ban dawo ba sai bayan watanni shida,dana dawo su na soma nema sai na tadda sun saida gidan sun tashi,kuma ba'asan ina suka koma ba,dole na haqura da neman nasu naci gaba da saka yarona addu'a,don gaskiya nasp na riqeshi d'ana,saboda gaskiya amana da hankali da nutsuwar da naga yana da ita,uwa uba yadda naga yanason mahaifiyarshi yana tattalinta,nasan lallai sai yaro na gari ne kawai zai hada wannan nagartar"
Dukansu shiru sukayi suna jinjina labarin,yayin da zuciyar aysha ta soma kuma rabuwa gida biyu,
"Kije kici gaba da addu'a ina da tabbas kan khalipha aysha...Allah ya baku xaman lafiya" anty safiyya ce ta amsa ayshan ta miqe cikin sanyin jiki tabar falon.
Sosai ranta ya dinga baci,hassada nacin ranta ba tare data sani ba,ta yaya ma aysha zata samu irin wannan gidan?,wayarta ta ciro ta soma neman tsohuwar lambarsa da suke waya,so take taji ta bakinsa,so take taji dalilin raina mata wayon da yayi tunda fari,saidai amsa daya ake bata is switched off,gani take ma kamar akwai wata a qasa,kaman ayshan ita ta shirya komai,wani irin gumi take ita kadai qwaqwalwarta na kaikawo,hakan ya sanya ta tashi don fitowa daga dakin sukayi kacibus da mummy a bakin qofa,duban asma'un tayi
"Kina jin sunan muhammad abdulhakim mai goro?" Kai asma'un ta kada,sosai ta sha jin sunan ko a bakin hamid ma
"Shine khalipha yaron da zai auri aysha" cikin qanqan da idanu take duban mummy,kamar tana zaton mummyn zata sauya zancan data gaya mata
"Mummy da gaske?"
"Ina wasa dake?" Ta fada itama a dan zafafe,sai kawai asma'un ta kewaye mummy ta fice da hanzari zuwa dakin aysha.
"Me kike da buqata mummy,da kinyi magana sai nazo basai kinzo da kanki ba" kai ta girgiza ranta na baci,a zatonta tana bacin rai ne saboda aysha sun rufeta,saidai abinda bata sani ba shine tana bacin rai ne saboda ayshan ta samu daukaka da muhallin da autarta bata samu ba,hassada kecin ranta ba tare data farga ba
"Wannan ai yafi qarfin kizo saidai ni nazo da kaina....godiya na taso takanas nayi miki,wato duk zaman da mukeyi dake da yadda muka riqeki ashe ke ba haka bane cikin ranki,kallon maqiyiyarki kikemin,kallon abokiyar adawarki abokiyar gabarki wadda bata son cin gabanki kike min,har ku hada baki da yaron nan ku rufe mana komai sai munje ganin jeranki sannan mu gani,kinsan mai arziqi ne baki gaya mana ba,amma ya zowa a sma'u a wanda baida komai saboda wani baqin nufi dake ranshi,ko ba komai da munsan waye ya bayyana kanshi xamuyi duk shirin daya dace yadda ba za'a ji kunya ba,to na gode da sakayyar da kika yimin Allah ya saka da alkhairi" ta juya tana shirin fita,iya qololuwar tashin hankali aysha ta shige shi,dama ita gwanar hawaye nan da nan ruwan hawaye ya soma layi a fuskarta,bata gane kan me mummyn ke magana ba,me take nufi ne ?batasan sanda ta isa gaban mummy ba ta tareta cikin kuka tana fadin
"Wallahi mummy ba mai kudi bane...talaka ne shima kamata,idan da mai kudi ne anty asma'u ita zata soma sanin hakan,tunda ita ta hadani da shi,ta hanyarta komai ya tabbata har kawo yau...ki tambayeta kiji" ta qarasa fada muryarta na sarqewa
"Ke dalla matsa....dake da asma'un dukanku lusarai ne...kada ma asma'un taji labari.....kunsan waye muhammad abdulhakim mai goro?,kunsan wanne irin arziqi ke gareshi,dukanku baku sani ba,cikin 'yan sa'o'in aka gayan wayeshi,aisha kin nunan iyakata kuma ina godiya" ta qarasa fada tana kewayeta gami da ficewa daga dakin.
Kuka aysha ta saki har sai da gwaggo asabe sake zaune tana kallon ikon Allah ita da mero suka taso suka riqeta gami da zaunar da ita,tsoro ne fal cikin zuciyarta,ta yaya zata shiga familynsa bayan ya soma dayi mata qarya?,a hakan zai roqeta?,a hakan zai cika alqawarin daya dauka,tana tsoro,tana tsoron faruwar wani abu,don me zai yaudareta,akanme zai ninketa yazo mata da siffar daba tashi bace,yanzu gashi ya hadata da mummyn,ya hadata da mutanen da suka zauna da ita da dadi babu dadi,ba kamar danginta da suka kasa zama da ita ba saboda wani banzan dalilinsu maras tushe wanda baici ace ya shafi rayuwarta ba.
"Ohni sadiya..wai wannan wane irin lamari ne haka yake faruwa?,indo wadanne irin mutanene haka kike zaune da su?,tunda muka zo daga wannan sai wancan?" Cewar gwaggo cikin bacin rai da tashin hankali.
Miqewa tayi tsaye ta dubi su mero
"Ina zuwa" ta fada kawai kana ta fice,da hijabin data idar da sallar azahar a jikinta don haka bata da buqatar sanya wani abun.
Parlourn daddy ta nufa kai tsaye,tayi qoqarin daidaita nutsuwarta sannan tayi sallama ta kutsa kai,su biyu ne zaune a falon shi da anty safiyya,da alama wata magana suka gama tattaunawa ko suke kan tattaunawar,dukkansu shuru sukayi ganin shigowarta falon,kai tsaye ta isa gaban daddy ta duqa tana hawaye
"Daddy don Allah ka kirashi ki bashi haquri ka gaya masa ka fasa bashi aurena,daddy bazan aureshi ba,bazan iya zama cikinsu ba" anty safiyya zatayi magana ya dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu sannan ya maida hankalinsa wajen aishan
"Saboda me?" Ya tambayeta
"Daddy....yazo min da siffar daba tasa ba,ya yaudareni daddy,wannan ha'inci ne daddy,a haka zanje na zauna da su?" Kasa daurewa safiyya tayi sai data furta
"Aisha,anso kashe rayuwarki ne Allah ya raya ta,an hadaki dashi saboda ana tsammanin bashi da komai Allah sai ya kaiki hannun mai komai din,wannan kadai bai isa ki godewa Allah ba?,wannan abun da kike fada tamkar butulcewa Allah fa kikeso kiyi"da hanzari ta daga kai tana kallon anty safiyya,akwai wani abu,akwai wani data sani kenan game da yadda auren ya qullu?
"Aisha" daddy ya kira sunanta bayan ya dakatar da safiyya
"Me yasa baki gayamin tun farko yadda abun yake ba kika ja bakinki kika yi shuru,kina zaton da an tafi a haka na hadaki aure da shi Allah bazai kamamu ba mu duka?"fada sosai daddy ya dinga yi irin wanda bai taba yi ba,alama ranshi ya baci sosai,kuka ta dinga yi tana bashi haquri,yace sam nauyin bakinta baiyi masa ba,haquri ta bashi da alqawarin ba zata sake ba,daga bisani ya kwantar mata da hankali da bata labarin farkon sanin daya soma yiwa khalipha a rayuwarsa.
"na sanshi can shekarun baya masu yawa ta sanadin faduwar jakar kudadena,kudade ne masu yawa wanda banda kudaden akwai muhimman takarduna harda na kamfani na,sosai na shiga tashin hankali a sannan,saboda matuqar kudaden suka bace a sannan tsaf zan iya shiga talauci bana wasa ba,cikin ikon Allah kwanaki uku da faruwar haka aka kira wayar kamfani na akace ni ake nema kan kudina dana yar,nayi murna sosai na buqaci inda zanje mu hadu da wanda ya tsinci kudin,ba bata lokaci ya bani adress din gidansu,yace nayi haquri,yana da wani uzuri ne da baya barinsa ya fita daga gida da da kansa zai kawomin,nikam a sannan kota kan hakan baibi ba,saboda ko a qafa yace min na tafi wata qasar na amso zuwa zanyi
Sanda na isa gidansu nayi matuqar mamaki,gashi dai gida har gida irin ginin masu kudi da wadata na sannan amma kana masa kallon farko zakasan babu da talauci ta tasamma yi masa raga raga,mamaki na bai sake qaruwa ba sai dana shiga na tadda matashin dan shekara ashirin na jiyyar mahaifiyarsa magashiyyan rai a hannun Allah da qannenshi maza guda biyu,kana kallonsu kasan kuka suka gamayi dukansu,sanda na amshi kudin na tambayeshi nawa yakeso ga mamakina sai yace min babu komai,alfarma daya yake da buqata na biya kudin aikin mahaifiyarsa ta rabu da zafi da radadin ciwon da take fama da shi,na zaci zai buqaci sama da haka,amma sai yace min buqatarsa kenan,matsanancin ciwon suger take fama da shi wanda shi har takai ga ya taba mata qoda za'a mata aiki.
Muna tsaka da wannan maganar saiga 'yan sanda katsama kanmu,miqewa naga khaliohan yayi yayin da suka yo kanshi kamar kura ta samu nama syka cukuikuyeshi,yayin da yajeta rantsuwa yana fadin bashi bane,matashi dake bayansu yana cewa
"Karku saurara masa,qarya yake ku dakeshi"ni na miqe na musu magana,sannan na tambayi ba'asi,nan dan samdan yace ana tuhumarshi ne da yiwa yarinyar wan babanshi fyade,kuka yake sosai a sannan yana rantsewa da duk abinda yasan me girma ne kan bashi bane,yanayin nagartar yaron ya sakamin tantama kan zancan,naja daya daga cikin 'yan sandan waje nace ya gayamin gaskiyar magana,na masa alqawarin kudade mai tsoka,nan yace ba shakka bashi bane,amma alhj idris da yaronshi ibrahim su suka biyasu kan kada au saurara idan sunzo su kamashi,daga nan su kaishi kotu ma birsin sukeso yayi,don ya matsa kan maganar gadonsu,a take na gaya masa sunana sai yayi sororo,na kira sauran 'yan sandan na sallamesu duka da wani abu,nan ibrahim yahau min hauka,nace koya wuce kona makashi kotu kan ya yiwa khalipha qazafi,haka ya wuce don kada allura ta tono garma,kuka sosai ya dinga yi mahaifiyarsa dake kwance tana tayashi,haka qannensa maza guda biyu,a sannan naso jin labarin rayuwarsu amma sai naga bashi yafi muhimmanci ba,lafiyar mahaifiyarsa itace gaba,muka je asibitin na biya duk wani abun da za'a buqata a aikin,hatta da abincin da ita da su zasu ci,cikin nasara akayi aikin aka gama lpy ta kuma samu sauqi,ina da niyya da shirin taimakon rayuwarsu tafiyar gaggawa ta sameni russia,wanda ban dawo ba sai bayan watanni shida,dana dawo su na soma nema sai na tadda sun saida gidan sun tashi,kuma ba'asan ina suka koma ba,dole na haqura da neman nasu naci gaba da saka yarona addu'a,don gaskiya nasp na riqeshi d'ana,saboda gaskiya amana da hankali da nutsuwar da naga yana da ita,uwa uba yadda naga yanason mahaifiyarshi yana tattalinta,nasan lallai sai yaro na gari ne kawai zai hada wannan nagartar"
Dukansu shiru sukayi suna jinjina labarin,yayin da zuciyar aysha ta soma kuma rabuwa gida biyu,
"Kije kici gaba da addu'a ina da tabbas kan khalipha aysha...Allah ya baku xaman lafiya" anty safiyya ce ta amsa ayshan ta miqe cikin sanyin jiki tabar falon.
Sosai ranta ya dinga baci,hassada nacin ranta ba tare data sani ba,ta yaya ma aysha zata samu irin wannan gidan?,wayarta ta ciro ta soma neman tsohuwar lambarsa da suke waya,so take taji ta bakinsa,so take taji dalilin raina mata wayon da yayi tunda fari,saidai amsa daya ake bata is switched off,gani take ma kamar akwai wata a qasa,kaman ayshan ita ta shirya komai,wani irin gumi take ita kadai qwaqwalwarta na kaikawo,hakan ya sanya ta tashi don fitowa daga dakin sukayi kacibus da mummy a bakin qofa,duban asma'un tayi
"Kina jin sunan muhammad abdulhakim mai goro?" Kai asma'un ta kada,sosai ta sha jin sunan ko a bakin hamid ma
"Shine khalipha yaron da zai auri aysha" cikin qanqan da idanu take duban mummy,kamar tana zaton mummyn zata sauya zancan data gaya mata
"Mummy da gaske?"
"Ina wasa dake?" Ta fada itama a dan zafafe,sai kawai asma'un ta kewaye mummy ta fice da hanzari zuwa dakin aysha.