← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 81 OF 114

Sashe 81

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A bakin layi anni ta sake yanke shawarar suje gidan habibu,sam bayaso yayi musu da ita,hakan ya sanya baice mata komai ba suka kama hanya a qafa,duk da nisan dake tsakanin gidajen haka suka taka har gidan,tun daga yanayin yadda matar gidan ta tarbesu farkon zuwan gidan nasu sukasan cewa akwai babbar matsala,tunda khalipha yaga yadda yaran gidan ke sangarta yasan tafiyarsu ba zata taba dai dai ba,tunda suka je aka zubesu a falo ba wanda yabinta kansu,har aka gama girkin rana a gabansu yaran suka baje suka ci abinsu ba wanda ya basu koda loma daya,a sannan hajar ta soma yatsina fuska tana radawa anni cewa yunwa takeji,haquri annanin ta bata saboda tasan cewa da zarar khalipha yaji ba zaman lafiya saiya samo ya bata,wata iriyar qauna da shaquwa ce tsakaninsa da ita fiye da sauran 'yan uwanta,tun tana yi a boye har khalipha ya fuskanci abinda ke faruwa,tunawa yayi duk cikinsu babu wanda aka yiwa iyaka da abincin gidansu a sanda suke dashi idan sunzo,daga babba har yaro idan yaje kanshi tsaye yake wucewa ya zabi kalar abinda yakeso a dafa masa,sai kawai ya nufi kitchen din gidan da kanshi,yarinyar gidan ya taras (zeenart a sannan)da mai aiki tana dafa mata indomie,ya tambayi mai aikin abinci,budar bakin yarinyar sai cewa tayi
"Ba za'a bayar ba makwadaita kwadayayyu" ta fada tana murguda baki,zuciya ta tasowa khalipha yayi yunqurin danneta sabida fadan anni daya fado masa,sai ya zari plate kawai ya bude tukunya ya zubo abincin ya fito,aikuwa ta biyoshi tana ihun barawo,umma ga barawon abinci bawai kuna don batasan khaliphan ba,kawai tsabar rashin tarbiyya ce.

Mai gidan da tunda sukazo akace musu yana barci bayan sunsan tabbas yaji zuwansu shi ya sauko daga samanshi yana tambayar zeenart din ya akayi
"Alhaji zuwa yayi har kitchen ya diba mana abinci" hannu yasa ya wafci abincin yana rufe khaliphan da fada
"Wannan wanne irin sakarcin banza ne da wofi,saboda tsabar rashin tarbiyya har takai ka dauki abinda ba naka ba ba'a baka ba?,to ni wannan iskancin ba'a gidana ba" haquri anni ta soma bashi khalipha na kallo zuciyarsa na tafasa,sai daya mula don kanshi yana hura hanci yasa aka basu daki,abinci ko yace saidai su jira na dare,saboda bacin rai khalipha wuni yayi a waje bai zauna agidan ba,ba laifi wunin da yayi a waje yayi masa rana,don neman kudi yayi sosai,bai dawo ba sai bayan sallar isha'i,ya shigo gidan a matuqar gajiye,cikin tausayawa anni ke dubanshi,qwalla ce ta cika mata idanu amma saota maida saboda tasan yanzun hankalinsa zai tashi,tuna tsantsar gata da suka samu daga mahaifinsu take,amma yau rana daya rayuwa ta juya musu baya cikin qiftawa da bismillah,dubansu yayi daua bayan daya,ya tambayi kowa lafiya ko suka amsa masa da eh,awara ya ciro mai zafi ya miqawa kowa tashi,saidai ta 'yar lelen tashi hajar daban take,ya qara mata da goba irin manyan nan da yaga tana yawanso,ba qaramin dadi suka jiba kuwa,anni ta dauko wani ragowar abinci cikin kwano ta tura gabanshi
"Ga naka abincin nan kaci mu munci namu,hala ma fushi kake damu tunda ka fita baka dawo ba sai yanzu" murmushin yaqe yayi yana amsawa da annin da a'ah,tunda ya kalli abincin yasan cewa ba qoshi sukayi ba,saboda haka ya juye tashi awarar akai yace kowa ya matso yasa hannu suci abincin yafi albarka.

Da murmushi anni ke dubansu sanda suke cin abincin,ta dago wayon khalipha,zuciyarta cike da tausayinsu da kyakkyawar addu'a da kuma fata da data dinga binshi dashi,ta tabbatar cewa Allah ya bata jarumin d'a,daya tamkar da dubu.

*mrs muhammad ce*

*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
44

Duk da cewa bai tashi a wahala ba bai kuma saba da ita ba amma data riskesu yasa hannu bibbiyu ya karbeta,ya kuma shiga bilhaqqi da gaskiya yana qoqarin ganin farinciki da walwalarsu
"Anni kema kici" khalipha ya fada yana dubanta,kai ta girgiza
"Kuci khalipha,ni cinku shine kwanciyar hankalina" sai shima ya tsame nashi hannun yaqici,sai data lallabashi da qyar sannan ya maida hannun nasa,a hakanma kusan sai suyi loma uku baiyi daya ba.

Zamanta a gidansu zeenart shima dai zama ne maras dadi,zaman qunci da takura,wulaqanci kyara da tsangwama,rashin kunya fitsara da sangarta babu wanda anni bata gani ba daga wajen yaran gidan,tsana da kyara qarara,yayin da khalipha ya dage ta wani fannin,duk hanyar da yasan zai samu kudi indai ta halas ce zaiyi komai kashinta,baida girman kai lalaci ko son jikinsa,amma da yake qasar tamu ga yadda ta zama samun sai addu'a kawai,ana samun amma da qyar,hakanan abinda ake samun bai taka kara ya karya ba,da haka ake jalautawa rayuwar yau fai gobe tsumma.

Barinsu gidan shima sanadiyyar sharrin sata da matar gidan ta dorawa anni,dukka yaran kuma suka dorar da cewa eh sun ga sanda annin ta dauka suna daki ta zaci bacci suke,haka aka musu korar kare a sannan khalipha baya nan ya tafi neman kudinsa,a qofar gidan suka wuni da kaya a gabansu,ga yunwa baci ba sha,sai yamma lis ya dawo ya samesu zube a wajen,cikin gigita ya qaraso wajensu yana tambayarsu
"Anni....lafiya?,me kike anni a waje?,kalli kayanki yadda sukai qura?,wadan nan kayanfa anni ke zakuyi dasu?" Murmushin qarfin hali ta soma saki duk don ta kwantar masa da hankali,haidar da shima ranshi ke bace tun a sannan shi ya shaida masa komao,cikin wani matsanancin fushi ya durfafi gidan gaba daya jijiyoyin kanshi sun tashi saboda bacin rai,cikinnzafin nama anni ta damqoshi,da qyar da iya tsaidashi
"Indai na isa dakai karka taka musu gida,ka wuce mu tafi" tilas ya dakata,saidai zubewa yayi a wajen ya saki kuka,yau ya kasa daurewa,bacin ran dake cin zuciyarsa yayi yawan da bazai iya daureshi ba a yau,hajar ita ta taso tana kuka ganin khaliphan na kuka,ta iso gabanshi ta soma share masa hawayen fuskarshi,kallonta yake rausayinta na kamashi,idan duk su maza ne zasu iya daurewa rayuwa,zasu iya rayuwa koda babu kayan more rayuwa babu qyale qyale ita kuma fa?,ta soma zama budurwa amma babu duk wani kayan alatu kona qyale qyale irin wadda diya mace keda buqata tattare da ita,bayason kukanta ko kadan,sai ya sakar mata murmushi yana riqe hannayenta,miqewa yayi tsaye ba tare daya ce da kowa komai ba ya isa gaban kayansu,ya goya daya ya riqe biyu a hannayensa yayi gaba,shi kadai yasan me yake ji cikin qirji da zuciyarsa,takawa ya soma yi zuwa bakin titi wanda hakan ya sanya suka bishi da sauran kayan.

Mota ya tsare musu,yana fadin sunan unguwar da zasu anni ta dubeshi,yana nufin zasu koma gidansu su zauna ne
"Khalipha,kanaso mu koma gidanmu kenan?"
"Allah yana sane damu anni yana kuma tare damu,mutanen nan dukkaninsu babu wanda zai iya riqemu,babu wanda ya tuna da halaccin abba a garesu sanda yana raye dai dai da rana daya,komawarmu gidanmu shine gata na farko da zamu yiwa kanmu" bata sake tankawa ba,duk da qarancin shekarunsa amma yana da zurfin tunani da kaifin hankali.

Tamkar kango haka gidan ya koma,babu komai a cikinsa,basusan wanda ya shigo ya kwashe sauran furnitures din dake cikin gidan ba,amma koma wane duk yadda akayi yana da spare key din gidan,duba da yanayin ginin gidan gini ne irin na masu kudi mai cike da security,ba yadda suka.iya haka suka gyara sauran abinda ya rage a gidan,suka hadu suka share gidan tas,abinda basu taba ba bazasuma iyaba saboda girmansa masu aiki ke musu,amma yau babu ko mutum daya daya zauna dasu cikin ma'aikatansu kowa ya kama gabanshi.

Khalipha shi yaci gaba da daukar dawainiyarsu,ya hana annin yin komai,duk wani aikin qarfi kona wahala yana ciki,saidai kuma qoqarin nashi yana gazawa,sakamakon dan abinda yake samun bai taka kara ya karya ba bazai wadacesu ba,nan da nan wahala ta sake bayyana muraran ajikinsu,kana kallonsu kasan yunwa ta samu gindin zama a jikinsu,ba'a maganar sutura dama ko karatu duk wannan tuni ya jima da fin qarfinsu,dole anni ta soma sana'a itama,wanda wankau ne zuwa daka,sai ya zamana ba'a samu sosai saboda yanayin yadda unguwar tasu take,uwa uba ma duk wanda ya kalli gidan nasu daga waje zaiyi dariya ne kawai yace rainin hankali akeso a yiwa mutane,jama'ar dake da gida irin wannan me zai kaisu yin wankau ko daka?,hajar ita ke fita maqotan unguwanninsu tana amso musu wankin ko daka ba tare da sanin khalipha ba,ranar daya sani din kiwa kwanan bacin rai yayi,yayi kuka yayi kuka har yaji babu dadi,kanshi kawai yake tuhuma yana ganin kaman qoqarinsa ya gaza,bayan kuma duk wani qoqari yana yinsa,duk wani aiki daya fado hannunsa matuqar bana haram bane to zaiy ya sama musu abinda zasuci koda kuwa kwasar kwata ne,ita kuma anni tausayinsa take,tana ganin wahalar da yakeyi tayi yawa,dalili kenan daya sanya ta kama sana'ar.

Tafi tafi sai aikin qarfin ma ya zama sai kana da hanya ko.kana da wani daya sanka,zaman gida saiya auri khalipha,yanaji yana gani gidan block din aljh idris yayan mahaifinsa yaje neman aiki suka hanashi,anni ita ta bashi shawarar yaje ya sameshi a gida suyi magana wala'alla yasakasu su daukeshi,da fari yaqi saboda shikam ya sare da halayyarsu gaba dayansu ya aje ta tasu a gafe,musamman alhj idris da dukkansu ya fisu mugun hali,daga bisani ne ya amince don baisan me annin ta hango ba.

Randa yaje din yayi kusan awa biyu yana jiran idris din bai bada umarnin ya shigo ba,sai daga bisani ne yaronshi ibrahim wanda baifi shekara daya ya baiwa khalipha ba yazo ya kirashi suka shiga falon alhj idris din tare
"Cire takalmanka mana malam" ibrahim din ya fada yana katsawa khalipha tsawa,dubanshi khalipha yayi donshi nashi takalman na daure a qafarshi bai cire ba,sai a sannan ya lura,takalmi ne da abbanshi shi ya siyo musu,kudinsa yakai dubu talatin ya dauka ana khaliphan ya baiwa ibrahim daya,nashi kam ya dade dacin kasuwarshi a lokacin da hajar bata da lafiya,basu da kudin magani babu dalilinsa ya saida ya siya mata magani,dama ba wani tayi arziqi suka masa ba kwata kwata dubu goma aka sayeshi.
Chapter 81 · 0% Book details