← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 114

Sashe 19

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Sosai yayi murna da zuwan bazatan da khalipha yayi masa,sun jima suna hira har haidar ya qosa ya fice acewarsa zai shiga capteria yaci abinci kafin su gama,don baiyi breakfast ba suka fito
"Saika dawo...amma karka bata mana lokaci,muna da abubuwan yi da yawa da muka baro a company ka sani"
"Zan dawo da wuri in sha Allahu" ya fada yana fita da dan sauri yana wulga qafarshi kamar zaiyi ball da wani abu.

Ita daya ce zaune saman table din,hannunta riqe da littafi tana dubawa,duk da rabin hankalinta na wajen aliya data zaunar da ita a wajen,kwata kwata zata iya irga yawan zuwanta wajen,don sam ba wajen zuwanta bane,jinta take duka a takure.

Bata ankara ba taji fallatsowar abu ta gefan fuskarta zuwa hijabin jikinta mai sanyi,da sauri ta daga kai dai dai sanda haidar ke fadin
"Subhanallah....sannu don Allah" sosai lemon ya bata jikinta,amma ba wannan ne ya dameta,ta handout dinta take,ganin bata dubeshi ba ya sanyashi sake cewa
"Am sorry pls madam kiyi haquri don Allah,wallahi ban sani ba...."
"Babu komai..." Ta fada cikin hanzari tana miqewa ganin yadda hankula suka soma dawowa kansu abinda bata so kenan
"La la la.....aysha garin yaya?" Aliya dake takowa zuwa wajen ta fadi tana duban haidar dake tsaye cikin rashin jin dadi,sam aysha bata kula da ita ba da tuni ta tareta,saboda sarai tasan halin aliyan
"Bai sani ba aliya...muje kawai" ta fadi tana son janye aliyan
"Amma dai malam baka kyauta ba....duba yadda kayi mata da jiki fisabilillahi"
"Aliyaaaaa....bai sani ba ya kuma bada haquri...muje don Allah" ta fada tana janye da hannun aliyar
"Am so sorry kiyi haquri" ya sake fada yadda zata jiyo
"Is ok" ta amsa ba tare data waiwayo ba,sauke ajiyar zuciya yayi bayan yaga sun fice,duk da aliya saidata juyo ta watsa masa harara,sam bai zaci zatai sauqin kai haka ba,yayi mamakin yadda ta nuna babu komai cikin sauqi tayi tafiyarta,dama har yanzu akwai yammata irinta?,komawa ya sakeyi reception ya sake order din wani abun shan yace su hado masa da abincin da yace yana so.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶

Zaune take gaban daddyn tana sauraron bayaninsa,wanda batasan daga inda aka samo wannan hikayar ba
"Badon mummynki ta ankarar da ni ba aysha ai zan tsammaci kin aminta da ahmad dinne....tunda dai haka ne babu takurawa zan musu bayani su janye...Allah ya kawo miki wani na gari ya hada hankulanku waje daya" amsa masa kawai da amin,don bata da wani abin cewa,miqewa tayi zuwa dakinta tana jujjuya maganar daddyn,hakanan taji babu dadi har ranta,ita dai abinda ta sani batayi maganar kowa da ahmad ba baya ga aliya,bata ce tana so ko bata so ba,a daren abun ya dan dameta,amma da yake ba wani sanyashi tayi can cikin ranta ba zuwa safiya ta rage tunawa da abun,ta saka karatunta a gaba,wanda yake final exam ce suke dab da fara zanawa.

Wannan abu shi ya kusa kawo baraka tsakanin mummy sa'adah da mummy laraba,mummy sa'adah taso wanke kanta,amma da yake ba abinda mummy laraban bata sani ba na mummy sa'adan kallonta kawai tayi,hakan bai hana ahmad ci gaba da kiran ayshan ba.

Cikin wata guda suka kammala jarabawarsu,komai yazo mata a saqi fiye da yadda ta zata,saidai ba abun mamaki bane hakan saboda ita kanta tasan ba qaramin karatu tayi ba,sai fatan samun sakamako mai kyau ta yadda zata samu damar dorawa daga inda ta tsaya

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶

Qarfe biyar da rabi na yammacin ranar,tana kan hanyarta ta dawowa daga gidan anty halima babbar diyar mummy data aiketa,bata wani jima ba ta dawo don sam babu sabo ko sakewa tsakaninta da ita,saboda kusan halayyarta daya da asma'u,abinda ya rabasu kadan ne,kusan photocopyn ta ce asma'u.

Dan uban horn aketa maka mata tunda ta sauka daga napep ta gangaro layin su,a dan sace ta waiwaya,mota ce qirar pilot baqa wul,tun daga glasses har jikin motar baqi ne,sheqi kawai take da daukar ido,tsoro ne ya kamata saboda yanayin layin nasu da bai cika jama'a ba,hatta da habu mai trader da ba'a rasashi qofar gidan da yake aiki yau baya nan,hakan ya sanyata qara dan uban sauri cikin yunqurin isa gida ko zata samu ta tsere,saidai haqanta bai cimma ruwa ba,tana dab da qofar gidan ya samu nasarar tare mata hanya,cak ta tsaya tana maida numfashin tsoro har zuwa sanda mamallakin motar ya bude ya fito,matashin saurayi ne wanda kallo daya zaka masa kasan kudi ilimi da hutu sun ratsashi yadda ya kamata,sanye yake cikin dinkin shadda jamfa da wando kanshi babu hula,fuskarsa dauke da murmushi ya zagayo inda take tsaye
"Kinga na kamaki babu inda zaki kuma guduwa tunda kinqi tsayawa" tsoro ne ya sake kamata,ya kamata kamar yaya,idanunta ta dan zaro tana satar kallon gefe da gefenta ko zata samu wanda zaya ceceta,mahaukacin horn din da aka danna daga bayansu wanda ko qarar tahowar motar ita bata ji na ya sanyata zabura saboda tsoro,waiwaya sukayi duka su biyun ita da wanda bata mako san sunanshi ba suna dubanta,asma'u ce ta fito,tana sanye da doguwar riga ta atamfa mai gajeran hannu,wuyanta nannade da dan qaramin mayafinta,yayin da qafafunta ke saye da hillshoes,glass din fuskarta daya kusa mamaye rabin fuskarta ta zare tana dubansu tare da takowa inda suke
"Hafiz....." Ta ambata da alamun mamaki,bai amsa ba kuma baida niyyar amsawa,don shidin ba wani ganeta yayi sosai ba
"Ke aysha me kike a nan....dalla wuce gida" ta fada cikin hargagi,daman jiran hanya take,sam tsaiwar bata yi mata saboda rashin sabo,saboda haka da hanzari ta nufi get din gidan ta tura ta shige,ajiyar zuciya ta sako sannan taci gaba da takawa a hankali zuwa ciki.

A falo ta tadda mummy zaune cikin lesukan da take saidawa
"Kin dawo?"
"Eh na dawo mummy....tana gaidaki"
"Lafiyarki qalau kuwa?"ta fada tana qare mata kallo
"lafiya lau" ta fadi tana miqa mata kudin data ciro daga jakarta ta soma yi mata bayani.

Suna tsaka da lissafi asma'u ta fado falon tana huci
"Mummy....ki jama yarinyar nan kunne,tana neman ta janyowa kanta abinda yafi qarfinta don bazance yafi qarfinmu ba" maida hankalinta mommy tayi kan asma'un tana dubanta
"Wani abu ne ya faru?"
"Sai data zauna ta jefar da jakarta gefe sannan tace
" kinsan da waye na gansu a tsaye kuwa?"
"Waye ne?" Mummyn ta sake tambaya tana yatsina fuska idonta kan asma'un
"Fahad mummy dan gidan IG fa?,batasan bata kai can ba?,zata debo abinda zaya zo yafi qarfinta,koda yake ita daya zaya dama wallahi,ke har kin isa tarayya da maza irin hafiz?,kinsan yawan matan dake sonshi,kyau da kudi?" ta qare maganar tana duban aysha da wani wulaqantaccen kallo,ajiyar zuciya mummy ta saki wanda ke nuna bata zaci abun baikai can inda take tunani ba,yayin da aysha ke rabe zaune a gefe guda kanta na kallon qasa,gaskiyar asma'u zalla take gani cikin maganganunta,gaskiya ne,ita din ba kowa bace,ita din batakai matsayin kowa ba,don me zata tsaya da wani?,don me zata tsaya da wanda ya amsa sunan wani?,to amma abu daya ya kamata a mata uzuri a kai,bata bashi dama ba,bata kuma saurareshi ba
"Ko aure zaki indo baki kai ki auri dan gidan IG guda ba,ko yace yana sonki bai san ainihin wace ke ba,koda ya sani kuwa to yaudararki yake.....ki bari miji dai dai ke yazo miki amma ba irinsu hafiz ba,don wannan yafi qarfin kanki" ta rufe maganar tana bayyana inda ta dosa kai tsaye daga qarshe
"Allah ya kyauta...ke saiki kiyaye" cewar mummy tana ci gaba da lissafinta,gefe guda na zuciyarta tana ganin dacewar abinda asma'un tayi
"In sha Allah" shine kawai abinda tace tana miqewa hadi da daukar jakarta ta wuce daki.

Kallo mai kama da harara asma'un tabi bayan ayshan da shi,taso tattauna zancan da mummyn amma sai ta fuskanci hankalinta na kan business dinta,bata wani tsawwala ba ta wuce nata dakin tunda ta cika burinta.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶

Yammacin ranar lahadi ne wanda yake dai dai da kusan watanni uku da kammala jarabawarsu,sanye take da riga da skert na atamfa brown wadda aka yiwa ado da yarfin yalo,hijabi ne a jikinta wanda ya sauko mata iya gwiwarta,fuskarta babu adon komai sai powder da man lebe data shafa bayan ta kammala yiwa daddy da ya yini yau a gida abincin dare,ita daya ce zaune cikin lambun gidan saman wani lilo dake daure tsakiyar shukokin dake cike a wajen,sosai takeson wajen yana kuma burgeta,yana debe mata kewa ba kadan na,takan iya shafe tsahon a wanni a wajen ita daya bata komai sai tuna rayuwarta mataki zuwa mataki,har zuwa bigiren da yau ta kawota kai,sau tari idan aka nemeta aka rasa cikin gidan to tana maqale ne a wajen,wajene da mutan gidan basu damu da shi ba,ta alaqanta hakan da basu san sirrin dake wajen ba da irin ni'imar daya tara ba,yakan tuna mata rayuwarta ta qauye sosai,duk da cewa ba wani abun burgewa sha'awa ko dadi a ciki da zata iya dorarwa,a yanzu ma lilawa take kadan kadan,idanunta na kafe waje guda tana kallonshi,wayarta dake saman cinyarta tana fidda sautun karatun kitabuttauhid na malam ja'afar mahmud adam,ta nutsu sosai tana jin karatu hadi da fahimtarsa kamar tana gaban malamin,mayyar karatun addini ce,tana da bibiya da kuma kiyayewa,babu wani karatu da idan tana saurararshi yake sakata nishadi irin karatun addinin islama,kada ma ace hadisi take saurara,wanda yawanci tafi son taji karatun Dr ahmad BUK.
Chapter 19 · 0% Book details