Sashe 106
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Washegari khalipha ya dawo bayan sallar azahar,don abba yazo tunda safe ya gansu ya wuce masallaci,a sannan aysha na ramuwar bacci ummi ta tasheta tace maza taje,haka ta dauraye fuskarta ta fita harabar wajen da yake zaune,idanu ta zuba mata wani abu na tsirga masa harta qaraso inda yake,ji yake kaman ya sureta,yana kallonta yasan bacci take aka tasota,saiya narke mata tun kafin tayi magana
"Wato an samu ummi an manta dani ko?,ba saqon saoda safe,ba saqon barka da safiya,babu na barka da rana,shikenan na gode...kice kawai ba zaki iya kula dani ba tunda kin samu ummi na auro wata kawai" har cikin ranshi da wasa yake,amma abun mamaki saiga qwalla aisha ta fara,abunma kamar yayi dariya amma ganin da gaske kuka zata mishi saiya daure,bai taba zaton yadda ake cewa masu suna aysha nada kishi sosai gaske ne ba kamar yanzu,da qyar yasha kanta,saiya koma seriouse dinshi sosai
"Ki shirya anjima zanzo ki rakani inyi wata siyayya" kai ta langabar
"Ya khalipha....ban gaji ba da ganinta"
"Rakiya nace zakimin ai ko?" Kai ta gyada
"Shikenan" kadan suka taba hira ya wuce shima masallaci,saboda addu'a yakeso yayi yau sosai kan rayuwarsu shida ayshan,harkokin kasuwancinsa,iyaye da 'yan uwanshi.
Gab da magariba ya dawo,yayi kyau sosai cikin shigar larabawa jallabiyya baqa harda hirami,ita kuma ta sanya abaya maroon da baqin niqaf bayan ta nade kanta da mayafin abayar kai kace hijabi ta saka,kallonta yake saboda wani kyau data yi masa,idanuwanta da suka fito ta tsakiyar niqaf din kamar an qara musu girma da kyau,tun a lokacin jikinsa gaba daya ya amsa har cikin zuciya tuhi da gangar jiki,duk wani kuzarin daya taho dashi ya bace,a haka suka lallaba masallaci sukayi magarina da isha'i sannan yace ta fito su tafi.
Katafaren shagon saida kayan ado ne na mata,binsa tayi kawai da kallo sanda ya nufi bangaren kayan bacci bayan ya gama siyan turaruka masu dan karen kyau da tsada,tana kallonshi don yace ba ruwanta ya dinga zaben kayan bacci kala kala,sai daya dauki wajen kala goma dukkansu babu mai qaramin kudi sannan ya biya suka wuce.
Wani shagon suka sake tsayawa nan gaba da wajen kadan,gwalagwalai suke siyarwa,kana ganin yadda suke gaisawa da bashi qima kasan babban custumer ne,hakanan akwai alamun sabo sosai tsakaninsu,kujera yaja mata yace ta zauna,sample aka kawo mata kala kala na sarqa da dan kunne,zobe da banguls khaliphan yace ta tayashi zabe,ta tambayeshi guda nawa yace kowanne bibbiyu,tana zaton anni ko wani zai saiwa saboda haka ta zage ta zabi masu kyau,ita kanta sun bala'in burgeta,basu dade sosai ba ya biyasu sukayi sallama suka fita.
Daganan wajen saida kayan maqulashe ya tsaya shima,yayi siyayya sannan suka shiga motar suka wuce,ta dan gaji hakanan ga kewar ummi,Allah Allah take su isa ya ajeta ta ganta sannan ta huta,sai taga dirven ya dauki wata hanya daban,ba ha yar hotel din da suka sauka ba,hakanan ba hanyar hotel din su ummi ba,dubanshi tayi
"Ina zuwa kuma ya khalipha"
"Masauki zamu koma nayi kewarki uwaisha....kiyi haquri gobe saina maidaki wajen ummi,ni kadaine bana jin dadi" batason bata masa dai dai da rana daya,duk yadda taso ganin ummi saita kada masa kai kawai,sai a sannan ta tuna ma yace mata dama kwana daya zatayi,amma batasan ba zata dawo ba data sake magana da ummin.
Area ce mai wani irin kyau mai kwantar da zukata,hakanan hotel din shima kansa tun daga gininshi da tsarinsa kasan na musamman ne,bata sake tabbatarwa ba sai da suka shiga dakin,duk kayansu yana ciki a shirye,shi ya maida qofar ya sanya muqulli ya rufe,haka kawai a ji jikina yayi sanyi,ta daga kai ta dubi khalipha dake kallonta yana murmushi
"Dakin yayi miki?,ko mu sauya waje?" Murmushu tayi mai sanyi sannan tace
"Sosai ya khalipa"
"Wayyo Allah" ya fada yana aje kayan siyayyar hannunshi,don bai barta ta dauki komai ba kamar yadda bai bar wani ya dauka musu ba
"Wanka da alwala....wazai fara ni koke?" Idanu tadan fiddo
"Ya khalipha...nikam haka zan kwanta bana jin yin wanka"
"No...dole kiyi,so kike ki zama qazama?" Ya fada yana kada kanshi,haka kawai take jin fargaba,saboda kallon da khaliphan yake mata saitake ganin kamar ba wanda ya saba yi mata ba,saita noqe kafada
"Toka fara yi sannan ni" hannunshi ya ware
"Well,hakan yayi" jallabiyar jikinsa ya soma zamewa,saita dan rintse ido kamar yadda ta saba,yana kallonta saidai wannan karon dariya ta bashi,ya qunshe abarsa yana kada kai ya shige toilet din.
Kaman yadda ya saba aqalla yana daukan minti talatin sannan ya fito,tayi wuf ta shige bandakin ganinsa daure da dan guntun towel yau sabanin da da yakan sanya rigar towel,sanda take qoqarin rufe qofar ya sanya hannu ya tokare qofar ya rufa mata baya
"Ya khalipha....don Allah" saita gaza qarasawa ganin ya cimmata ya kaita bango,ya mata rumfa gaba daya,tsoronshi da kwarjinsa wanda bata taba jiba yau ya kamata,so yake lallai ta kalleshi amma taqiya,nunfashinsu ya dinga cakuduwa da juna,murya can qasa yace daita
"Wannan saurin da kike kika fada toilet duk na meye,to sai kin nunamin abinda kike tsoro" kamar zata sanya masa kuka take masa magiya
"Babu komai don Allah kayi haquri,nidai babu komai" wani murmushi ya saki wanda shi kadai yasan ma'anarshi ya janye baya yana cije lips dinshi,saiya nufi famfo ya sake daura alwala sannan ya juy ya dubeta,har yanzu tana tsaye inda ya ritsata
"Kiy sauri ki fito na baki minti goma,idan ba haka ba,zan shigo na daukoki ko baki gama ba"murmushi tayi a kunyace,juyawa yayi ya fice sannan yaja mata qofar toilet din.
Sanda ta fito tuni yana saman abun sallah,sanye da jallabiyya fara qar har daukan ido take,kansa saye da hula tashi ka fiya naci baqa,dakin ya bule da wani irin sassanyan qamshi,wani kyau taga yayi mata sosai,don karta shagala da kallonsa saita kauda kanta,riga ta gani aje ta bacci da kuma after mai kauri gefanta,girgiza kai tayi sanda taga yadda rigar take,amma data tuna zata dora after din saita dauka ta koma bandaki ta shirya acan,ta mulke jikinta da wani turare daya aje mata wanda qamshinsa da dadinsa ya dinga sanyata kasala.
Binta yayi da kallo sanda ta fito daga bandakin,sai yayi mata nuni da gefansa,matsawa tayi ta saita sahu yadda ya dace ya kabbara sallah cikin mamakin sallar meye itama ta tayar,raka'a biyu sukayi sukayi sallama,yaja doguwar addu'a sosai wanda ke tattare da roqon dukkan alkhairi sannan ya shafa,jiyowa yayi ya zauna yana fuskantarta gami da tanqwashe qafa,janye idanunta tayi daga nashi tana jin zuciyarta na bugawa,wata fargaba na shigarta,sunanta ya kira wanda ya sanya ta daga kai ta dubeshi,a nutse yake mata tambayoyi game da abinda ya shafi addininta,sallah tsarki da wanka,kada kai kawai yake yana gamsuwa da bayaninta,kai karantse wata malama ce,sai data kammala sannan ya dora hannunshi ya karanta addu'ar nan da annabi ya umarcemu ga duk wanda Allah ya horewa yayi wani sabon abu,ko mata ko abun hawa,har ya gama tana saurarenshi,hannunsa ya sanya ya janyo ledar dake gafansa wadda suka siyo kayan ciye ciye a ciki,ya fidda komai ya aje a gabansu,itadai nata ido jiki a salube,donta shinshino wani abu,da kanshi ya dinga ciyar da ita,duk da taso ta turje da farko yayi kicin kicin ya nuna yayi fushi,cikin hikima ya dinga janta da hira wanda ya sanyata ta sake,sai gata tana qyalqyala dariya,bayan sun gama ita ta gyara wajen kafin ta kammala ya haye gado abinshi
"Malama a cire hijabin nan da after din mana haka?,banfa ga kwalliyar ba" sai ta dan diririce kadan saboda tuna yanayin rigar dake qasa,girarshi ya dage mata
"Yes....ko so kike nayi asarar kudina?" Ya fada yana zuba mata idanu,hakanan ta dinga fidda kayan kunya na saukar mata,sai daya ragw saura rigar baccin kawai,zuwa sannan numfashinsa ya soma masa nauyi,tunda Allah ya halicceshi bai taba ganin sura irin haka baka,ashe ayshan ta zarta dukkan yadda yake tunani,hannunshi ya miqa mata yana daga zaune saman gadon,bayanshi jingine da fuskar gadon qafafunshi miqe
"Kai zo nan muga wani abu....ya maqale miki a gashi meye haka kamar qadangare?"gaba daya basirarta ta tafi,dama atsorace take haka kawai,sai ta kwasa tayi wajenshi babu shiri,batasan cewa wayo yayi mata ba sai data ji ta shigo hannu,saqonni yake aika mata masu wuyar bijirewa,masu nauyi a qwaqwalwa,masu rikita lissafi,sai daya warware mata dukkan wani lissafinta sannan ya rada mata
"Zanso darenmu na farko ya zama cikin wannan garin mai albarka kamar yadda na jima ina burin haka a rayuwata a duk sanda Allah ya bani matar aure,saboda kwadayin albarkar dake cikin garin,kin bani damar cika wannan buri nawa uwaisha?" Kai ta gyada mishi tana rufe idanunta,tana son ta yaqi tsoto da fargabar dake taso mata
"Na gode,na gode" ya dinga maimaita mata yana cusa kanshi tsakanin wuyanta da sumar kanta ta sauko tayi musu rumfa duka su biyun.
Cikin wannan sassanyan daren,khalipha da ayshan suka zama abu guda,khaliphan ya samu ayshan fiye da yadda yake tsammani duk da cewa shi din farin shiga ne,ya bita a sannu yanda ya kamata saidai hakan bai hanata jin jiki ba,tunda ita dinma baquwa ce a fannin,saidai yanayin yadda ya riritata ya taqaita mata wahala qwarai da batasan yadda zata kaya mata ba.
"Wato an samu ummi an manta dani ko?,ba saqon saoda safe,ba saqon barka da safiya,babu na barka da rana,shikenan na gode...kice kawai ba zaki iya kula dani ba tunda kin samu ummi na auro wata kawai" har cikin ranshi da wasa yake,amma abun mamaki saiga qwalla aisha ta fara,abunma kamar yayi dariya amma ganin da gaske kuka zata mishi saiya daure,bai taba zaton yadda ake cewa masu suna aysha nada kishi sosai gaske ne ba kamar yanzu,da qyar yasha kanta,saiya koma seriouse dinshi sosai
"Ki shirya anjima zanzo ki rakani inyi wata siyayya" kai ta langabar
"Ya khalipha....ban gaji ba da ganinta"
"Rakiya nace zakimin ai ko?" Kai ta gyada
"Shikenan" kadan suka taba hira ya wuce shima masallaci,saboda addu'a yakeso yayi yau sosai kan rayuwarsu shida ayshan,harkokin kasuwancinsa,iyaye da 'yan uwanshi.
Gab da magariba ya dawo,yayi kyau sosai cikin shigar larabawa jallabiyya baqa harda hirami,ita kuma ta sanya abaya maroon da baqin niqaf bayan ta nade kanta da mayafin abayar kai kace hijabi ta saka,kallonta yake saboda wani kyau data yi masa,idanuwanta da suka fito ta tsakiyar niqaf din kamar an qara musu girma da kyau,tun a lokacin jikinsa gaba daya ya amsa har cikin zuciya tuhi da gangar jiki,duk wani kuzarin daya taho dashi ya bace,a haka suka lallaba masallaci sukayi magarina da isha'i sannan yace ta fito su tafi.
Katafaren shagon saida kayan ado ne na mata,binsa tayi kawai da kallo sanda ya nufi bangaren kayan bacci bayan ya gama siyan turaruka masu dan karen kyau da tsada,tana kallonshi don yace ba ruwanta ya dinga zaben kayan bacci kala kala,sai daya dauki wajen kala goma dukkansu babu mai qaramin kudi sannan ya biya suka wuce.
Wani shagon suka sake tsayawa nan gaba da wajen kadan,gwalagwalai suke siyarwa,kana ganin yadda suke gaisawa da bashi qima kasan babban custumer ne,hakanan akwai alamun sabo sosai tsakaninsu,kujera yaja mata yace ta zauna,sample aka kawo mata kala kala na sarqa da dan kunne,zobe da banguls khaliphan yace ta tayashi zabe,ta tambayeshi guda nawa yace kowanne bibbiyu,tana zaton anni ko wani zai saiwa saboda haka ta zage ta zabi masu kyau,ita kanta sun bala'in burgeta,basu dade sosai ba ya biyasu sukayi sallama suka fita.
Daganan wajen saida kayan maqulashe ya tsaya shima,yayi siyayya sannan suka shiga motar suka wuce,ta dan gaji hakanan ga kewar ummi,Allah Allah take su isa ya ajeta ta ganta sannan ta huta,sai taga dirven ya dauki wata hanya daban,ba ha yar hotel din da suka sauka ba,hakanan ba hanyar hotel din su ummi ba,dubanshi tayi
"Ina zuwa kuma ya khalipha"
"Masauki zamu koma nayi kewarki uwaisha....kiyi haquri gobe saina maidaki wajen ummi,ni kadaine bana jin dadi" batason bata masa dai dai da rana daya,duk yadda taso ganin ummi saita kada masa kai kawai,sai a sannan ta tuna ma yace mata dama kwana daya zatayi,amma batasan ba zata dawo ba data sake magana da ummin.
Area ce mai wani irin kyau mai kwantar da zukata,hakanan hotel din shima kansa tun daga gininshi da tsarinsa kasan na musamman ne,bata sake tabbatarwa ba sai da suka shiga dakin,duk kayansu yana ciki a shirye,shi ya maida qofar ya sanya muqulli ya rufe,haka kawai a ji jikina yayi sanyi,ta daga kai ta dubi khalipha dake kallonta yana murmushi
"Dakin yayi miki?,ko mu sauya waje?" Murmushu tayi mai sanyi sannan tace
"Sosai ya khalipa"
"Wayyo Allah" ya fada yana aje kayan siyayyar hannunshi,don bai barta ta dauki komai ba kamar yadda bai bar wani ya dauka musu ba
"Wanka da alwala....wazai fara ni koke?" Idanu tadan fiddo
"Ya khalipha...nikam haka zan kwanta bana jin yin wanka"
"No...dole kiyi,so kike ki zama qazama?" Ya fada yana kada kanshi,haka kawai take jin fargaba,saboda kallon da khaliphan yake mata saitake ganin kamar ba wanda ya saba yi mata ba,saita noqe kafada
"Toka fara yi sannan ni" hannunshi ya ware
"Well,hakan yayi" jallabiyar jikinsa ya soma zamewa,saita dan rintse ido kamar yadda ta saba,yana kallonta saidai wannan karon dariya ta bashi,ya qunshe abarsa yana kada kai ya shige toilet din.
Kaman yadda ya saba aqalla yana daukan minti talatin sannan ya fito,tayi wuf ta shige bandakin ganinsa daure da dan guntun towel yau sabanin da da yakan sanya rigar towel,sanda take qoqarin rufe qofar ya sanya hannu ya tokare qofar ya rufa mata baya
"Ya khalipha....don Allah" saita gaza qarasawa ganin ya cimmata ya kaita bango,ya mata rumfa gaba daya,tsoronshi da kwarjinsa wanda bata taba jiba yau ya kamata,so yake lallai ta kalleshi amma taqiya,nunfashinsu ya dinga cakuduwa da juna,murya can qasa yace daita
"Wannan saurin da kike kika fada toilet duk na meye,to sai kin nunamin abinda kike tsoro" kamar zata sanya masa kuka take masa magiya
"Babu komai don Allah kayi haquri,nidai babu komai" wani murmushi ya saki wanda shi kadai yasan ma'anarshi ya janye baya yana cije lips dinshi,saiya nufi famfo ya sake daura alwala sannan ya juy ya dubeta,har yanzu tana tsaye inda ya ritsata
"Kiy sauri ki fito na baki minti goma,idan ba haka ba,zan shigo na daukoki ko baki gama ba"murmushi tayi a kunyace,juyawa yayi ya fice sannan yaja mata qofar toilet din.
Sanda ta fito tuni yana saman abun sallah,sanye da jallabiyya fara qar har daukan ido take,kansa saye da hula tashi ka fiya naci baqa,dakin ya bule da wani irin sassanyan qamshi,wani kyau taga yayi mata sosai,don karta shagala da kallonsa saita kauda kanta,riga ta gani aje ta bacci da kuma after mai kauri gefanta,girgiza kai tayi sanda taga yadda rigar take,amma data tuna zata dora after din saita dauka ta koma bandaki ta shirya acan,ta mulke jikinta da wani turare daya aje mata wanda qamshinsa da dadinsa ya dinga sanyata kasala.
Binta yayi da kallo sanda ta fito daga bandakin,sai yayi mata nuni da gefansa,matsawa tayi ta saita sahu yadda ya dace ya kabbara sallah cikin mamakin sallar meye itama ta tayar,raka'a biyu sukayi sukayi sallama,yaja doguwar addu'a sosai wanda ke tattare da roqon dukkan alkhairi sannan ya shafa,jiyowa yayi ya zauna yana fuskantarta gami da tanqwashe qafa,janye idanunta tayi daga nashi tana jin zuciyarta na bugawa,wata fargaba na shigarta,sunanta ya kira wanda ya sanya ta daga kai ta dubeshi,a nutse yake mata tambayoyi game da abinda ya shafi addininta,sallah tsarki da wanka,kada kai kawai yake yana gamsuwa da bayaninta,kai karantse wata malama ce,sai data kammala sannan ya dora hannunshi ya karanta addu'ar nan da annabi ya umarcemu ga duk wanda Allah ya horewa yayi wani sabon abu,ko mata ko abun hawa,har ya gama tana saurarenshi,hannunsa ya sanya ya janyo ledar dake gafansa wadda suka siyo kayan ciye ciye a ciki,ya fidda komai ya aje a gabansu,itadai nata ido jiki a salube,donta shinshino wani abu,da kanshi ya dinga ciyar da ita,duk da taso ta turje da farko yayi kicin kicin ya nuna yayi fushi,cikin hikima ya dinga janta da hira wanda ya sanyata ta sake,sai gata tana qyalqyala dariya,bayan sun gama ita ta gyara wajen kafin ta kammala ya haye gado abinshi
"Malama a cire hijabin nan da after din mana haka?,banfa ga kwalliyar ba" sai ta dan diririce kadan saboda tuna yanayin rigar dake qasa,girarshi ya dage mata
"Yes....ko so kike nayi asarar kudina?" Ya fada yana zuba mata idanu,hakanan ta dinga fidda kayan kunya na saukar mata,sai daya ragw saura rigar baccin kawai,zuwa sannan numfashinsa ya soma masa nauyi,tunda Allah ya halicceshi bai taba ganin sura irin haka baka,ashe ayshan ta zarta dukkan yadda yake tunani,hannunshi ya miqa mata yana daga zaune saman gadon,bayanshi jingine da fuskar gadon qafafunshi miqe
"Kai zo nan muga wani abu....ya maqale miki a gashi meye haka kamar qadangare?"gaba daya basirarta ta tafi,dama atsorace take haka kawai,sai ta kwasa tayi wajenshi babu shiri,batasan cewa wayo yayi mata ba sai data ji ta shigo hannu,saqonni yake aika mata masu wuyar bijirewa,masu nauyi a qwaqwalwa,masu rikita lissafi,sai daya warware mata dukkan wani lissafinta sannan ya rada mata
"Zanso darenmu na farko ya zama cikin wannan garin mai albarka kamar yadda na jima ina burin haka a rayuwata a duk sanda Allah ya bani matar aure,saboda kwadayin albarkar dake cikin garin,kin bani damar cika wannan buri nawa uwaisha?" Kai ta gyada mishi tana rufe idanunta,tana son ta yaqi tsoto da fargabar dake taso mata
"Na gode,na gode" ya dinga maimaita mata yana cusa kanshi tsakanin wuyanta da sumar kanta ta sauko tayi musu rumfa duka su biyun.
Cikin wannan sassanyan daren,khalipha da ayshan suka zama abu guda,khaliphan ya samu ayshan fiye da yadda yake tsammani duk da cewa shi din farin shiga ne,ya bita a sannu yanda ya kamata saidai hakan bai hanata jin jiki ba,tunda ita dinma baquwa ce a fannin,saidai yanayin yadda ya riritata ya taqaita mata wahala qwarai da batasan yadda zata kaya mata ba.