← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 114

Sashe 29

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

A daren washegari daddy ya kira mummy sa'adah ya sanar mata zuwan masu neman auren ayshan,a zahiri ta nuna zumudi da farinciki,amma a badini baki kawai ta tabe,madadin ta gaya mata tayi musu tanadin abin tabawa kamar yadda aka yiwa maneman auren asma'u sai taja bakinta ta tsuke,taqi ma shaida mata bare tayi qoqarin yin wani abu,sai asma'u data gayawa,dariya asma'un ta dinga yi tana cewa
"To dama mommy me za'a bawa wadan nan?,...nasan yadda dansu yake suma haka suke..qilan ma gwara shi sau dubu a kansu....,mummy ki shirya kina da gagarumin biki....don wallahi tun yanzu ma kisan ya zakiyi da daddy Allah karma ya wani ce zai hada mana biki,don bakin rijiya ba wajen wasan makaho bane ehe" fuskarta qunshe da murmushi saidai tana harararta,don itama harga Allah tafiso a barta a bikin auta su raqashe,ba zata yarda ya hade musu biki da ayshan ba ya jawo musu zubewar mutunci
"Saiki gayawa daddyn naku ai" buga qafa tayi tana duban mummyn
"Allah mummy yace zai hada mana biki fasa auren zanyi,sawa sweet hamid zanyi yacewa daddyn ya qara wata daya ko biyu ai dole ya haqura"
"Kwantar da hankalinki,babu mai hada mana biki ma" tsalle tayi ta ruqunqume mummyn
"Sai mummy na...." Dariya suka sanya baki dayansu.

***** ***** ***** **** **

Sha daya na safe tana kitchen tana hada breakfast din asma'u wadda takeson fita da safen,sam bata masan da cewar yau za'a zo wani neman aurenta ba,ta riga ta bayar da cewa khaliphan yayi tafiyarsa ne abinsa,saboda tayi imanin babu yadda za'ayi mutum yaga mace kamar asma'u,wayayya mai kyau nasaba da dukiya sannan ya zabeta,ita hakanma yafi mata,zuciyarta tafi nutsuwa sosai,don batasan ya lamarin zai kasance ba idan har ya karbi auren nata ba,ta yaya zasu zauna bayan babu wata kalma data jibanci soyayya wadda ta taba shiga tsakaninsu,basu taba za su yi magana mai taken ta fahimtar juna ce a tsakaninsu ba,basu suka zabi juna ba,ba wanda yasan kowa sani tun daga na halayyar zuwa na ra'ayi,wannan gambizar dame tayi kama?,tafiyarsa tana jin maslaha ce kawai a rayuwarsu su duka,gabaki daya a duniyarta a yanzu ta zurfafa karatunta shine kawai burinta,ko sau daya bata taba darsawa kanta tunanin yin aure,wannan ta baiwa kanta cewa sai cikakkun mata masu abinda zasuyu tutiya da shi,itakam me take da shi?,me ta mallaka,taji ma da tarin tulin matsalolin dake neman shaqe rayuwarta su kaita kushewarta wanda har yau bata samu magani ba.

Motsin data ji shi ya sanyata juyowa,mummy ce ta shigo,ta rusuna cikin girmamawa ta gaidata,ta amsa kana ta juya ta fice ba tare data dauki komai ba,daddy ke maganar baqi sun iso a kawo musu abin tabawa,ta shigo ta kuna rasa me zatayi,ayshan zata roqa ta rufa mata asiri ko ko yaya?,itakam bata san ma me ake ba,daga bisani dai taga daya daga cikin masu aikin gidan ta shigo ta shirya lemuka da ruwa kan faranti ta fita da su,itama tana gama hada break din ta diba zuwa dining ta soma shiryawa a can.

Tana tsaka da gyara wajen taji muryar daddy yana shigowa falon,da alama waya yake,takun takalman asma'u suka karade falon,kai tsaye ta nufi dining din ta ja kujera ta zauna tana duban ayshan fuskarta qunshe da fara'ar da batasan ya meye ba,kallo daya ayshan ta yiwa fuskarta ta dauke kai,hakanan taji fara'ar bata gamsheta ba
"Me kika dafa?" Ta fada tana latsa wayarta,bata ce komao ba ta bubbude kwanukan,sai data daga kai ta dubesu sannan tace
"Zuba maza da sauri fita zanyi" faranti ta jawo ta soma zuba mata dai dai sanda daddy ya gama wayar suka soma magana da mummy
"Mun gama sun tafi"
"Nawa suka kawo?"
"Dubu talatin ne" daddy ya fada yana ciro kudin da suka kawo din daga aljihunsa,wani sanyi ya ratsa mummy a badini tana jin cewa lallai Allah ya yiwa diyarta gyadar dogo,yayin da a zahiri kuwa ta cunkushe fuska tana cewa
"Haba daddy...yanzu kai ya za'ayi ka bada auren yarinya akan dubu talatin kaman wata atamfa....haba sai kasa a zagemu ace muna sane"
"Babu komai sa'adatu...albarka auren ake nema ba tarin dukiya ko qyale qyale ba,yaron kuma yana da dukkan nagartar da za'a iya bashi auren kowacce diya wannan kawai ya isa"
"Amma aysha indo a dubu talatin daddy" saida mummy tayi furucin qarshe sannan ta ankara,mummunar faduwar gabanta tazo dai da sanda asma'u ta bushe da dariya har tana neman qwarewa da farfesun da take diba da cokali tana sha
"Wai.....dubu talatin....kudin takalmi na" asma'un ta fada tana dariya qasa qasa don kada daddyn ya jiyota,sosai jikin aysha ke rawa da jin abinda bata tsammata ba haka nan bata shirya masa ba,aure?...aure a irin wannan lokacin?.....wanne irin mutum ne shi da ya amince zai aureta a haka?.

Abincin da bata gama zubawa ba kenan ta saki sarving spoon din ta wuce dakinta.

Kuka ta zauna sosai tayi a bakin gado,tsoro da firgici yana kamata,tunanin makomarta take,ya kuma rayuwarta zata sake juya mata,auren da babu soyayya a karo na biyu,auren da babu sanayya sabo ko fahimtar juna,ya sunan zamansu?,ya zata kasance shine kawai abinda ta dinga juyawa cikin ranta,wayarta ta jawo,a yau tana jin buqatar abokin shawara fiye da kullum,yau tana fatan idan ta kira aliya ta sameta a waya,ba kamar ragowar kwanakin ba da bata samunta,saidai yau dinma data kira haka aka sake gaya mata layin a kashe yake,jikinta a sanyaye ta aje wayar ta qura mata ido,bakinta cike fal da addu'ar neman yayewar qunci da haskawar lamuranta baki daya.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶

Tun safiyar ranar bata sake takowa falo ba bare ta leqo wajen gidan,tana nade kan gado,sallah kawai ke sauko da ita data gama zata koma ta sake kwanciya.

Qarar bude qofar dakinta ya sanya ta daga kanta tana duban bakin qofar,inna laraba ce,da sauri ta miqe ta zauna saman gadon fuskarta qunshe da murmushi tare da nuna zumudi take saukowa daga kan gadon
"Inna....yaushe kika dawo?"
"Ban wuce minti talatin ba cikin gidan nan...komawa kuma zan sakeyi ma" ta fada tana murmushi,tunda babbar 'yar mummy cuta aka kai inna laraba take can gidan,ba qaramin kewarta aysha keyi ba,don kusan da ita kadai take zama ta taba hira cikin gidan,saboda yadda inna ke janta a jiki tare da nuna mata qauna,haka nan jininsu ya hadu sosai da innar,gaisheta ta fara yi innar ta amsa tana cewa
"Baqo gareki fa 'yata....inajin surukin namu ne yazo....yau bakina har kunne nazo na tadda abun alkhairi...ubangiji yasa abokin arziqin ki ne"kanta a sunkuye jikinta a matuqar sanyaye ta amsa
" ki maza ki fita...idan ban koma ba kafin ki gama ma gaisa sosai"
"Toh inna" kawai ta fada innar ta fice ta barta tsaye gaban kayan sawarta tana neman hijabi,bawai don bata ga hijabin bane,hakanan jikinta yayi wata iriyar mutuwar ga fargabar data cika mata zuciya.

Har zata fice a falon sai ta koma kitchen ta qofar baya,ta hado masa lemo da ruwa ta dora cup ta wuce da shi.

Daga nesa ta hangoshi,ya baiwa qofar shigowa baya,qafarsa daya na saman kujera daya tana qasa,bata iya hango abinda yake amma dan duqe yake gwaiwar hannunsa kan gwiwar qafarshi,takowa take idanunta a kanshi,gabanta na faduwa duk sanda nisan dake tsakaninsu ya ragu
"Assalamu alaikum" tayi sallama tana tsaye daga bayanshi kanta na kallon qasa,a nutse ya sauke qafafunshi sannan ya waiwayo inda take tsaye,dubanta yayi sau daya sannan ya amsa sallamar yana nemawa kanshi wajen zama,bata motsa ba har sai data tabbatar ya zauna sannan ta dora farantin,tq bude robobin duka ta zuba masa ruwa da lemon sannan taja kujerarta can baya ta zauna
"Ina yini" ta furta a hankali cikin sanyayyar muryarta da sai ka zaci da gayya take yinta,idanunsa ya dauke daga kan kofunan ya maidasu saman fuskarta da take kallon qasan wajen ya amsa mata da lafiya lau,daga haka shuru ne ya biyo baya,ya zuba mata idanunsa yana karantarta,yayin da tausayinta ya dinga ratsa zuciyarshi,sai ya dinga kwatanta ace qaramar qanwarsa ce haka a gabansa ta fuskanci rayuwar data bashi labari koma take kan fuskanta,hajar ya tuna,harbkwanan gobe bai mantawa da ita,bai manta yadda ta tafi ta barsu,tabon yana nan a zukatansu bai goge ba.

Duk da bata kalleshi ba hakanan take jin idanunsa a kanta,tunda take bata taba ganin namijin da yake mata kwarjini irinsa ba.

Batasan yaushe ya taso ba,sai tsintsarsa tayi zaune saman teburin,hannayensa sarqafe da juna,tazarar dake tsakaninsu bata da yawa,hakan ya sanya zuciyarta soma bugawa da sauri da sauri,don kaf rayuwarta ba zata iya tuna sanda ta zauna haka da namiji tsakaninta da shi da qaramar tazara ba.
Chapter 29 · 0% Book details