Sashe 66
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta fannin abokan kwananta kuwa sai sam.barka,dukkansu mutanen kirki ne kamar yadda take addu'a Allah ya hadata dana gari,hanan matashiya ce wadda zasuyi shekaru daya,haifaffiyar kano saidai iyayenta na zaune akano saboda yanayin aikin gwamnati da babu inda baya kai mutum,'yar gata ce sosai kasancewarta ita daya ce mace cikin yaran da mamanta ta haifa,tana da ilimi nutsuwa da kamun kai,tana da surutu,sauqin kai da saurin sabo da jama'a,batason muce mara kamun kai mara tambayi ko kintsi,yanayin rayuwa da take cikin mutane da suke a waye,uwa uba gata bata rasa komai ba saita zama 'yar ado 'yar kwalliya,hanan badai wayewa da gogewa ba,baya ga tsafta taba da son kwalliya da qyale qyale na mata,duk wanda ya santa a haka ya santa,hanan nada saurayinta Abubakar saddiq wanda aka riga akayi musu baiko da shi aka saka musu rana,shekara guda,wato shekara mai zuwa kenan,suna matuqar son juna irin soyayyar nan mai tsafta.
Sai ruqayya ummu hunaifa,matar aure ce wadda aqalla ta basu shekara hudu ko uku,saidai tana da sauqin kai faran faran da son jama'a,macace wadda itama 'yar gayu ce mai zaman kanta,wanda gayunta ya nuna har a jikinta,shekararta uku da aure yanzu haka tana da yarinya 'yar shekara daya,suna zaune a farawa saidai mijinta na aiki a abujane shima,duk weekend yana dawowa gida yayi da iyalinsa,mijinta nada hali don a revenue yake aiki,ruqayya nada ilimin xama da dan adan da experience na rayuwa mai yawa,sakamakon dan yawace yawace na qasashe da sukayi ada da mijints ibrahim,da kuma tashi da tayi a hannun kakarta,tun zuwan aysha taji jininsu ya hadu,kamar yadda Allah ya hada jininsu da hanan,wannan kenan.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Dakin babu kowa sai ita kadai,ita kadai dince ta dawo saboda hanan da mmn hunaifa duka suna aji,sakamakon banbancin course da suke dashi,kowacce akwai abinda take karanta,rana ake qwalawa sosai,shi yasa tana shigowa ta sauya kaya zuwa doguwar riga mai yankakken hannu,ta nade tulin gashinta daya soma damunta da dankwalin rigar,sannan ta shiga bandaki ta daura alwala ko zata ji sanyi,duk da tana fashin salla,saman gadonta ta dawo tayi rubda ciki,dai dai nan kiran aliya ya shigo mata,ba bata lokaci ta daga don dama kwana biyu basuyi wata doguwar hira ba karatu ya soma sa kowa gaba.
Sun kuwa jima suna hirarsu daga bisani sukayi sallama ta yanke ta kira anni suka gaisa,daga anni ta nemi mero sai gwaggo asabe,wanda daga bisani ta tuqe kan lambar umminta,ta jima tana kallon lambar kamar ta kira haka zuciyarta ke raya mata,tayi kewarta qwarai,tana son jin muryarta koda fada zata yi mata,tana son jin motsinta ko yaya ne,qwalla ce ta cika mata idanu,saidai tayi iya yibta ta maidata jin an turo qofar dakin.
Hanan ce,kallo daya zaka yi mata ka tabbatar a jikace take,haka ne kuwa don litatafan ta watsar a qasa
"Wayyo eesha yunwa" dariya aysha tayi tana saukowa daga saman gadonta
"Aikuwa kin daki gurbi,don yau ban dora komai ba na zaci tun yau zaku tafi gida weekend" ciki ta kama tana yamutsa fuska
"Ki taimako don Allah" dariya tayi ta soma yunqurin kunna gas
"Saikin dan qara haquri" saman katifar ta ta koma ta kwanta tana yar mitar data baiwa aysha dariya,tana tsaka da jajjage maman hunaifa ta shigo dakin,ita daya ce don tun wancan satin tabat hunaifa a gidansu bata dawo da ita ba,ba irin mitar dasu aysha basuyi ba
"Ke kike biye mata aysha,barta don Allah yau tasha yunwarta,saison abincin amma bazata iya tsayawa ta dafa ba" ta fada tana hararar hanan
"Haba surukata(haka take tsokanarta tunda qanin maman hunaifan ya ganta yace yana so),idana gaban nazir ishaaq dinne ma haka zaki fada?"
"Eh mana tunda ke son jiki gareki"
"Karki damu zan koya fa ai aysha zata koya min" ta fada tana miqewa zaune
"Ko ba zaki koyamin ba naga kina bata rai?" Sosai ta baiwa aysha dariya,zama da hanan akwai dadi amma idan baka iya ba saikuyita fada,bata ma kalleta ba bare ta gane hakan da har zatayi mata sharhi
"Zanfi kowa murnar ki koya din,saboda sanwa adon macace"
"Gaya mata dai" cewar mmn hunaifa,haka suka dinga zolayar juna suna hirarrakinsu,har aysha ta gama musu jallop din couse couse data ji kifi suka hadu suka ci.
Qarfe hudu hanan ta fito a wanka,tana saka doguwar rigarta ta dubi aysha
"Ko zaki rakani,naga tunda kika zo baki taba zagayawa ko yaushe daga daki sai aji"
"Ina zaki je" mmn hunaifa ta tambayeta
"Kinsan jibi weekend,ga lallen hannu na ya fita,kaina tun last month rabonsa da retourching zan leqa ayimin"
"Nima fa lallen nakeso wlh,abban hunaifa zai biyo jibi mu wuce gida"
"Za'aci amarci kenan?" Hanan ta fada tana kashe ido cikin son tsokano ruqayya,dariya ta bata ta riga ta saba da halinta
"Allah ya shiryeki hanan,ko kunyata bakiji" ta fada tana shiryawa itama
"Ki shirya muje ko?" Ta sake cewa aysha wadda ke kwance tana duba handout,sauketa tayi daga fuskarta tadan yatsina fuska
"Kuje kawai,nikam ban sha'awa,kaina ma kuma a wanke yake" baya hanan taja tana dubanta
"Nimam aysha mamaki kike bani,kekam kaman ba budurwa ba?,duk wani qyale qyale na mata babu ke a ciki,ko dan saurayi haka ban taba ganinki da shi ba?,to tashi yaukam ko kallo saikinje kinyi" ba yadda ta iya da jarabar hanan,hakanan ta miqe ta daura alwala ta sake shafa mai powder da man lebe ta zizara kwalli,har ta dauki hijabinta zata dora saman rigar jikinta tace bata isa ba,bazata jawo a rainasu ba waje zasu je na masu aji,hakanan ta maida ta ciro doguwar riga tayi rolling da mayafinta,plate shoes ta saka da jakarshi,sai wani agogo dan siriri da yazo a cikin jakar
"Ma sha Allah" mmn hunaifa tace
"Da ina da wani qanin bayan ishaaq da nayi masa kamu wallahi" hakanan taji gabanta ya fadi,saita tuna khalipha,tunda ya tafi basu yi waya ba gashi sunci qarfin semester farko,dariya tayi kawai ta basar da zancan suka fito daga dakin,duk cikinsu babu wanda yasan komai game da rayuwarta,ba wanda yasan tana da aure,har yau kuma batayi maganar da kowa ba cikinsu,kallon budurwa duk suke mata,anni ce babarta,haidar qaninta.
Tunda suka fito duk wanda suka gamu da su saisun kalleta,ta rasa kallon na meye,har hakan ya soma damunta yasa ta fara tsarguwa ko tayi wani abu ba dai dai ba,don yawanci idan zata fita lacture shigar hijabi takeyi wani lokaci harda niqab,jefi jefi hanan ko mmn hunaifa kan tsaya su gaisa da wasu wasu kuma su wuce,mamaki take ya akayi sukasan jama'a haka?,sai da suka fito gate din makaranta suka samu abun hawa suka wuce.
Babban waje ne wanda idan aka ce mata akwaishi a wudil zata qaryata hakan,gurin suna gyaran gashi da jan lalle da baqi,hakanan akwai turarukan jiki dana kaya masu kyau da zabar qamshi,kana shiga wajen ma zakasan eh lallai akwai turare a wajen,hanan aka soma yiwa gyaran kai aka sa mata lalle sai mmn hunaifa,daga bisani hanan din da taimakon mmn hunaifan suka tubure sai an saka mata,hakan ba yadda ta iya ta ware kanta aka soma gyara mata
"La haula fi shi'atillah,ba banza ba bakison gyaran kai,muda bamu da mai yawa muke damuwa dama da shi" inji hanan gana zaro ido,itakam murmushi kawai tayi,sai take jinta a takure kaman tana waje,bayan an gama itama aka saka mata lallen,amma.ja tace tana so,iya yatsun hannu da qafa,data cire kuwa saiga yatsun nata shar da su,lallen yayi marroon a farar fatarta,itakanta sai daya bata sha'awa,don ta manta when last da tayi qunshi irin haka.
Sai magariba suka gama,hanan ta siya turarukan kayan dana jiki leda biyu,da gawayi irin mai saurin kamawar nan ta biya suka wuce,suna zuwa daki ta miqawa aysha daya
"Nima a gun mmn hunaifa na soma gani,yana da kyau idan ya kama jikinki" godiya tayi mata bayan ta amsa din,don tana jin qamshinsa a kayanta yana da dadi sosai,a ranar ita kanta taji dadin yadda kanta yayi kyau,hakan bayan ta gama sallar tayita kallon yatsunta har hanan ta lura ta dinga yi mata tsiya.
Tun daga sannan zuwan itama ya zame mata jiki,ko basu je ba data fita ita zata je a sake mata,cikin lokaci kadan saiga ayshan ta soma koyar wasu abubuwa irin na matan da suke da aji daga wajen hanan da mmn hunaifa,yanayin zamantakewarsu da samari da kuma mijinta,idan suna wani abun kallonsu kawai take,ruqayya badai iya tarairayar miji da shagwabashi ba,hakanan hanan da nata saurayin,wani lokaci ita kunya ma take ji sukuwa ko a jikinsu,har gori suke mata kan tayi zuciya tayi saurayi
"Na aurar dake keda hanan na huta lokaci daya" cewar anty ruqayya,sai abun ya soma burgeta,ta dinga jin inama itace su,ta dinga ji inama zata samu wanda zai nuna mata zallar kulawa kamar ibrahim din mmn hunaifa shida mmn hunaifar,ko hanan ita da saddiq dinta,da alama soyayya zaqi gareta,tana son dandana nau'in wannan soyayyar baya gata sauran mutane gama gari data sameta a yanzu,takan jima tana wannan tunanina ranta.
Cikin taimakon Allah suka gama semester daya har suka soma nisa cikin ta biyun,a sannan ayshan ta samu qarin wayewa da budewar ido,komanta ya soma sauyawa saboda gogayya da mu'amala da mutane iri daban daban,shuru shurunta ya ragu duk da cewar har yanzu akwai wannan kunyar da kamun kan,saidai yanayin ado da kwalliya,qyale qyale,iya magana da sauransu duka akwai sauyi tattare da hakan.
A wani zuwa da tayi weekend anni ta mata maganar zuwa gida,itakanta tana son hakan,don tunda tabar gidan a qalla yanzu watanni kusan bakwai zuwanta daya gidan,babu musu ta shirya,kwalliya tayi sosai abinta,dama gashi ta soma zama expert a wannan bangaren,kwalliya mai sanyi da aji da nuna asalin gayu,ba hauka ba hayaniya,haidar shi zai kaita kaman yadda suka saba yawanci idan zata fita ko zata koma makaranta shi yake kaita.
Sai ruqayya ummu hunaifa,matar aure ce wadda aqalla ta basu shekara hudu ko uku,saidai tana da sauqin kai faran faran da son jama'a,macace wadda itama 'yar gayu ce mai zaman kanta,wanda gayunta ya nuna har a jikinta,shekararta uku da aure yanzu haka tana da yarinya 'yar shekara daya,suna zaune a farawa saidai mijinta na aiki a abujane shima,duk weekend yana dawowa gida yayi da iyalinsa,mijinta nada hali don a revenue yake aiki,ruqayya nada ilimin xama da dan adan da experience na rayuwa mai yawa,sakamakon dan yawace yawace na qasashe da sukayi ada da mijints ibrahim,da kuma tashi da tayi a hannun kakarta,tun zuwan aysha taji jininsu ya hadu,kamar yadda Allah ya hada jininsu da hanan,wannan kenan.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Dakin babu kowa sai ita kadai,ita kadai dince ta dawo saboda hanan da mmn hunaifa duka suna aji,sakamakon banbancin course da suke dashi,kowacce akwai abinda take karanta,rana ake qwalawa sosai,shi yasa tana shigowa ta sauya kaya zuwa doguwar riga mai yankakken hannu,ta nade tulin gashinta daya soma damunta da dankwalin rigar,sannan ta shiga bandaki ta daura alwala ko zata ji sanyi,duk da tana fashin salla,saman gadonta ta dawo tayi rubda ciki,dai dai nan kiran aliya ya shigo mata,ba bata lokaci ta daga don dama kwana biyu basuyi wata doguwar hira ba karatu ya soma sa kowa gaba.
Sun kuwa jima suna hirarsu daga bisani sukayi sallama ta yanke ta kira anni suka gaisa,daga anni ta nemi mero sai gwaggo asabe,wanda daga bisani ta tuqe kan lambar umminta,ta jima tana kallon lambar kamar ta kira haka zuciyarta ke raya mata,tayi kewarta qwarai,tana son jin muryarta koda fada zata yi mata,tana son jin motsinta ko yaya ne,qwalla ce ta cika mata idanu,saidai tayi iya yibta ta maidata jin an turo qofar dakin.
Hanan ce,kallo daya zaka yi mata ka tabbatar a jikace take,haka ne kuwa don litatafan ta watsar a qasa
"Wayyo eesha yunwa" dariya aysha tayi tana saukowa daga saman gadonta
"Aikuwa kin daki gurbi,don yau ban dora komai ba na zaci tun yau zaku tafi gida weekend" ciki ta kama tana yamutsa fuska
"Ki taimako don Allah" dariya tayi ta soma yunqurin kunna gas
"Saikin dan qara haquri" saman katifar ta ta koma ta kwanta tana yar mitar data baiwa aysha dariya,tana tsaka da jajjage maman hunaifa ta shigo dakin,ita daya ce don tun wancan satin tabat hunaifa a gidansu bata dawo da ita ba,ba irin mitar dasu aysha basuyi ba
"Ke kike biye mata aysha,barta don Allah yau tasha yunwarta,saison abincin amma bazata iya tsayawa ta dafa ba" ta fada tana hararar hanan
"Haba surukata(haka take tsokanarta tunda qanin maman hunaifan ya ganta yace yana so),idana gaban nazir ishaaq dinne ma haka zaki fada?"
"Eh mana tunda ke son jiki gareki"
"Karki damu zan koya fa ai aysha zata koya min" ta fada tana miqewa zaune
"Ko ba zaki koyamin ba naga kina bata rai?" Sosai ta baiwa aysha dariya,zama da hanan akwai dadi amma idan baka iya ba saikuyita fada,bata ma kalleta ba bare ta gane hakan da har zatayi mata sharhi
"Zanfi kowa murnar ki koya din,saboda sanwa adon macace"
"Gaya mata dai" cewar mmn hunaifa,haka suka dinga zolayar juna suna hirarrakinsu,har aysha ta gama musu jallop din couse couse data ji kifi suka hadu suka ci.
Qarfe hudu hanan ta fito a wanka,tana saka doguwar rigarta ta dubi aysha
"Ko zaki rakani,naga tunda kika zo baki taba zagayawa ko yaushe daga daki sai aji"
"Ina zaki je" mmn hunaifa ta tambayeta
"Kinsan jibi weekend,ga lallen hannu na ya fita,kaina tun last month rabonsa da retourching zan leqa ayimin"
"Nima fa lallen nakeso wlh,abban hunaifa zai biyo jibi mu wuce gida"
"Za'aci amarci kenan?" Hanan ta fada tana kashe ido cikin son tsokano ruqayya,dariya ta bata ta riga ta saba da halinta
"Allah ya shiryeki hanan,ko kunyata bakiji" ta fada tana shiryawa itama
"Ki shirya muje ko?" Ta sake cewa aysha wadda ke kwance tana duba handout,sauketa tayi daga fuskarta tadan yatsina fuska
"Kuje kawai,nikam ban sha'awa,kaina ma kuma a wanke yake" baya hanan taja tana dubanta
"Nimam aysha mamaki kike bani,kekam kaman ba budurwa ba?,duk wani qyale qyale na mata babu ke a ciki,ko dan saurayi haka ban taba ganinki da shi ba?,to tashi yaukam ko kallo saikinje kinyi" ba yadda ta iya da jarabar hanan,hakanan ta miqe ta daura alwala ta sake shafa mai powder da man lebe ta zizara kwalli,har ta dauki hijabinta zata dora saman rigar jikinta tace bata isa ba,bazata jawo a rainasu ba waje zasu je na masu aji,hakanan ta maida ta ciro doguwar riga tayi rolling da mayafinta,plate shoes ta saka da jakarshi,sai wani agogo dan siriri da yazo a cikin jakar
"Ma sha Allah" mmn hunaifa tace
"Da ina da wani qanin bayan ishaaq da nayi masa kamu wallahi" hakanan taji gabanta ya fadi,saita tuna khalipha,tunda ya tafi basu yi waya ba gashi sunci qarfin semester farko,dariya tayi kawai ta basar da zancan suka fito daga dakin,duk cikinsu babu wanda yasan komai game da rayuwarta,ba wanda yasan tana da aure,har yau kuma batayi maganar da kowa ba cikinsu,kallon budurwa duk suke mata,anni ce babarta,haidar qaninta.
Tunda suka fito duk wanda suka gamu da su saisun kalleta,ta rasa kallon na meye,har hakan ya soma damunta yasa ta fara tsarguwa ko tayi wani abu ba dai dai ba,don yawanci idan zata fita lacture shigar hijabi takeyi wani lokaci harda niqab,jefi jefi hanan ko mmn hunaifa kan tsaya su gaisa da wasu wasu kuma su wuce,mamaki take ya akayi sukasan jama'a haka?,sai da suka fito gate din makaranta suka samu abun hawa suka wuce.
Babban waje ne wanda idan aka ce mata akwaishi a wudil zata qaryata hakan,gurin suna gyaran gashi da jan lalle da baqi,hakanan akwai turarukan jiki dana kaya masu kyau da zabar qamshi,kana shiga wajen ma zakasan eh lallai akwai turare a wajen,hanan aka soma yiwa gyaran kai aka sa mata lalle sai mmn hunaifa,daga bisani hanan din da taimakon mmn hunaifan suka tubure sai an saka mata,hakan ba yadda ta iya ta ware kanta aka soma gyara mata
"La haula fi shi'atillah,ba banza ba bakison gyaran kai,muda bamu da mai yawa muke damuwa dama da shi" inji hanan gana zaro ido,itakam murmushi kawai tayi,sai take jinta a takure kaman tana waje,bayan an gama itama aka saka mata lallen,amma.ja tace tana so,iya yatsun hannu da qafa,data cire kuwa saiga yatsun nata shar da su,lallen yayi marroon a farar fatarta,itakanta sai daya bata sha'awa,don ta manta when last da tayi qunshi irin haka.
Sai magariba suka gama,hanan ta siya turarukan kayan dana jiki leda biyu,da gawayi irin mai saurin kamawar nan ta biya suka wuce,suna zuwa daki ta miqawa aysha daya
"Nima a gun mmn hunaifa na soma gani,yana da kyau idan ya kama jikinki" godiya tayi mata bayan ta amsa din,don tana jin qamshinsa a kayanta yana da dadi sosai,a ranar ita kanta taji dadin yadda kanta yayi kyau,hakan bayan ta gama sallar tayita kallon yatsunta har hanan ta lura ta dinga yi mata tsiya.
Tun daga sannan zuwan itama ya zame mata jiki,ko basu je ba data fita ita zata je a sake mata,cikin lokaci kadan saiga ayshan ta soma koyar wasu abubuwa irin na matan da suke da aji daga wajen hanan da mmn hunaifa,yanayin zamantakewarsu da samari da kuma mijinta,idan suna wani abun kallonsu kawai take,ruqayya badai iya tarairayar miji da shagwabashi ba,hakanan hanan da nata saurayin,wani lokaci ita kunya ma take ji sukuwa ko a jikinsu,har gori suke mata kan tayi zuciya tayi saurayi
"Na aurar dake keda hanan na huta lokaci daya" cewar anty ruqayya,sai abun ya soma burgeta,ta dinga jin inama itace su,ta dinga ji inama zata samu wanda zai nuna mata zallar kulawa kamar ibrahim din mmn hunaifa shida mmn hunaifar,ko hanan ita da saddiq dinta,da alama soyayya zaqi gareta,tana son dandana nau'in wannan soyayyar baya gata sauran mutane gama gari data sameta a yanzu,takan jima tana wannan tunanina ranta.
Cikin taimakon Allah suka gama semester daya har suka soma nisa cikin ta biyun,a sannan ayshan ta samu qarin wayewa da budewar ido,komanta ya soma sauyawa saboda gogayya da mu'amala da mutane iri daban daban,shuru shurunta ya ragu duk da cewar har yanzu akwai wannan kunyar da kamun kan,saidai yanayin ado da kwalliya,qyale qyale,iya magana da sauransu duka akwai sauyi tattare da hakan.
A wani zuwa da tayi weekend anni ta mata maganar zuwa gida,itakanta tana son hakan,don tunda tabar gidan a qalla yanzu watanni kusan bakwai zuwanta daya gidan,babu musu ta shirya,kwalliya tayi sosai abinta,dama gashi ta soma zama expert a wannan bangaren,kwalliya mai sanyi da aji da nuna asalin gayu,ba hauka ba hayaniya,haidar shi zai kaita kaman yadda suka saba yawanci idan zata fita ko zata koma makaranta shi yake kaita.