Sashe 46
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A haka lantana daya daga cikin masu aikin gidan ta shigo ta tadda ta
"Lallai indo a gaisheki da qoqari,amarya guda da gyaran kitchen?,lallai" ta fada tana kama habarta alamar mamaki,da murmushi a fuskar aysha ta juyo ta kalli lantanar
"Banda abinki lantana wannan kitchen haka komai a hautsine,ta yaya zakuji dadin yin aikin?" Baki ta dan tabe tana aje farantan hannunta
"Wallahi gajiya nahi aisha....tun safe kana tsaye...ka gyara a bata,kowa kuma da kiran da zai maka....dama kuma kece mai juriyar,nikam nayi iya yina na gaji"
"Allah ya rufa asiri"
"Amin....ai gwara kiyi mana ma na bankwana,zamuyi kewarki wallahi indo" inji lantana tana nuna alhininta a fuskarta zuwa zuciya,sun saba da ayshan saboda sauqin kanta,hakanan sau tari takan amshe ayyukansu tayi idan tana da lokaci,ba ruwanta da qyamar mutum ko girman kai,ba kamar asma'u ba da basu taba jin dadinta ba,ayshan bata ce komai ba sai murmushi da tayi,wanda banda lotsawar da kumatunta yayi ma ba zaka gane hakan ba,kama mata lantanar tayi suka soma gyaran tare.
Basufi mintuna goma ba suka soma jiyo tashin hayaniya daga falon gidan,a hankali muryar anty safiyya tafi ta kowa fitowa
"Mu zasu nunawa iskancin banza iskancin wofi...mu zasu nunawa arziqi?,dama tun ranar kamu nake kula da take takensu,kai tun ranar kawo kaya,ina ruwanmu da wani familynsu ko arziqinsu,abinda muka sani kawai shine mun basu auren 'yar uwarmu,hakanan muma ba'a talauce suka ganmu ba bare suyi mana dagawa" ta qarashe fada tana huci
"Ke kinga yadda suke wani daddaga hanci da kallon kowa d'ai d'ai kamar kansu aka fara kudi,kina fa gani da muka shiga yiwa ango da amarya liqi sauka sukayi daga kan stage dinfa...." Anty kubra ta fada cikin jin haushi itama
"Su taka a hankali mi tsaf zan kora musu jawabi wallahi...ai muma ba tsiya suka ga tana binmu ko?....koma tsiyar ce a haka dansu yaga yarmu yace yana son aure" anty hajja wadda take qanwace ga momy ita ke binta ta fada.
"Kowa ya sayi rariya ai yasan zata zubda ruwa....tun daga yanayin halayyar yaron ya kamata su gane kowanne tsuntsu kukan gidansu yakeyi,don dai kai kawai baka isa ka fada bane baka da ikon gin magana" lantana ta fada,itadai aysha bata ce komai ba,tunda ba huruminta bane,har suka kammala ta wanke hannunta ta yiwa lantana sallama ta juya tabar kitchen din.
A kacame ta tadda falon,asma'u na kumfar baki anty safiyya nayi,da alama wani abun ne ya sake faruwa,tana jin anty safiyya na cewa
"Nikam babu matar data isa na sake jera kafada da ita bare ta wulaqantani bayan Allah bai wulaqantani ba,kije ku qarata ke dasu ke kika zabarwa kanki...banda shi mara mutunci ne har yace ki baiwa yan uwansa haquri sannan ya saurareki?" Cikin kuka asma'u tace
"Kinji ko mummy....wallahi ki mata magana,kinga zata jawo min matsala ko....nasan halin hamid wlh tsaf zai tsiri fushi da ni qarshenta ma sai wani satin za'a qarasa wani abun...nidai ki mata magana kawai"
"Ai na haifu,kuma 'yar halak ce ni...kije Allah ya bada sa'a" anty safiyya ta fada tana barin falon,ta haura sama dakin da suka sauka ita da sauran 'yan uwanta.
"Maganar gaskiya asma'u nima fa naji haushi...kuma hamid ya bani mamaki...ban zaci haka yake babu kwalli a idanunsa ba,giyar kudi na dibansa kenan?" Cewar anty kubra wadda sakuwa ce ta asma'un
"Kinga don Allah bana son qananun maganganu,nice dai zan aureshi na zauna da su,kuma naji ina son abina a haka ko yaya yake tunda shima yana sona" ta fadi cikin fada tana tasowa kubrar kamar zata doketa
"Allah ya bada sa'a" itama ta fada tana barin wajen,sai asma'un ta fada jikin mummy tana rushewa da kuka,duk sun hada mata zafi,gaba daya bikin yana neman juye mata,yaqi zuwa mata a dadin rai yadda taso,ga wannan tirka tirka da takeao ta kunno kai tsakanin dangin hamid din da nata,gefe guda kuma maganar aysha har yau na cin ranta,ba kamar yauma da take sake tambayar hamid waye muhammad abdulhakim mai goron,a yadda yake gaya mata waye shi ta tsorata matuqa,tana tsoron faruwar wani anu,tana tsoron kada reshe ya juye da mujiya,batason abinda zai sanya ta kasance itace a qasa har abada,koda yaushe tafison taga itace a sama sama da kowa.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Qarfe goma na safiyar washegari suka kammala shirinsu na wucewa takai,a sannan har aliya itama ta iso,ta ishi aysha da tambaya kan maganar data ce zasuyi,murmushi tayi kawai tace
"Me kike ci na baka na zuba?,zamuyi ai".
Sallamar lantana ita taja hankalinsu
"wani ne a waje yake jira wai an turoshi zai kaiku takai" cikin mamaki aysha ke kallon lanta
"Mu kuma?...takai?" Ta fada tana tunanin waye haka zai aiko?,iya tunaninta bata gane ko waye zai mata wannan karamcin ba,hakan yasa dole ya zira hijabinta tace
"Zo muje aliya inga ko waye" suka fice daga dakin.
Tun daga nesa ta gane baquwar mota ce ba irin ta gidansu ba,saidai bata iya ganin waye a ciki har ta qarasa gaban motar ta tsaya,murfin motar ne ya bude,wani matashin dan kimanin shekaru arba'in ya fito,cikin girmamawa yace
"Ranki ya dade boss ne ya aiko ni....ina fatan kun kammala shiryawa"
"Wanne boss?" Murmushi yayi sannan yace
"Wanne boss ne bayan muhammad khalipha?" Hannunta ta daga
"Ohk....ka koma kawai,zamu bi motar haya" ta fadi tana kama hannun aliyar dake binta da kallon tambaya suka juya.
Tana gab da shiga falon wayarta ta dauki ruri,dubawa tayi K ce ta bayyana kamar yadda tayi serving number dinsa
Numfashi ta aje sannan ta daga wayar ta kara a kunneta
"Me ya faru tsakaninki da sani,yace min wai ance ya tafi"
"Bbu komai,zamu bi motar haya ne kawai...."
"Bai dace ba aysha...maida hannun alkhairi baya fa kenan?"aliyata fada tana tsaye daga gefanta
"Aliya....kin san waye?"ta fada tana kallon hanya ba tare data dubi aliyan ba
"a'ah"ta bata amsa tana girgiza kanta dukka idanunta da hankalinta na kan ayshan
" khalipha ne fa aliya,wanda zan aura"
"Arrrrrrhhhhh" aliya ta fada tana rufe bakinta da tafukan hannayenta duka biyun kamar mai maitsoron kar wani yaji ihunta,idanunta a waje hakanan fuskarta qunshe da murmushi
"How comes sashen....tell me pls" juyowa tayi tana duban aliya,hannayenta harde a qirjinta,fuskarta a hade tsaf
"Khalipha ya saka min shakku mai yawa a kansa aliya....ta yaya zaizo min da wata fuska?,ta yaya zaizo min da wata siga?....a yadda khalipha yazo min aliya ashe ba haka bane....wannan ba yaudara bane?"
"Ya salam.....haba...ni nasan kaman na taba sanin face dinshi a wani waje wlh...kaman ya taba zuwa wajen abba na...oh my god...ina zuwa" aliya ta fada tana zame hannunta daga riqon data yiwa aysha,da sauri sauri kaman wadda zata tashi sama ta koma qofar gida,da idanu aysha take kallonta tana mamakin saurin me take ina zata?,me yasa bata ga alamun jimami ko tayata bacin rai kan abinda khaliphan ya aikata ba?.
Tana nan tsaye kaman sakarya har aliyan ta dawo fuskarta washe da fara'a ta kama hannun aysha ta jata zuwa ciki,a parlour suka ga asma'u zaune sanye da kayan bacci,kaman ko yaushe tana saqale da earpiece a kunnenta da alamu ma waya take,harara ta danqara musu wadda kowaccensu ta ganta,wata fara'a ta musamman aliya ta qirqira tana sake riqe hannun aysha sosai tana cewa
"Kinsan me goro family kuwa aysha?....ai ke Allah ne ya tarfawa garinki nono,dare daya dama Allah kanyi bature..." Ta qarashe fada suna tura qofar dakin ayshan suka shige,hannunta aysha ta cire bayan sun shiga din tana kallon aliya gami da kallon qofar dakin nata kaman wani zai shigo,dariya aliya ta bushe da shi har tana duqawa kadan
"Banson fitina aliya kin sani ko?" Ayshan ta fada a narke kamar mai shirin sanya kuka,bata tanka mata ba sai taja hannunta zuwa bakin gadon ayshan ta zaunar da su a tare sannan ta kalli gwaggo asabe
"Gwaggo kiyiwa aysha fada taiwa kanta fada...mijin da Allah ya bata da don jama'a da dama ne ba zata sameshi ba,bama shi ba gwaggo ko mai gadin gidansa ba zasu yarda ta aura ba....duk bata duba haka ba zata tsaya tana wani goce goce maras tushe ko dalili?,khalipha kaman wani tsanin ki ne na fita daga tsangwamar da kika dade kina fuskanta tsahon rayuwarki,Allah ya sani baki ma sanshi ba bare kiyi kwadayin abun hannunshi koda jama'a zasu fadi hakan,ke kinfi kowa sanin kanki,kinfi kowa sanin wacece ke" ta fada tana duban idanun ayshan kai tsaye sannan ta dafa kafadarta
"So pls aysha....ki nutsu ki fuskanci gabanki kawai...." Ta fadi tana sauke hannunta sannan ta cewa su gwaggo
"Ku shirya da sauri gwaggo....angon ya turo driver shi zai kaimu har qofar gida"
"To ma sha Allahu....kinga mun huta hawa ta haya kuwa" gwaggwon ta fada cikin farinciki,sannan daga bisani tayiwa ayshan dan fada da jan hankali,itakam kawai tana zaune tana jinsu,amma harga Allah tana da fargaba...su asma'u kawai sun isheta isharar tsamiyar talaka da mai kudi bata jiquwa waje daya...masu kudi basa qaunar talaka sam,kansu suke so,isu isu suke mu'amala da junansu,amma koma meye ta miqawa Allah zabinta.
"Lallai indo a gaisheki da qoqari,amarya guda da gyaran kitchen?,lallai" ta fada tana kama habarta alamar mamaki,da murmushi a fuskar aysha ta juyo ta kalli lantanar
"Banda abinki lantana wannan kitchen haka komai a hautsine,ta yaya zakuji dadin yin aikin?" Baki ta dan tabe tana aje farantan hannunta
"Wallahi gajiya nahi aisha....tun safe kana tsaye...ka gyara a bata,kowa kuma da kiran da zai maka....dama kuma kece mai juriyar,nikam nayi iya yina na gaji"
"Allah ya rufa asiri"
"Amin....ai gwara kiyi mana ma na bankwana,zamuyi kewarki wallahi indo" inji lantana tana nuna alhininta a fuskarta zuwa zuciya,sun saba da ayshan saboda sauqin kanta,hakanan sau tari takan amshe ayyukansu tayi idan tana da lokaci,ba ruwanta da qyamar mutum ko girman kai,ba kamar asma'u ba da basu taba jin dadinta ba,ayshan bata ce komai ba sai murmushi da tayi,wanda banda lotsawar da kumatunta yayi ma ba zaka gane hakan ba,kama mata lantanar tayi suka soma gyaran tare.
Basufi mintuna goma ba suka soma jiyo tashin hayaniya daga falon gidan,a hankali muryar anty safiyya tafi ta kowa fitowa
"Mu zasu nunawa iskancin banza iskancin wofi...mu zasu nunawa arziqi?,dama tun ranar kamu nake kula da take takensu,kai tun ranar kawo kaya,ina ruwanmu da wani familynsu ko arziqinsu,abinda muka sani kawai shine mun basu auren 'yar uwarmu,hakanan muma ba'a talauce suka ganmu ba bare suyi mana dagawa" ta qarashe fada tana huci
"Ke kinga yadda suke wani daddaga hanci da kallon kowa d'ai d'ai kamar kansu aka fara kudi,kina fa gani da muka shiga yiwa ango da amarya liqi sauka sukayi daga kan stage dinfa...." Anty kubra ta fada cikin jin haushi itama
"Su taka a hankali mi tsaf zan kora musu jawabi wallahi...ai muma ba tsiya suka ga tana binmu ko?....koma tsiyar ce a haka dansu yaga yarmu yace yana son aure" anty hajja wadda take qanwace ga momy ita ke binta ta fada.
"Kowa ya sayi rariya ai yasan zata zubda ruwa....tun daga yanayin halayyar yaron ya kamata su gane kowanne tsuntsu kukan gidansu yakeyi,don dai kai kawai baka isa ka fada bane baka da ikon gin magana" lantana ta fada,itadai aysha bata ce komai ba,tunda ba huruminta bane,har suka kammala ta wanke hannunta ta yiwa lantana sallama ta juya tabar kitchen din.
A kacame ta tadda falon,asma'u na kumfar baki anty safiyya nayi,da alama wani abun ne ya sake faruwa,tana jin anty safiyya na cewa
"Nikam babu matar data isa na sake jera kafada da ita bare ta wulaqantani bayan Allah bai wulaqantani ba,kije ku qarata ke dasu ke kika zabarwa kanki...banda shi mara mutunci ne har yace ki baiwa yan uwansa haquri sannan ya saurareki?" Cikin kuka asma'u tace
"Kinji ko mummy....wallahi ki mata magana,kinga zata jawo min matsala ko....nasan halin hamid wlh tsaf zai tsiri fushi da ni qarshenta ma sai wani satin za'a qarasa wani abun...nidai ki mata magana kawai"
"Ai na haifu,kuma 'yar halak ce ni...kije Allah ya bada sa'a" anty safiyya ta fada tana barin falon,ta haura sama dakin da suka sauka ita da sauran 'yan uwanta.
"Maganar gaskiya asma'u nima fa naji haushi...kuma hamid ya bani mamaki...ban zaci haka yake babu kwalli a idanunsa ba,giyar kudi na dibansa kenan?" Cewar anty kubra wadda sakuwa ce ta asma'un
"Kinga don Allah bana son qananun maganganu,nice dai zan aureshi na zauna da su,kuma naji ina son abina a haka ko yaya yake tunda shima yana sona" ta fadi cikin fada tana tasowa kubrar kamar zata doketa
"Allah ya bada sa'a" itama ta fada tana barin wajen,sai asma'un ta fada jikin mummy tana rushewa da kuka,duk sun hada mata zafi,gaba daya bikin yana neman juye mata,yaqi zuwa mata a dadin rai yadda taso,ga wannan tirka tirka da takeao ta kunno kai tsakanin dangin hamid din da nata,gefe guda kuma maganar aysha har yau na cin ranta,ba kamar yauma da take sake tambayar hamid waye muhammad abdulhakim mai goron,a yadda yake gaya mata waye shi ta tsorata matuqa,tana tsoron faruwar wani anu,tana tsoron kada reshe ya juye da mujiya,batason abinda zai sanya ta kasance itace a qasa har abada,koda yaushe tafison taga itace a sama sama da kowa.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Qarfe goma na safiyar washegari suka kammala shirinsu na wucewa takai,a sannan har aliya itama ta iso,ta ishi aysha da tambaya kan maganar data ce zasuyi,murmushi tayi kawai tace
"Me kike ci na baka na zuba?,zamuyi ai".
Sallamar lantana ita taja hankalinsu
"wani ne a waje yake jira wai an turoshi zai kaiku takai" cikin mamaki aysha ke kallon lanta
"Mu kuma?...takai?" Ta fada tana tunanin waye haka zai aiko?,iya tunaninta bata gane ko waye zai mata wannan karamcin ba,hakan yasa dole ya zira hijabinta tace
"Zo muje aliya inga ko waye" suka fice daga dakin.
Tun daga nesa ta gane baquwar mota ce ba irin ta gidansu ba,saidai bata iya ganin waye a ciki har ta qarasa gaban motar ta tsaya,murfin motar ne ya bude,wani matashin dan kimanin shekaru arba'in ya fito,cikin girmamawa yace
"Ranki ya dade boss ne ya aiko ni....ina fatan kun kammala shiryawa"
"Wanne boss?" Murmushi yayi sannan yace
"Wanne boss ne bayan muhammad khalipha?" Hannunta ta daga
"Ohk....ka koma kawai,zamu bi motar haya" ta fadi tana kama hannun aliyar dake binta da kallon tambaya suka juya.
Tana gab da shiga falon wayarta ta dauki ruri,dubawa tayi K ce ta bayyana kamar yadda tayi serving number dinsa
Numfashi ta aje sannan ta daga wayar ta kara a kunneta
"Me ya faru tsakaninki da sani,yace min wai ance ya tafi"
"Bbu komai,zamu bi motar haya ne kawai...."
"Bai dace ba aysha...maida hannun alkhairi baya fa kenan?"aliyata fada tana tsaye daga gefanta
"Aliya....kin san waye?"ta fada tana kallon hanya ba tare data dubi aliyan ba
"a'ah"ta bata amsa tana girgiza kanta dukka idanunta da hankalinta na kan ayshan
" khalipha ne fa aliya,wanda zan aura"
"Arrrrrrhhhhh" aliya ta fada tana rufe bakinta da tafukan hannayenta duka biyun kamar mai maitsoron kar wani yaji ihunta,idanunta a waje hakanan fuskarta qunshe da murmushi
"How comes sashen....tell me pls" juyowa tayi tana duban aliya,hannayenta harde a qirjinta,fuskarta a hade tsaf
"Khalipha ya saka min shakku mai yawa a kansa aliya....ta yaya zaizo min da wata fuska?,ta yaya zaizo min da wata siga?....a yadda khalipha yazo min aliya ashe ba haka bane....wannan ba yaudara bane?"
"Ya salam.....haba...ni nasan kaman na taba sanin face dinshi a wani waje wlh...kaman ya taba zuwa wajen abba na...oh my god...ina zuwa" aliya ta fada tana zame hannunta daga riqon data yiwa aysha,da sauri sauri kaman wadda zata tashi sama ta koma qofar gida,da idanu aysha take kallonta tana mamakin saurin me take ina zata?,me yasa bata ga alamun jimami ko tayata bacin rai kan abinda khaliphan ya aikata ba?.
Tana nan tsaye kaman sakarya har aliyan ta dawo fuskarta washe da fara'a ta kama hannun aysha ta jata zuwa ciki,a parlour suka ga asma'u zaune sanye da kayan bacci,kaman ko yaushe tana saqale da earpiece a kunnenta da alamu ma waya take,harara ta danqara musu wadda kowaccensu ta ganta,wata fara'a ta musamman aliya ta qirqira tana sake riqe hannun aysha sosai tana cewa
"Kinsan me goro family kuwa aysha?....ai ke Allah ne ya tarfawa garinki nono,dare daya dama Allah kanyi bature..." Ta qarashe fada suna tura qofar dakin ayshan suka shige,hannunta aysha ta cire bayan sun shiga din tana kallon aliya gami da kallon qofar dakin nata kaman wani zai shigo,dariya aliya ta bushe da shi har tana duqawa kadan
"Banson fitina aliya kin sani ko?" Ayshan ta fada a narke kamar mai shirin sanya kuka,bata tanka mata ba sai taja hannunta zuwa bakin gadon ayshan ta zaunar da su a tare sannan ta kalli gwaggo asabe
"Gwaggo kiyiwa aysha fada taiwa kanta fada...mijin da Allah ya bata da don jama'a da dama ne ba zata sameshi ba,bama shi ba gwaggo ko mai gadin gidansa ba zasu yarda ta aura ba....duk bata duba haka ba zata tsaya tana wani goce goce maras tushe ko dalili?,khalipha kaman wani tsanin ki ne na fita daga tsangwamar da kika dade kina fuskanta tsahon rayuwarki,Allah ya sani baki ma sanshi ba bare kiyi kwadayin abun hannunshi koda jama'a zasu fadi hakan,ke kinfi kowa sanin kanki,kinfi kowa sanin wacece ke" ta fada tana duban idanun ayshan kai tsaye sannan ta dafa kafadarta
"So pls aysha....ki nutsu ki fuskanci gabanki kawai...." Ta fadi tana sauke hannunta sannan ta cewa su gwaggo
"Ku shirya da sauri gwaggo....angon ya turo driver shi zai kaimu har qofar gida"
"To ma sha Allahu....kinga mun huta hawa ta haya kuwa" gwaggwon ta fada cikin farinciki,sannan daga bisani tayiwa ayshan dan fada da jan hankali,itakam kawai tana zaune tana jinsu,amma harga Allah tana da fargaba...su asma'u kawai sun isheta isharar tsamiyar talaka da mai kudi bata jiquwa waje daya...masu kudi basa qaunar talaka sam,kansu suke so,isu isu suke mu'amala da junansu,amma koma meye ta miqawa Allah zabinta.