Sashe 43
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A sanyaye ta koma dakinta,su mero suka zuba mata ido saidai ba wanda ya iya tambayarta komai,bankado qofar dakin da akayi shi yaja hankalinsu su duka suka daga kai suna kallon bakin qofar,gabanta ta qaraso yau qarara muraran take jin haushinta da kishi da ita ba tare kuma da tana da wani sahihin dalili kan hakan ba,wayarta ta cilla mata saman cinyarta
"Ke saka mana number khalipha wadda yake using da ita" a natse ta daga kai ta kalleta,tunda suke da ita yaune karo na farko data kirashi da khalipha sak ba yaron oga ba
"Waye khalipha?"harara ta watsa mata sannan tace
"yaron oga nake nufi"
"Ke da kika soma hadani da shi inaga ke zaki fi kowa samun lambarsa" ta furta anutse sannan ta miqe ta nufi toilet,wanda sanadiyyar tashin nata wayar ta subuto ta fadi qasa,hakan ba qaramin bata ran asma'u yayi ba
Cikin zafin nama da salo na huce haushi da takaici asma'u ta damqo hijabin aysha tana cewa
"Dawo dan uwarki...." Wani wawiyar fincika aysha ta yiwa hijabin nata cikin bacin rai da quna,duk yadda take da mahaifanta bata sake a zagesu,duk yadda suke duk kashinsu dai iyayenta ne,hakanan ba'a sauyawa tuwo suna,wani kallo ta watsawa asma'u,wanda hakan ya dan firgitata,saboda yadda lumsassun idanun ayshan masu kama dana wanda kejin bacci suka bude sosai a yau
"Karki kuskura ki sake zagemin mahaifiya....wannan shine kuskure na farko da zakiyi dana sanin aikatashi a kaina" tuni mamaki ya kashe asma'u,yau itace aysha ke maidawa magana haka gatsal kai tsaye,ayshan dako duka zata kai.mata ba zata daga kai ta dubeta ba,lallai abinda take gudu yana gaf da afkuwa,wato daga jin labarin wanda zata aura har ta soma komawa haka kenan?,lallai dole ta gaggauta daukan mataki tun wankin hula baikaita dare ba
"Ni aisha ni kikewa haka?" Ta fada cikin tsananin mamaki tana nuna kanta,bata tanka mata ba ta juya ta shige bandakin,itama asma'un sake juyawa tayi ta fice fuuu daga dakin zuwa falon daddy.
"Daddy ka dakatar da shi,kar kayi kuskuren aurawa aisha shi,mayaudari ne kuma maqaryaci ne shi,labarin haka yanzu ya zomin,daddy ka dakatar da aurensu" tsai dadddyn yayi yana kallonta ya kafeta da ido harta gama,bai taba tsammanin haka halayyar asma'un take ba sai yau,yaushe ta debo dukkan wadan nan dabi'un oho bai sani ba
"Jeki kiramin mahaifiyarki ku taho tare" ranta ne yayi sanyi,tana zaton zata cimma gaci taje ta taho da mummy,saidai kalaman daya soma furtawa da bude mata dukkan plan din data qulla kan aishan har Allah ya qaddara zata auri khalipha ya girgizata,ga akayi daddy yasan da dukka wadan nan abubuwan?,ya mata tas har hakan ya sanyata kuka mai yawa,tare da qara mata tsanar aisha,sosai yayi mata kaca kaca bai saurara ba,mummy tayi tsumu tana jinsu,ta kasa sanya baki saboda ita batasan ya zasu qarke ba ita da shi.
Haquri ta dinga bashi ta dinga bashi,tare da yi masa alqawarin ba zata sake maimaita kuskure makamancin hakan ba,ya umarceta taje ta nemi yafiyar aysha duk da Allah yayi mata sakayya,bayan ya sallameta mummy ya dirarwa,wanda hakan ba qaramin bacin rai ya haifar ba,ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba,ta nuna masa ita batasan meke faruwa ba,ya qalubalanceta ya kuma bata laifinta,haquri itama ta bayar cikin kissa tare da kwantar da kai,saboda bata son wani abu mara dadi ya bullo da zai bata bikinsu,tilas daga qarshe yayi haquri tare dayi mata gargadi mai qarfin gaske ta kuma amsa dukka laifin.
Shigarta toilet din alwala ta daura ko zata ji sauqin bacin ran dake yankar zuciyarta,saidai har ta fito hawaye bai yanke saman fuskarta ba,gefan gadonta ta zauna kai tsaye ta dauki wayarta,wannan karon babu fargaba ta kira mahaifiyarta,gab da zata tsinke aka daga
"Waye?" Aka tambayeta kamar yadda ta saba,alamu dake nuna har yau bata da matsayin da zati serving na numberta
"Nice ummi...Aisha ce 'yarki"
"Sau nawa zan fada miki ki daina kirana kafin ki gane abinda nake nufi?" Ta fada cikin salon tambaya,kafin aysha tayi yunqurin cewa komai ta ja tsaki gami da yanke wayar,kuka aysha ta saki mai sauti idanunta akan gwaggo asabe,a hankali ta tashi zuwa inda take ta zauna gabanta sosai tana dubanta
"Batasan zanyi aure ba...ba zata zo bikina bare na samu kowacce albarka da diya ke samu a wajen mahaifiyarta duk lokacin data tashi tafiya gidan miji,duk wata matsalata ni kadai na santa,ban taba dan dana dadin uwa ba,gwaggo...ke kadaice fata na na qarshe,ke kadai nake saka ran zan samu amsata daga bakinki...gwaggo...don girma da daraja ta annabin rahama ki gaya min...me na yiwa ummi na?,me na aikata mata haka daya saka ta tsaneni?,meye laifina meye kuma aibuna?" Ta qarashe maganar tana fashewa da kuka mai fidda sauti gami da kifa kanta saman cinyarta,hannu gwaggo asabe ta dora saman kan ayshan,tana jin dukkaninsu basu kyauta,dukansu masu laifi ne,suma kuma suna da tasu gudunmawar da suka taka wajen baqincikin da ayshan ke hadiya,a yau tana jin zata gayawa aysha dalilin wannan wakaci kaa tashin dake faruwa tsakaninta da mahaifiyarta,dukkaninsu a lokacin duk da sunji zafin abun basu zaci zaiyi tsanani har haka ba,ita kanta gwaggo asaben da take 'yar uwa ga ummin nata abun na bata haushi da takaici gami da mamaki,tamkar sake rabasu akayi bayan wancan dalilin daya zama silar wanzuwar komai
"Na roqeki gwaggo ki fiddani daga duhu izuwa haske,ki warwaremin wannan DAURIN BOYEN,na jima cikin zullumi tashin hankali tsoro da firgici saboda irin qiyayya qarara da nake ganowa daga idanun mahaifiyata....me yayi zafi gwaggo?" Ta qare da sigar tambayar kamar zata shide numfashinta zai tsaya
"Yau xan baki labari indo...yau in sha Allah ba zaki sake kwana da tunanin kin aikatawa mahaifiyarki wani laifi ba" ta fada tana sauke ajiyar zuciya,mero da ita tayi saura a dakin saboda karime tana waje bata shigo ba,saboda kusan itama tabi sahun 'yan takaici da jimami,dubanta gwaggo asabe tayi
"Zauna mero.....baki zama wata bare ba ko baquwar al'amarin"komawa tayi ta zauna tana tattara hankalinta wajen gwaggo asabe kamar yadda aysha tayi,shuru ne ya ratsa dakin kafin daga bisani gwaggo tace.
"kamar yadda kika sani cewa dangin mahaifinki fulani ne gaba da baya,yayin da mu dangin mahaifiyarki muka kasance manoma ne,har kakanki kafin Allah yayi masa rasuwa ya kasance sarkin noma na qauyenmu,fadan manoma da makiyaya fada ne daya jima yana wanzuwa tsakanin wadan nan mutane guda biyu,fada ne daya janyo asarar rayuka da dama,ya janyo asarar dukiyoyi rashin kwanciyar hankali da lumana,ya kuma janyo gurbacewar mu'amala tsakanin manoma da makiyaya,to wannan abu ya shafi qauyenmu,duk da cewa mu ba'ayi kashe kashe ba,amma rashin jituwa ya shiga tsakani da sabani mai girma,kowa ya tsayawa bangarensa,kowa yana goyan bayan dan uwansa da yake jin labari a can wani yanki an kashe ko anci zarafinsa,hakan ya kawo silar daya zama manoma da makiyaya basa ga maciji a tsakaninsu,a irin wannan ne Allah ya hada soyayya tsakanin mahaifinki baffale da mahaifiyarki,suna tsananin son junansu qwarai da gaske,sam basuyi duba da abinda kaje ya kawo ba,basuyi la'akari da abinda ke faruwa tsakanin jinsin biyu ba,soyayyarsu kawai suka saka a gaba,sanda soyayyarsu ta bayyana,kowa cikin gidansu sunja daga kan daya bazai auri daya ba,duk wata hanya ta rabasu anbi amma sunqi su rabu,junansu kawai suke so,bana mantawa mahaifiyarki ansha jibgarta a gabana amma bata sauya zani ba,a haka suka ci gaba da gudanar da soyayyarsu ba tare da sun yarda da qudurin raba su ba.
Sanda suka tada maganar aure gagarumar rigima ta barke cikin qauyenmu,abu har ya kai gaban alqali,inda yaja kunnen iyayen da su qyale yaransu suyu aure tunda suna son junansu,mai yiwuwa hakan ya zama silar kawo zaman lafiya a tsakani.
Toh tun asali mahaifiyarki macace mai zafi fada da kuma fushi,tana da wuyar saukowa a fushi idan ranta ya baci,hakanan bata yarda a take haqqinta ko waye zata qwaci kanta a hannunsa,tana da riqo idan ka bata mata,saidai takan sauko idan ka nemi yafiyarta,dalili kenan daya sake taka rawa wajen kawo hatsaniya tsakaninta da matar babanta inna kulu,kowa cikin fadin garin yasan ta da wannan hali,hakan ya sanya kaf 'yan matan qauyenmu ba yarinyar dake kawo mata wargi,mahaifiyar baffale ta miqe ta fadi wannan halaye nata,ta kuma ce ko donsu ba zata bari danta ya aureta ba,ba zata hada jini da ita ba.
An buga sosai kafin daga bisani Allah ya qaddara cewa sai baffale ya aureta,biki akayi sosai kasancewar tana da dangin mahaifiya a nan cikin birni,an mata komai na gata,jeran da babu tamkarsa,hakan ya sake hura wutar kishi a zuciyar faccalolinta tun kafin ta shigo,don duk cikinsu ba wadda ta samu irin gatan data samu,hakanan yadda baffale ke take take a kanta babu wadda ta samu irin wannan soyayyar.
To wani irin zama zance tayi cikin gidansu mahaifinki,tsakaninta da mijinta salamun salamun,zaman lafiya suke da qaunar juna,hakanan yana nuna mata qauna ko a gaban waye,nan fa qananun maganganun cikin faccalolinta da gutsiri tsoma suka soma yawa,kowacce kishi take da ita,saidai sunsan halinta duk wadda ta tareta gaba da gaba ta gaya mata maganar banza tofa itama ranta sai ya baci,ba zata qyale mace ba,suka dinga gutsura magana suna yiwa surukar tasu nuni data saka ido a rayuwar gidan baffale,suka karanta mata da alama ta mallakeshi,kasancewarsa shine qarami hakan yayi tasiri a ranta nan da nan,sannan uwa uba ga kuma kallon da take mata na yarinya mara kunya mara dagawa kowa qafa fitsararriya,nan fa aka fara sa toka sa katsi tsakanin su,mahaifiyarki ita kadai tsakanin faccaloli da uwar miji,amma da yake jarumar gaske ce duk ta iya da su,ta tare iskancin kowa,kuma bata fasa nuna soyayya da kulawa mijinta ba,tana matuqar sonshi hakanan tana kiyaye duk abinda baiso gami da bashi amanna,ta bashi yarda ta sakankance kan cewa bazai taba tozartata ko wulaqantata ba,mu kanmu a sannan mun jinjina mata da irin qoqarin zaman da tayi,a haka ake zaune har tsahon shekara guda,bata taba haihuwa ba sai bari da take yawan yi a kai akai,da wannan kuma suka samu dama suka tasa ta a gaba da habaici da gori,ba uwar mijin ba ba faccalolin ba.
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_
*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_
*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
(08030811300)
26
*DB*
"Ke saka mana number khalipha wadda yake using da ita" a natse ta daga kai ta kalleta,tunda suke da ita yaune karo na farko data kirashi da khalipha sak ba yaron oga ba
"Waye khalipha?"harara ta watsa mata sannan tace
"yaron oga nake nufi"
"Ke da kika soma hadani da shi inaga ke zaki fi kowa samun lambarsa" ta furta anutse sannan ta miqe ta nufi toilet,wanda sanadiyyar tashin nata wayar ta subuto ta fadi qasa,hakan ba qaramin bata ran asma'u yayi ba
Cikin zafin nama da salo na huce haushi da takaici asma'u ta damqo hijabin aysha tana cewa
"Dawo dan uwarki...." Wani wawiyar fincika aysha ta yiwa hijabin nata cikin bacin rai da quna,duk yadda take da mahaifanta bata sake a zagesu,duk yadda suke duk kashinsu dai iyayenta ne,hakanan ba'a sauyawa tuwo suna,wani kallo ta watsawa asma'u,wanda hakan ya dan firgitata,saboda yadda lumsassun idanun ayshan masu kama dana wanda kejin bacci suka bude sosai a yau
"Karki kuskura ki sake zagemin mahaifiya....wannan shine kuskure na farko da zakiyi dana sanin aikatashi a kaina" tuni mamaki ya kashe asma'u,yau itace aysha ke maidawa magana haka gatsal kai tsaye,ayshan dako duka zata kai.mata ba zata daga kai ta dubeta ba,lallai abinda take gudu yana gaf da afkuwa,wato daga jin labarin wanda zata aura har ta soma komawa haka kenan?,lallai dole ta gaggauta daukan mataki tun wankin hula baikaita dare ba
"Ni aisha ni kikewa haka?" Ta fada cikin tsananin mamaki tana nuna kanta,bata tanka mata ba ta juya ta shige bandakin,itama asma'un sake juyawa tayi ta fice fuuu daga dakin zuwa falon daddy.
"Daddy ka dakatar da shi,kar kayi kuskuren aurawa aisha shi,mayaudari ne kuma maqaryaci ne shi,labarin haka yanzu ya zomin,daddy ka dakatar da aurensu" tsai dadddyn yayi yana kallonta ya kafeta da ido harta gama,bai taba tsammanin haka halayyar asma'un take ba sai yau,yaushe ta debo dukkan wadan nan dabi'un oho bai sani ba
"Jeki kiramin mahaifiyarki ku taho tare" ranta ne yayi sanyi,tana zaton zata cimma gaci taje ta taho da mummy,saidai kalaman daya soma furtawa da bude mata dukkan plan din data qulla kan aishan har Allah ya qaddara zata auri khalipha ya girgizata,ga akayi daddy yasan da dukka wadan nan abubuwan?,ya mata tas har hakan ya sanyata kuka mai yawa,tare da qara mata tsanar aisha,sosai yayi mata kaca kaca bai saurara ba,mummy tayi tsumu tana jinsu,ta kasa sanya baki saboda ita batasan ya zasu qarke ba ita da shi.
Haquri ta dinga bashi ta dinga bashi,tare da yi masa alqawarin ba zata sake maimaita kuskure makamancin hakan ba,ya umarceta taje ta nemi yafiyar aysha duk da Allah yayi mata sakayya,bayan ya sallameta mummy ya dirarwa,wanda hakan ba qaramin bacin rai ya haifar ba,ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba,ta nuna masa ita batasan meke faruwa ba,ya qalubalanceta ya kuma bata laifinta,haquri itama ta bayar cikin kissa tare da kwantar da kai,saboda bata son wani abu mara dadi ya bullo da zai bata bikinsu,tilas daga qarshe yayi haquri tare dayi mata gargadi mai qarfin gaske ta kuma amsa dukka laifin.
Shigarta toilet din alwala ta daura ko zata ji sauqin bacin ran dake yankar zuciyarta,saidai har ta fito hawaye bai yanke saman fuskarta ba,gefan gadonta ta zauna kai tsaye ta dauki wayarta,wannan karon babu fargaba ta kira mahaifiyarta,gab da zata tsinke aka daga
"Waye?" Aka tambayeta kamar yadda ta saba,alamu dake nuna har yau bata da matsayin da zati serving na numberta
"Nice ummi...Aisha ce 'yarki"
"Sau nawa zan fada miki ki daina kirana kafin ki gane abinda nake nufi?" Ta fada cikin salon tambaya,kafin aysha tayi yunqurin cewa komai ta ja tsaki gami da yanke wayar,kuka aysha ta saki mai sauti idanunta akan gwaggo asabe,a hankali ta tashi zuwa inda take ta zauna gabanta sosai tana dubanta
"Batasan zanyi aure ba...ba zata zo bikina bare na samu kowacce albarka da diya ke samu a wajen mahaifiyarta duk lokacin data tashi tafiya gidan miji,duk wata matsalata ni kadai na santa,ban taba dan dana dadin uwa ba,gwaggo...ke kadaice fata na na qarshe,ke kadai nake saka ran zan samu amsata daga bakinki...gwaggo...don girma da daraja ta annabin rahama ki gaya min...me na yiwa ummi na?,me na aikata mata haka daya saka ta tsaneni?,meye laifina meye kuma aibuna?" Ta qarashe maganar tana fashewa da kuka mai fidda sauti gami da kifa kanta saman cinyarta,hannu gwaggo asabe ta dora saman kan ayshan,tana jin dukkaninsu basu kyauta,dukansu masu laifi ne,suma kuma suna da tasu gudunmawar da suka taka wajen baqincikin da ayshan ke hadiya,a yau tana jin zata gayawa aysha dalilin wannan wakaci kaa tashin dake faruwa tsakaninta da mahaifiyarta,dukkaninsu a lokacin duk da sunji zafin abun basu zaci zaiyi tsanani har haka ba,ita kanta gwaggo asaben da take 'yar uwa ga ummin nata abun na bata haushi da takaici gami da mamaki,tamkar sake rabasu akayi bayan wancan dalilin daya zama silar wanzuwar komai
"Na roqeki gwaggo ki fiddani daga duhu izuwa haske,ki warwaremin wannan DAURIN BOYEN,na jima cikin zullumi tashin hankali tsoro da firgici saboda irin qiyayya qarara da nake ganowa daga idanun mahaifiyata....me yayi zafi gwaggo?" Ta qare da sigar tambayar kamar zata shide numfashinta zai tsaya
"Yau xan baki labari indo...yau in sha Allah ba zaki sake kwana da tunanin kin aikatawa mahaifiyarki wani laifi ba" ta fada tana sauke ajiyar zuciya,mero da ita tayi saura a dakin saboda karime tana waje bata shigo ba,saboda kusan itama tabi sahun 'yan takaici da jimami,dubanta gwaggo asabe tayi
"Zauna mero.....baki zama wata bare ba ko baquwar al'amarin"komawa tayi ta zauna tana tattara hankalinta wajen gwaggo asabe kamar yadda aysha tayi,shuru ne ya ratsa dakin kafin daga bisani gwaggo tace.
"kamar yadda kika sani cewa dangin mahaifinki fulani ne gaba da baya,yayin da mu dangin mahaifiyarki muka kasance manoma ne,har kakanki kafin Allah yayi masa rasuwa ya kasance sarkin noma na qauyenmu,fadan manoma da makiyaya fada ne daya jima yana wanzuwa tsakanin wadan nan mutane guda biyu,fada ne daya janyo asarar rayuka da dama,ya janyo asarar dukiyoyi rashin kwanciyar hankali da lumana,ya kuma janyo gurbacewar mu'amala tsakanin manoma da makiyaya,to wannan abu ya shafi qauyenmu,duk da cewa mu ba'ayi kashe kashe ba,amma rashin jituwa ya shiga tsakani da sabani mai girma,kowa ya tsayawa bangarensa,kowa yana goyan bayan dan uwansa da yake jin labari a can wani yanki an kashe ko anci zarafinsa,hakan ya kawo silar daya zama manoma da makiyaya basa ga maciji a tsakaninsu,a irin wannan ne Allah ya hada soyayya tsakanin mahaifinki baffale da mahaifiyarki,suna tsananin son junansu qwarai da gaske,sam basuyi duba da abinda kaje ya kawo ba,basuyi la'akari da abinda ke faruwa tsakanin jinsin biyu ba,soyayyarsu kawai suka saka a gaba,sanda soyayyarsu ta bayyana,kowa cikin gidansu sunja daga kan daya bazai auri daya ba,duk wata hanya ta rabasu anbi amma sunqi su rabu,junansu kawai suke so,bana mantawa mahaifiyarki ansha jibgarta a gabana amma bata sauya zani ba,a haka suka ci gaba da gudanar da soyayyarsu ba tare da sun yarda da qudurin raba su ba.
Sanda suka tada maganar aure gagarumar rigima ta barke cikin qauyenmu,abu har ya kai gaban alqali,inda yaja kunnen iyayen da su qyale yaransu suyu aure tunda suna son junansu,mai yiwuwa hakan ya zama silar kawo zaman lafiya a tsakani.
Toh tun asali mahaifiyarki macace mai zafi fada da kuma fushi,tana da wuyar saukowa a fushi idan ranta ya baci,hakanan bata yarda a take haqqinta ko waye zata qwaci kanta a hannunsa,tana da riqo idan ka bata mata,saidai takan sauko idan ka nemi yafiyarta,dalili kenan daya sake taka rawa wajen kawo hatsaniya tsakaninta da matar babanta inna kulu,kowa cikin fadin garin yasan ta da wannan hali,hakan ya sanya kaf 'yan matan qauyenmu ba yarinyar dake kawo mata wargi,mahaifiyar baffale ta miqe ta fadi wannan halaye nata,ta kuma ce ko donsu ba zata bari danta ya aureta ba,ba zata hada jini da ita ba.
An buga sosai kafin daga bisani Allah ya qaddara cewa sai baffale ya aureta,biki akayi sosai kasancewar tana da dangin mahaifiya a nan cikin birni,an mata komai na gata,jeran da babu tamkarsa,hakan ya sake hura wutar kishi a zuciyar faccalolinta tun kafin ta shigo,don duk cikinsu ba wadda ta samu irin gatan data samu,hakanan yadda baffale ke take take a kanta babu wadda ta samu irin wannan soyayyar.
To wani irin zama zance tayi cikin gidansu mahaifinki,tsakaninta da mijinta salamun salamun,zaman lafiya suke da qaunar juna,hakanan yana nuna mata qauna ko a gaban waye,nan fa qananun maganganun cikin faccalolinta da gutsiri tsoma suka soma yawa,kowacce kishi take da ita,saidai sunsan halinta duk wadda ta tareta gaba da gaba ta gaya mata maganar banza tofa itama ranta sai ya baci,ba zata qyale mace ba,suka dinga gutsura magana suna yiwa surukar tasu nuni data saka ido a rayuwar gidan baffale,suka karanta mata da alama ta mallakeshi,kasancewarsa shine qarami hakan yayi tasiri a ranta nan da nan,sannan uwa uba ga kuma kallon da take mata na yarinya mara kunya mara dagawa kowa qafa fitsararriya,nan fa aka fara sa toka sa katsi tsakanin su,mahaifiyarki ita kadai tsakanin faccaloli da uwar miji,amma da yake jarumar gaske ce duk ta iya da su,ta tare iskancin kowa,kuma bata fasa nuna soyayya da kulawa mijinta ba,tana matuqar sonshi hakanan tana kiyaye duk abinda baiso gami da bashi amanna,ta bashi yarda ta sakankance kan cewa bazai taba tozartata ko wulaqantata ba,mu kanmu a sannan mun jinjina mata da irin qoqarin zaman da tayi,a haka ake zaune har tsahon shekara guda,bata taba haihuwa ba sai bari da take yawan yi a kai akai,da wannan kuma suka samu dama suka tasa ta a gaba da habaici da gori,ba uwar mijin ba ba faccalolin ba.
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_
*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_
*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
(08030811300)
26
*DB*