← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 114

Sashe 26

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ina cikin wannan halin labarin yin auren ummina ya sameni,na tsinceshi ne ina daga kurkukun da aka sakani,zaman da matan gidanmu keyi qasan bishiya na kisan dabe daga safiya zuwa yammaci,an baje kolin maganar kowa na tofa albarkacin bakinsa,a nan naji cewa a legos zata zauna,ta samu mijin ne cikin dangin mamarta dake birni,kusan duk wanda zai bude baki yayi magana a kai ba alkhairi zai fada ba,sai mugun abu yarfe da sharri,duk da cewa na danji kishin wani da zata aura bayan ga baba na amma na mata murna jin zata samu ci gaba ne,duk da bata damu da rayuwata ba,haka aka sha biki cikin garin na kece raini da tsone idon 'yan adawa,yako tsone din,don zama na musamman akayi cikin gidan har na kwanaki biyu ana tattauna abinda aka gani wajen bikin da abinda ya faru,don faccalolinta banda inna talle da tata adawar ta bilhaqqi ce ba wadda bata je ba bata kuma riqo tsarabar gidan bikin ba,ina daga daki ina jiyo qarar motocin da suka zo suka dauki ummina tabar garin takai zuwa legos,a sannan kamar nayi tsuntsuwa naje na taresu na ganta koda ba zata min magana ba,koda zata dakeni,koda zata tsinemin din kamar yadda tace,don ban sani ba shin zan sake ganinta ko mun rabu kenan?,a haka ina hawaye har na daina jiyo sautin motocin.

Tun daga ranar ban sake ganin ummi na ba sai idan tazo garin ganin gida,duk sanda ko zata zo din zan saki jiki na jima a soron gidan baba ina kallonta,koda kuwa waye ya aikeni,ko aiken waye a hannuna,a sannan duka sa'anni na suna gidan aurensu,a masu shekaruna ni kadai na rage cikin gidan.

Wani zubin kuma hanyar da take bi nake zuwa na zauna,ina sane nake fitowa wai yadda zata ganni ko ta manta da ni ne,sau tari idan muka hada ido harara take cilla min ko taja min qwafa,ta rage duka na,don wani bin har tazo ta tafi ba zaka ga ta dakeni ba,hakan kuma ina zaton baya rasa nasaba da girma da taga na fara,saidai ban isheta kallo ba,ko muhalli kuma bata yarda mu hadanikam kallonta kawai nake yadda ta canza lokaci daya tayi kyau,a yadda naji mutanen gidanmu na gulmar mijinta yana da shi,tana kuma jin dadi fiye da gidanmu data bari nesa ba kusa ba.

A haka rayuwa taci gaba da garamin,ga girma na fara yi,a lokacinne na samu mutum daya yake kulani saboda qazanta ta da rashin gyara wato dan ladi,babu mutumin dana tsana a rayuwata sama da shi,saboda tantirin dan iska ne,haka nan cikakken dan shaye shaye,babu nau'in abun mayen da baya sha kaf cikar fadin garinmu an sanshi,a hakan kuma 'yan gidanmu tayani murna suke an samu mai sona,idan dan ladi zai shekara bina da yimin magana bazan kulashi ba saboda haushinsa nake ji,a haka dai bai haqura ba yake bibiyata,duk da shima wani lokaci idan ya gaji yaba min maganganu yake
"Dalla can donma na rufa miki asiri nace zan aureki?,waye ma ya taba cewa yana sonki?,aibu fal tattare dake,uwarki ma data kawoki duniya gudunki take amma ni na bugi qirji nace ina sonki,banza mara rabo,kuma wallahi saina aureki inga ta tsiya" iren iren wadan nan kalaman yake jifa na da shi koda a hanya muka hadu gaban mutane,bama irin ranar da yake a cakensa.

A haka ummi na tayi haihuwar farko ta haifi mace,duk sanda tazo garin saina aika yara a zuwan qawarta ke aikowa a bani yarinyar ta dade a waje na,ina son yarinyar ina qaunarta sosai,inajin kamar ota kadai nake da ita a duniya,hakan ya sanya basma ta saba da ni ta shaqu da ni,sam ummi bata farga da hakan ba sai da basma ta soma wayo ta fara yawaita yi mata zancena,a nan naga tashin hankali,tayimin duka ta kuna koran gargadi mai qarfi babu ni babu ita,itama basman bata qyaleta ba,saidai ko gezau bamuyi ba,duka kuwa muna shanshi bama ya kamar sanda basman ta sake wayo,take debo kayan bayarwa cikin na mamanta da nata take kawo min,ranar dukanmu ta hada ta daka ta kuma jefoni waje tare da aikawa gidanmu ayimin gargadin zuwa gidansu tunda ba gidanmu bane,haka inna yelwa ta dinga bala'i da masifa,shikenan duk sanda tazo gari bani ba sake fita har sai tabar garin.

*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKO SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*

*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_

*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_

*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_

*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_

*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_

*DB*

17

Tashin hankali na gaba dana sake fuskanta shine shirin aurar da ni da ake ga dan ladi,wanda babu wanda ya tambayeni ko ya tsaya jin ra'ayina aka bada ni gareshi,tamkar auren sadaka zance aka shirya yimin,domin babu abinda dan ladin ya kawo gidanmu da sunan kudin zance kayan sa rana da sauransu,hasalima sake tunzurashi ake akan cewa ya taimaka su rabu da qaya,domin wai na tasamma tsufa a gabansu,duk da cewa duka duka a sannan ban wuce shekara goma sha uku cikin ta sha hudu ba,duk da lalacewa irin ta dan ladi wai mahaifiyarsa qyama take ya aureni,tana cewa za'a joganawa danta ni,danta yafi qarfin aurena,amma da yake dai Allah ya hukunta cewa sai na shiga gidansu na dandani tasu kalar azabar haka aka daura aurena da shi,babu wani abu dake nuna cewa bikin yarinya budurwa ake,duk wani gata da akewa budurwa yayin auren fari ni ban sameshi ba ban ganshi ba,a wannan lokaci nayita zuba idanu ko zanga ummi na amma shiru,bama ganinta ba,naso ace ko wani motsi nata da zai nuna tana sane da ni ko tana sane da aure na nasamu daga gareta amma maqatau,hakanan dangin mamata suka hado kayan da zasu iya dai dai qarfinsu suka kawo amma inna yelwa ta aje gefe tace sam ita da taba kayan zuri'ar gidansu ummina,ta hadamin buta tukunya da kwanukan cin abinci,sai katifa da labulaye da fulalluka iya abinda aka jera min kenan aka daukeni ziqau babu gyara aka kaini,hana rantsuwa dai ranar an sakani nayi wanka da kyau.

Tunda aka kaini dakina qwaya daya wanda aka jawa katangar kara da makewayi kusa da shi nake zaune ina raba idanu,santin dakin nake a raina saboda sau dubu yafi bolar da nake kwana kyawun gani,tun ina jiyo hayaniyar jama'a har gidan ya dauki shuru,ina nan zaune bansan sanda tsohuwar gajiya ta sanyani na sulale nabi lafiyar ledar da aka malalawa tsakar dakin ba.

Faduwar abu da naji yif a kaina shi ya farkar da ni a zabure nayi yunqurin miqewa,saidai nauyin da yake kaina ya fi qarfina,sai dana lura da kyau naga ashe dan ladi ne,wanda maganganun da yake furtawa kawai sun isa su gaya maka a make yake qwarai..."qasa aysha tayi da kanta,cikin jin nauyi da kunya tace
"Nayi alqawarin bazan boye maka komai ba.....idan nace komai ina nufin harda rayuwar aure na da danladi....a wannan daren dan ladi ya nemi karbar haqqinsa ta qarfi,saidai sam naqi yarda,haka muka dinga artabu da shi cikin dakin,wanda daga qarshe da yaga ina neman gajiyar da shi ya kamani ya yimin duka dan gaske wanda sai da naji a jikina,duk da na saba da duka kusan ni jakarsa ce amma wannan ya shiga jikina matuqa,saboda an yishi ne cikin fitar hayyaci,kafin kace meye fuskata ta kumbure haka jiki na,yadda naga rana haka naga dare,amma duk da hakan ban fasa tashi sallar asuba ba yadda na saba,bayan na gama na samu na rabe gefe guda ina maida numfashin wahala,idanu na kan dan ladi dake baje saman katifata,ni kuwa gani kwance kan dandanyar ledar daki.

Bashi ya farka ba sai tara na safe,zuwa lokacin har tsakar gidan gidan ya cika da hayaniya kala kala ta yara da manya,da alama kowa ya shiga sabgarsa,tashi yayi yana hardewa wanda hakan ke nuna bai gama wartsakewa ba ya dubeni ya watsan harara gami da jan qwafa,da alama yana sane da abinda ya faru jiya kuma yana qufule da ni,ficewarsa yayi,tunda ya fice din kuwa ba wanda ya nemi ni hatta da shi kanshi,sai da sha biyun rana ta kusa naga yunwa na shirin hallakani na miqe na debi ruwa na shiga makewayi nayi wanka,na cika kofi da ruwa na sha,na danji dama dama a jikina sannan na saka hijabina na fito cikin gidan,gida ne kamar namu na mutane da yawa,matan yayye da matan qanne da uwar miji,haka aka dinga bina da kallo wanda nasan baya rasa nasaba da sanin wace ni da kuma kokawarmu ta daren jiya da.nasan mafi yawa sunyi zatan wani abu ne ya faru,nidai na gaidasu na wuce wajen mamar dan ladi da suke kira da fatsi,tun daga yanayin amsa gaisuwarta nasan cewa akwai wata a qasa,ilai kuwa hakanne,domin kuwa na sake fadowa jahannama ta biyu ce,duk wata bauta ta gidan kusan a kaina take,zagi hantara da gori kuwa babu kalar wanda ba'a yimin,babu wanda ban haddace ba cikin qwaqwalwata,gefe daya kuma idan dare yayi mu hadu da dan ladi wanda kullum sai yayi yunqurin karbar haqqinsa ni kuwa naqi bada hadin kai,saboda bala'in qyanqyaminsa nake ga tsoro dake tattare da ni,uwa uba qiyayyar da nake masa,idan ya gama yunqurinsa haqarsa bai cimma ruwa ba sai ya kamani yamin duka,wansa hakan bazai hana gobe da sassafe na tashi aikin gida ba koda wanne irin ciwo naji wannan ba ruwan mama fatsi bane,sau tari takanmin habaici da gugar zanar ita bata ga me nakeyi a gidan ba bata ga amfani na ba,ashe rashin tarbiyyar dan ladi ta kai ya gaya mata cewa har yau bai karbi haqqinsa a wajena ba,randa na gane hakan takaici kunya da baqinciki sun sakani kuka mai yawan gaske.

A haka naci gaba da zama cikin wannan uquba,ko qofar gida ban taba leqawa ba bare nayi tunanin zuwa gida,duk da suma gidan ba ruwansu da ni,ba wanda ya taba takowa inda nake idan ka debe yan qananun yaran gidan da basu san me ake ba,idan yawonsu ya debosu zasu shigo gidan,a nan zanta jin dadi in riqesu ina aiki muna hira ina tambayarsu mutanen gidan suna bani labarin abubuwan da suka faru da bana nan,koyaya dan uwa yake yana da dadi,hakan na yimin dadi kuma yana deban kewa.
Chapter 26 · 0% Book details