← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 114

Sashe 11

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Babu wata cikakkar fara'a a fuskarta haka ta iso
"Mun yini lafiya"
"Lafiya lau ya mutanen gidan"
"Suna lafiya....." Ta amsa ciki ciki
"Ina saqon?" Ta buqata kai tsaye saboda tana tantamar idan ka ya kawo din
"Gasu nan" ya fada hannayensa na harde a qirjinsa ba tare da ya motsa ba yana karantar yanayinta lamarin na sake bashi tsoro da mamaki,sai ya cire hannunsa daya ya saka cikin aljihun wandonshi,ganin haka ya sanyata tadan saki ranta sannan tace
"Ok....mu shiga daga ciki mana" ta fada tana duban qofar gidan sannan ta maido idanunta kanshi,kafadunsa ya daga duka biyun yana ci gaba da qoqarin zaro kudin,ba tare daya dubeta ba yace
"Ba sai na shiga ba,abinda kika fi buqata na kawo miki kawai muyi sallama na wuce" bata fahimci komai ba haka bata ce komai ba,saboda hankalinta dukka yana kan kudin daya ciro a aljihunsa,wanda kai tsaye bata ce ga adadinsu ba,bandir bandir ne sababbi kar a miqe na 'yan dubu dubu guda biyar,sai 'yan dari biyar biyar kuma daban,wadan can ya maida aljihunsa ya irga 'yan dari biyar biyar din dubu goma ya miqa mata yana kallonta
"Lissafa kiga sun kai?" Amshewa tayi,cike da zumudi qasan ranta tare da fatan samun qari ta lissafa cikin qwarewa sannan tace
"Sun cika" sai ya kada kai ya sake ciro wadancan bandiran yana dubanta yace
"Nawa kika ce kina buqata a baya?" Farrrr tayi da ido dadi na ratsata,addu'arta ta karbu cikin zumudin daya kasa boyuwa tace
"40k kawai nake buqata,ina zaton zata isheni komai da komai" sai ya miqa mata dukkan kudaden hannun nasa yace
"Zaki iya gane nawa ne nan ko?" Cikin zumudi bakinta a washe tace
"Yes,duk bandir daya dubu dari ce,duka wannan five hundred thousand kenan"kai ya gyada hannayensa soke cikin aljihunsa,ya dan shaqi iska sannan yace
"ki riqe duka na baki" idanunta ta waro baki daya tana jujjiya kudin cikin rudewa tace
"Kai muhammad please da gaske kake?,dama ka samu kudin kake ta min wasa da hankali haka,oh my god sweetheart na gode na gode,dama ni na sani ba zaka barni naji kunya ba,dama ashe wasa kake min"
"Eh....gwadaki nake.....kuma kinyi failing....baki ci wannan jarabawar ba khadija,kin fadi warwas har abada" sai kuma ta dan saurara daga murnar da take tana dubansa cikin mamakin kalamanshi
"Kamar yaya wacce iriyar jarabawa?"murmushi ya fidda mai kyau wanda ya sake fitar da kyan surarshi,sai taga yau taga yafi kullum yi mata kyau,ya zaro wayarsa yana dannawa wadda khadijan ta bita da kallo,idan bata manta ba wancan satin ta taba tambayar kudin wayar taji tafi qarfin kanta,don har saurayinta ta tamnaya ya siya mata ita a sannan yace bata da hankali,ashe ba qananun kudi ta baro masa ba, cikin burgewa take bin wayar da ido,idanunsa na kan screen din wayar yace
"Kudi kike so khadija bani ba,kudi sunfi miki soyayyata,sune gaba da komao a wajenki....gasu nan na baki su a madadina...as from today ki saka a ranki baki taba sanin wani mai suna muhammad ba a rayuwarki ko mai kama da shi,kisawa ranki kamar a mafarki alaqarmu ta taba wanzuwa....." Ya qarashe maganar yana kashe wayar tare da maidata aljihunsa fuskarsa qunshe da murmushi wanda take cakude da mamaki,haushi al'ajabi da takaicin halayyar 'yammatan yau,yayin data saki baki kawai tana binsa da kallo saboda lissafinta dake neman dagulewa lokaci guda.

Kunya da tsoron rasashi a sanda ta fahimci wayeshi suka dabaibayeta,tsoron subucewarsa daga hannunta a sanda ta gane cewa type dinta ne shi suka cikata,cikin qoqarin kare kai ta bude baki da niyyar bawa kanta kariya,saidai isowar motocinsa wajen yasa ta kasa furta komai,a gabanta ilyas daya daga cikin yaranshi ya bude masa bayan motar ya shige ba tare da ya sake koda waiwayarta ba,tana kallo suka janye motocin suka fice daga layin suka barta tsaye riqe da rafas din kudi.

Har suka bace daga layin tana tsaye tana bin kyawawan baqaqen motocin da kallo mamaki ya daskarar da ita,da gaske wannan shine ainihin muhammad ba wanda ta sani ba?,shin mafarki take ko gixo idanunta ke mata,saita maida idanunta kan kudin tana jujjuyasu tare da qare musu kallo,qwaqwalwarta a daure take tamau,ta rasa me zata aiwatar,takai hancinta ta shanshanasu,wani irin lallausan qamshi suke fitarwa irin mai kwantar da zuciya,take nadama da dana sani suka lullubeta,ya akayi ta kasa boye zalamarta?,ya akayi ta kasa gane cewa muhammad ba qaramin mutum bane?,iya motoci kawai data gani na biye da shi da kyautar daya mata a yanzu sun isa bata amsar cewa shi din wani ne,shi din isashshe ne,sam bata jin zata iya haqura da shi,asarace da ba zata iya jurewa ba,samun irinsu muhammad a wannan zamanin tamkar gudun yada qanin wani ne ga 'ya mace,mai rabo ke samu,zata san yadda zata lallabashi ta dawo da shi cikin rayuwarta,tabbas sai ya zama mallakinta cikon burin rayuwarta kenan,jiki a salube ta juya ta shige gidan tana gyara riqon kudin a hannunta zuciyarta cike da zulumi da fargabar kada ta rasa muhammad daga rayuwarta.
*_WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER (08030811300)_*

*DAURIN BOYE*

*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*

09

A gaggauce ta tsame hannunta daga cikin flour din da take kwabawa ta dauraye hannunta ta goge jikin towel sannan ta fita a kitchen din don amsa kiran da mommy sa'adah keta qwala mataba tare da tayi la'akari da aikin data sanyata take yi ba

Cikin bedroom dinta ta taddata,tana zaune gefan gado,daga daura da ita kayan turarukan wuta ne lodi guda da alama lissafinsu takeyi,yar lelen nata kuma na gaban madubi tana ta shafe shafe da qalqale qalqale,saboda yau fita ce ta musamman zatayi,dinner ake na wata cikin qawayenta na makaranta da take aure,qawaye ne irinta 'yan ji da kai da daukar duniya da fadi,su kansu kayan da zata sanya a ranar order dinsu aka yi mata bayan an musu dinki na musamman,ba'a maganar jaka da takalmin da zata sanyawa qafafunta na kudade masu yawa.

"Mommy gani" aysha ta furta tana rusunawa gefan mommyn,wayarta ta aje sannan ta dubeta
"Saura me da me ki kammala ne?,qarfe shida na yamma fa zasu soma taron,kuma nasan tana can tana jira"
"Mommy na gama komai da komai,doghnout din ne naga kamar bazai isa ba shine zan dan qara yawanshi"
"Zaikai kamar nan da minti nawa?" Ta tambayeta bayan ta kalli agogo
"Awa daya ko minti hamsin"
"To kiyi sauri ki gama din,saboda ke zan aika ki kai matan"
"To mommy" ta fadi tana miqewa tare da qoqarin ficewa daga dakin
"Idan kin gama ki debi komai kimin packaging,ki hada masa dambun kazar nan da kika ma daddy last week,yau nake xaton hamid zai dawo gobe zai shigo waje na" cewar asma'u dake goga jambaki kan lebanta,wanda ta bada umarni ne kawai ba tare data waiwayo ta dubi wadda ta bawa umarnin ba
"Toh" shine abinda aysha ta fada tana ficewa daga dakin cikin ranta tana fadin autan maza,hamid shine saurayin asma'u data zaba cikin dubban samarin da Allah ya bata a matsayinta na budurwa 'yar qwalisa wadda har ranta takejin duniya na damawa da ita,me ji da kyau aji ado da gata takowanne fanni,hamid ya yiwa asma´u dari bisa dari,tana jin ya dace da tsarinta ya kuma yi dai dai da ra´ayinta,hamid matashin saurayin dan kasuwa ne maiji da gata da kuma dukiya,mutum ne shi mai shegen son girma,son matsayi da qyamatar mu'amala da duk wani wanda baikaishi arziqi ba,tafiyarsu tazo dai dai da asma'u saboda katarin hali da akayi yazo guda,soyayya ake bugawa sosai,wani irin so asma'u take masa wanda yake baiwa kowa mamaki,irinson da ba'a taba ganinta ta yiwa wani d'a namiji shi ba,saboda ta jima tana jan maza a qasa,tana daga musu kai da hura musu hanci saboda baiwar kyau da Allah ya bata da iya kwalliya,uwa uba gata data samu daga wajen uwa da uba kasancewarta auta a gidansu,saidai tashin farko ta matowa hamid,ya rushe duk wani plan nata ya tafi da zuciyarta,a yanzu haka babu wanda baisan da zaman soyayyarsu ba,haka nan ta tsaidashi a matsayin wanda zata aura,saidai iyaye duka basu shiga ciki ba,saboda tana da plan din sai ta gama degree dinta sannan a soma maganar aurensu,shi dinma hakan ya masa shi yasa komai ke tafiyar musu dai dai,suke kuma gudanar da soyayyarsu hankali kwance.

Sam jinin aysha da hamid zan iya cewa bai hadu bane ko kuma banbancin halayya ya sanya hakan,tsakaninta da shi gaisuwa,sai ko idan yazo ta miqa masa kayan maqulashen da asma'u ke sawa ta hada masa ta kama gabanta,yana da ji da kai girman kai da kuma daga kai da jin shi wani ne,wannan halayyarsa ce a jininsa.

Cikin awa gudan ta kammala komai ciki harda wanka,ta shirya tsaf cikin lace bayan ta nannade jikinta da laffaya wadda ta dace da shigarta,ita ba ma'abociyar son kwalliya bace,hakan ya sanya kaso hamsin na kyawunta ke boyewa idan ba ka mata kyakkyawan kallo ko kyakkyawan sani ba,ita dai barta da qamshi,tana son qamshi,kuma dukkan turaren da take amfani da shi ba mai hayaniya bane,saika matsa kusa da ita zaka dinga jin tashinsa,kuma a hankali,yawanci tafi ta'ammali da turaren kaya haka sai rollon body spray masu kyau da dadi tamkar wata babarbariya.

A parlour ta tadda momy tsaye tana amsa waya,dai dai sanda asma'u ta fito,ba banza ba ta kashe awa guda tana kwalliya,ba qaramin kyau tayi ba,duk wanda ya ganta kuma dole ya sake juyawa ya kalleta,ankon lace din yayi masifar karbarta,uwa uba make up din da tayi
"Hey momy sai na dawo" ta fada tana ficewa cikin hanzari tana kada muqullin mota,itama hannu mommyn ta daga mata cikin dan daga murya take cewa
"Kiyi qoqarin dawowa kafin daddynku ya dawo kinji na gaya miki" daga haka ta maida wayarta taci gaba da yi,hannun kujera aysha ta samu ta zauna idanunta kan film din da ake haskowa a tashar zee world hannayenta rungume a qirjinta tana jiran mommy ta gama wayar ta bata umarnin tafiya,sai data gama din sannan ta dubeta
"Na saka usama ya sanya komai a cikin mota,a motar asma'u zakuje saboda ta fita a tawa,na mata bayanin komai ki gaisheta idan kinje"amsa mata tayi ta miqe ta fice daga falon yayin data bar mommy na zama saman kujera tare da qwalawa daga cikin 'yan aikinta kira ta kawo mata drinks.
Chapter 11 · 0% Book details