Sashe 110
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Qarfe goma da wani abu na safiya suke takawa cikin asibitin hannayensu sarqafe da juna,duk wanda ya kallesu saiya sake juyawa ya dubesu,kana kallonsu kasan cewa masoya kuma ma'auratan da suka dace da juna,ba qaramin kyau sukayi ba,shi yana sanye da suit yayin da take sanye da atamfa dinkin doguwar riga,fuskarta tayi wani irin kyau,tayi fresh abinta saika dauka wani makeup tayi,saidai babu komai a fuskar tata sai powder kwalli da man lebe,gab da zasu shiga cikin asibitin ya daga waya ya kira annin ya tambayeta dakin da aka kwantar da kawu idris ta gaya mishi,ya kashe wayar ya maida aljihunsa yana sakin ajiyar zuciya,hannunshi ta riqe sosai tsam saboda tasan yanzun ranshi zaya baci,tasanya daya hannun nata ta zare glass din fuskarta ta lanqwasheshi cikin hannunta,juyowa yayi suka hada idanu saita narke masa tana tsayawa daga takawar da suke zuwa cikin asibitin,gira ya daga mata alamar tambaya,a shagwabe tace dashi
"Ya khalipha pls mana,idan kasan ranka zaya baci ba zaka saki ranka ba ka tsaya ni na shiga,sai na gawa anni kai baka shiga ba" kai.ya kada yana sake mata murmushi,ya kashe mata idonsa daya
"Noo princess uwaisha....muje" da haka suka ci gaba da takawa.
Tun daga varender da dakin yake suka dinga jiyo ihu,haka suka dinga takawa har zuwa bakin dakin,wasu daga cikin yaranshi da 'yan uwa ne tsaitsaye bakin qofar dakin jugum jugum,duk wanda ka kalla alamun tashin hankali ya bayyana qarara a fuskarshi,hango khalipha ya sanya sukayo wajenshi suna mishi sannu da zuwa,amsawa yayi yana zare glass din fuskarsa gami da kallon qofar dakin da ihun ke fitowa,zame hannun aysha yayi daha cikin nashi yadan sunkuya saitin kunneta
"Ki tsaya anan yanzu zan fito" kai ta gyada jikinta a sanyaye itama,bisa dukkan alamu mai mara lafiyan ne ke wannan ihun da qarajin.
Tura qofar dakin yayi bakinsa dauke da sallama,duk da ihun da kawu idris yake kwararawa bazai bari aji sallamar ba,ibrahim ne yake riqe dashi,matarsa tana gefe tana zubda qwalla,tsayawa yayi khalipha yayi yana dubanshi
"Ibrahim nace maka ka kwaramin ruwa,cikina...wuta ce,wutace take ci ajikina,baka ganta ba,nace baka ganta ba,jikina zafi yake min ibrahim jikina"
"Sakeshi" khalipha ya fada yana duban kawu idriss din,sakinsa ibrahim yayi yana share gumi da qwalla,addu'a ya soma yi yana tofa masa a jikinsa, hankali zafin da yakeji ya ragu sosai,ihun da yake ya tsaya sai qananun surutai
"Na gode khalipha,na gode" ya dinga maimaitawa,kana ji kasan sambatu yake
"Na gode khalipha ka yafemin naci dukiyarku,na cinye dukiyarku,nina kasheshi,nina kashesheki" gabansa ne yayi mummunan faduwar,sai ya zuba mishi idanu,a hankali ya bude bakinsa
"Kai ka kashe wa?"
"Babanku sa'idu,nine dasu hamza suka qi saina kasheshi ni kadai,saboda inason ayshatu inason na aureta" wani irin tuquqi yaji qirjinsa yanayi,take idanunshi suka sauya kala,sannu sannu ya dinga ja baya yana kallonshi,ya yunquro zai cafko khaliphan yana cewa
"ka tsaya karka tafi,tofamin addu'a tofamin,zafin da nakeji ya dawo....ka tsaya mana" juyawa yayi ya fice idanunsa jajur,tashin hankalin daya ji ba kadan bane a sannan,mutuwar babanshi da hajar ta dawo masa sabuwa fil,cikin wani irin zafin nama ya ja hannun aysha ba tare daya waiwaya ya dubi kowa ba suka fice yana jiyo ihun idriss.
Tunda suka sauka a gidansu na cyprus ta kasa gane kanshi,duk wani abu tayi amma ba canji,data gaji kawai saita zauna ta sanya mishi kuka,a rude a janyota jikinsa yana tambayarta
"Meya faru uwaisha?,nine ko?,am sorry kiyi haquri,uwaisha.....shi ya kashemin abba na,me yayi masa haka arayuwa bayan tarin alkhairai daya musu?"sosai maganar ta daketa,saita daga kai tana dubanshi,yau taga ahalin da suka fi nata zalunci,taga ahalin da suka dara nata ahalin mugunta da watsi da zumuncin Allah,maganar ta kidimata,saidai ya zama dole ta rage razanar data yi saboda ta maidashi cikin mode dinshi
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un,gaskiya ne ya aikata babban xalunci akan ran da bata jiba bata gani ba,abba ajalinsa ya riya yazo,koda kawu idris ko babu shi tilas saiya tafi,tsakaninka da abba yanzu haka addu'a ce,haqiqa Allah baya barin wanda ya kashe wata rai ba tare data cancanci hakan ba,ka zuba ido kaga shima zai tabbata ne a duniya?,komai daren dadewa sai ya tafi inda abban yaje" da kalamai masu dadi tayi amfani ta samu kanshi,ya dinga sauke ajiyar zuciya ajejjere,tsananin fushi bacin rai da rudanin daya shiga suna sauka.
Gab da zasu kwanta wayarshi ta dauki kida,ya duba sai yaga haidar ne
"Ya akayi haidar,ina fata kowa lafiya"
"Eh mukam lpy lau,kawu idris ne ya wuce,baku jima da barin asibitin ba yarasu"idanunsa khalipha ya lumshe,maganganun aysha na dawo masa fes aka,kamar a sannan take gaya mishi,sautin haidar shi ya katse masa tunaninsa
" yaya mutanen nan Allah ne kadai yasan zunubin da suka aikata bayan dukiyarmu da suka cinye,kasan gaba daya fuskar kawu idris tayi baqi?,har ya mutu bai daina kiran cikinsa wuta naci a ciki ba?"
"Allah ya riga daya fada ya kuma gargademu cewa,duk wanda yake cin dukiyar maraya da zalunci haqiqa wuta yake ci a cikinsa,da sannu kuma xai shiga wutar sa'ira,zai iya yiwuwa Allah ya nuna ishararsa ne saboda sauran abokan barnarsa su kawu hamza dake raye"
"Sun girgiza ya khalipha.....kafin a dauki gawar kawu idriss saida suka warwarewa anni komai suna kuka wiwi da neman gafararta saboda yadda sukaga gawar kawu idris ta koma,ya tabbata su suka jefamu a halin talauci a baya,su suka tattare komai namu suka cinye"
"Ai ubangiji baya bacci,kuma gashinan sun gani zahiri,Allah yasa mu dace,yasa muyi kyakkyawan qarshe"
"Amin ya Allah yaya" daga haka sukayi sallama ya kashe wayar yana ajiyar zuciya,gaskiya ne Allah baya zalunci daidai da qwayar xarra,ko yaya ka zalunci musulmi ko kaci masa haqqinsa koda qwayar gero ce bakai ba aljanna saika biyashi,koda iya ladar data rage maka kenan ka shiga aljanna ba ruwan ubangiji saika biya haqqin wani daka ci.
A haka aysha ta shigo dauke da coffe sai tururi yake
"Ya khalipha....."
"Shshshshs...." Ya fada yana katseta
"Daga yau banason wannan sunan,yanzu fa haidar ya gama cemin yaya kema ki fada,meye banbancin kenan?" Ya fada yana dage girarshi yana kallonta,wani sassanyar murmushi daya ratsa zuciyarshi ta saki tana aje coffen a gefanshi,cikin zuciyarta tana jin dadin yadda ya sake,gadon ta hau sosai ta kama hannayensa gaba daya cikin lallausan tafin hannunta tana murmushi
"Ka zabi dukkan sunan da kakeso ni kuma zan kiraka dashi ko a gaban waye" murmushin shima ya saki,yana jin dadin yadda take fifitashi fiye da kowa,take fifitashi fiye da duk abinda takeso a duniya,take zabar farincikinsa saman nata,kamo fuskarta yayi ya sumbaci goshinta cikin alfahari da ita
"Na baki zabi matata,na amince miki ki zaba min dukkan sunan daya dace da ra'ayinki" murmushi ta sakar masa tana matsa 'yan yatsunshi
"Bazan iyakance wani suna qwaya daya da zan kiraka dashi ba,ka cancanci dukkan wani suna dake nuna qauna da soyayya your royal highness" idanu ya zaro yana jin dadj,ba shakka ta cika mace ta gari macen qwarai,wanda ma'aiki S A W yace idan ka kalleta zata faranta maka,idan ka umarceta zata yi maka biyayya,idan kayi rantsuwa zata kubutar dakai,idan kayi tafiya ko baka nan zata kare maka kanta da dukiyarta,shikam me zaya ce da ubangijinsa banda godiya?.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Da sallama ya shigo dakin nata bayan ya bar mahaifiyarshi da qannenshi a babban falon gidan,a hankali ta sauke ajiyar zuciya bayan dogon tunanin data gama yi kana ta dago tana dubanshi,gaba daya daddy kafin rasuwarshi ya gama yi mata dabaibayi da kalamanshi kamar yana sane da abinda take shiryawa na barin gidan hamid,ya gaya mata cewa muddin babu ce zata sanyata barin aurenta indai shi ya haifeta bai yafe mata ba,matuqar mijinta na bata kulawa iyakar qarfinsa to yana umartarta ta zauna gidanta,saidai idan yazo da wata cutarwa da shafeta ko addininta,to a yanzun hamid din ya sauya,ba rashin ci babu rashin sha,duk da cewa duk wani jin dadi dada yake dashi yanzu babu,dalili kenan daya sanya yawan yawan halayensa sauyawa,saidai ita sam ya fita a kanta,kallonshi kawai take.
Da tausayinta kan fuskarshi ya zauna hannun kujerar da take kai,yanzun ya gama tsawatarwa qannenshi kan rashin kunyar da suke mata
"Kiyi haquri asma'u,na tsawatar musu kuma in sha Allahu daga yanzu hakan ba zata sake faruwa ba,kimin addu'a Allah ya sake buda min ba don halina ba,in daukeki na sauya miki gida" kallonshi kawai tayi ta miqe ta shige bedroom dinta,yayin da shima ya bita da kallo,gaba daya ta sauya tun daga mutuwar daddyn tayi wani mugun sanyi,sai ya miqe ya bita,tana zaune gefan gado,kallonshi take da mamaki don ta manta yaushe rabon da tayi masa irin hakan ya biyota
"Ki daure ki yafemin asma'u,nasan cewa harda haqqinki na takureki da nakeyi da rashin wadataki bayan ina da damar haka shi yasa Allah ya jarabceni,duk da cewa ni maison kudi ne amma takaicin yadda kika dinga tatsata,quru quru ya bayyana ba don Allah kikesona ba,hakanan ba zaki aureni ba idan ban miki barin kudi ba yasa nima ma takuraki sanda mukayi auren,ashe Allah ba ruwanshi,na sauke haqqinki kawai dake kaina shine mafitata,ki yafemin asma'u don Allah" kwanciya tayi kawai ta juya mishi baya,a zuciyarta tanason tayi yaqi da khalipha ta karbi hamid,saidai hakan na nufin su zauna a qaramar rayuwa?,to idan ma bata amshi hamid ba ya za'ayi ya samu khalipha?,mutumin data tabbatar daya tsallake baya qasar,ko baya ga haka ita kanta idan ta zauna tana tuna abubuwan da tayi mishi a rayuwa saita dinga jin nauyin abubuwan da mamakin yadda akayi ma tayi wani abun,a lokacin duniyar nayi da ita,duka a ture wannan ya zatayi da nasihar daddy,da wannan tunanin zuciyarta ta yanke mata tilas zama da hamid ya kamata,saidai tasan yadda zata lallashi kanta ta amshi tayinsa ta sabunta sonshi cikin zuciyarta,don idan ma tace batason hamid din ita kanta tasan ta yiwa kanta qarya.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
"Ya khalipha pls mana,idan kasan ranka zaya baci ba zaka saki ranka ba ka tsaya ni na shiga,sai na gawa anni kai baka shiga ba" kai.ya kada yana sake mata murmushi,ya kashe mata idonsa daya
"Noo princess uwaisha....muje" da haka suka ci gaba da takawa.
Tun daga varender da dakin yake suka dinga jiyo ihu,haka suka dinga takawa har zuwa bakin dakin,wasu daga cikin yaranshi da 'yan uwa ne tsaitsaye bakin qofar dakin jugum jugum,duk wanda ka kalla alamun tashin hankali ya bayyana qarara a fuskarshi,hango khalipha ya sanya sukayo wajenshi suna mishi sannu da zuwa,amsawa yayi yana zare glass din fuskarsa gami da kallon qofar dakin da ihun ke fitowa,zame hannun aysha yayi daha cikin nashi yadan sunkuya saitin kunneta
"Ki tsaya anan yanzu zan fito" kai ta gyada jikinta a sanyaye itama,bisa dukkan alamu mai mara lafiyan ne ke wannan ihun da qarajin.
Tura qofar dakin yayi bakinsa dauke da sallama,duk da ihun da kawu idris yake kwararawa bazai bari aji sallamar ba,ibrahim ne yake riqe dashi,matarsa tana gefe tana zubda qwalla,tsayawa yayi khalipha yayi yana dubanshi
"Ibrahim nace maka ka kwaramin ruwa,cikina...wuta ce,wutace take ci ajikina,baka ganta ba,nace baka ganta ba,jikina zafi yake min ibrahim jikina"
"Sakeshi" khalipha ya fada yana duban kawu idriss din,sakinsa ibrahim yayi yana share gumi da qwalla,addu'a ya soma yi yana tofa masa a jikinsa, hankali zafin da yakeji ya ragu sosai,ihun da yake ya tsaya sai qananun surutai
"Na gode khalipha,na gode" ya dinga maimaitawa,kana ji kasan sambatu yake
"Na gode khalipha ka yafemin naci dukiyarku,na cinye dukiyarku,nina kasheshi,nina kashesheki" gabansa ne yayi mummunan faduwar,sai ya zuba mishi idanu,a hankali ya bude bakinsa
"Kai ka kashe wa?"
"Babanku sa'idu,nine dasu hamza suka qi saina kasheshi ni kadai,saboda inason ayshatu inason na aureta" wani irin tuquqi yaji qirjinsa yanayi,take idanunshi suka sauya kala,sannu sannu ya dinga ja baya yana kallonshi,ya yunquro zai cafko khaliphan yana cewa
"ka tsaya karka tafi,tofamin addu'a tofamin,zafin da nakeji ya dawo....ka tsaya mana" juyawa yayi ya fice idanunsa jajur,tashin hankalin daya ji ba kadan bane a sannan,mutuwar babanshi da hajar ta dawo masa sabuwa fil,cikin wani irin zafin nama ya ja hannun aysha ba tare daya waiwaya ya dubi kowa ba suka fice yana jiyo ihun idriss.
Tunda suka sauka a gidansu na cyprus ta kasa gane kanshi,duk wani abu tayi amma ba canji,data gaji kawai saita zauna ta sanya mishi kuka,a rude a janyota jikinsa yana tambayarta
"Meya faru uwaisha?,nine ko?,am sorry kiyi haquri,uwaisha.....shi ya kashemin abba na,me yayi masa haka arayuwa bayan tarin alkhairai daya musu?"sosai maganar ta daketa,saita daga kai tana dubanshi,yau taga ahalin da suka fi nata zalunci,taga ahalin da suka dara nata ahalin mugunta da watsi da zumuncin Allah,maganar ta kidimata,saidai ya zama dole ta rage razanar data yi saboda ta maidashi cikin mode dinshi
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un,gaskiya ne ya aikata babban xalunci akan ran da bata jiba bata gani ba,abba ajalinsa ya riya yazo,koda kawu idris ko babu shi tilas saiya tafi,tsakaninka da abba yanzu haka addu'a ce,haqiqa Allah baya barin wanda ya kashe wata rai ba tare data cancanci hakan ba,ka zuba ido kaga shima zai tabbata ne a duniya?,komai daren dadewa sai ya tafi inda abban yaje" da kalamai masu dadi tayi amfani ta samu kanshi,ya dinga sauke ajiyar zuciya ajejjere,tsananin fushi bacin rai da rudanin daya shiga suna sauka.
Gab da zasu kwanta wayarshi ta dauki kida,ya duba sai yaga haidar ne
"Ya akayi haidar,ina fata kowa lafiya"
"Eh mukam lpy lau,kawu idris ne ya wuce,baku jima da barin asibitin ba yarasu"idanunsa khalipha ya lumshe,maganganun aysha na dawo masa fes aka,kamar a sannan take gaya mishi,sautin haidar shi ya katse masa tunaninsa
" yaya mutanen nan Allah ne kadai yasan zunubin da suka aikata bayan dukiyarmu da suka cinye,kasan gaba daya fuskar kawu idris tayi baqi?,har ya mutu bai daina kiran cikinsa wuta naci a ciki ba?"
"Allah ya riga daya fada ya kuma gargademu cewa,duk wanda yake cin dukiyar maraya da zalunci haqiqa wuta yake ci a cikinsa,da sannu kuma xai shiga wutar sa'ira,zai iya yiwuwa Allah ya nuna ishararsa ne saboda sauran abokan barnarsa su kawu hamza dake raye"
"Sun girgiza ya khalipha.....kafin a dauki gawar kawu idriss saida suka warwarewa anni komai suna kuka wiwi da neman gafararta saboda yadda sukaga gawar kawu idris ta koma,ya tabbata su suka jefamu a halin talauci a baya,su suka tattare komai namu suka cinye"
"Ai ubangiji baya bacci,kuma gashinan sun gani zahiri,Allah yasa mu dace,yasa muyi kyakkyawan qarshe"
"Amin ya Allah yaya" daga haka sukayi sallama ya kashe wayar yana ajiyar zuciya,gaskiya ne Allah baya zalunci daidai da qwayar xarra,ko yaya ka zalunci musulmi ko kaci masa haqqinsa koda qwayar gero ce bakai ba aljanna saika biyashi,koda iya ladar data rage maka kenan ka shiga aljanna ba ruwan ubangiji saika biya haqqin wani daka ci.
A haka aysha ta shigo dauke da coffe sai tururi yake
"Ya khalipha....."
"Shshshshs...." Ya fada yana katseta
"Daga yau banason wannan sunan,yanzu fa haidar ya gama cemin yaya kema ki fada,meye banbancin kenan?" Ya fada yana dage girarshi yana kallonta,wani sassanyar murmushi daya ratsa zuciyarshi ta saki tana aje coffen a gefanshi,cikin zuciyarta tana jin dadin yadda ya sake,gadon ta hau sosai ta kama hannayensa gaba daya cikin lallausan tafin hannunta tana murmushi
"Ka zabi dukkan sunan da kakeso ni kuma zan kiraka dashi ko a gaban waye" murmushin shima ya saki,yana jin dadin yadda take fifitashi fiye da kowa,take fifitashi fiye da duk abinda takeso a duniya,take zabar farincikinsa saman nata,kamo fuskarta yayi ya sumbaci goshinta cikin alfahari da ita
"Na baki zabi matata,na amince miki ki zaba min dukkan sunan daya dace da ra'ayinki" murmushi ta sakar masa tana matsa 'yan yatsunshi
"Bazan iyakance wani suna qwaya daya da zan kiraka dashi ba,ka cancanci dukkan wani suna dake nuna qauna da soyayya your royal highness" idanu ya zaro yana jin dadj,ba shakka ta cika mace ta gari macen qwarai,wanda ma'aiki S A W yace idan ka kalleta zata faranta maka,idan ka umarceta zata yi maka biyayya,idan kayi rantsuwa zata kubutar dakai,idan kayi tafiya ko baka nan zata kare maka kanta da dukiyarta,shikam me zaya ce da ubangijinsa banda godiya?.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Da sallama ya shigo dakin nata bayan ya bar mahaifiyarshi da qannenshi a babban falon gidan,a hankali ta sauke ajiyar zuciya bayan dogon tunanin data gama yi kana ta dago tana dubanshi,gaba daya daddy kafin rasuwarshi ya gama yi mata dabaibayi da kalamanshi kamar yana sane da abinda take shiryawa na barin gidan hamid,ya gaya mata cewa muddin babu ce zata sanyata barin aurenta indai shi ya haifeta bai yafe mata ba,matuqar mijinta na bata kulawa iyakar qarfinsa to yana umartarta ta zauna gidanta,saidai idan yazo da wata cutarwa da shafeta ko addininta,to a yanzun hamid din ya sauya,ba rashin ci babu rashin sha,duk da cewa duk wani jin dadi dada yake dashi yanzu babu,dalili kenan daya sanya yawan yawan halayensa sauyawa,saidai ita sam ya fita a kanta,kallonshi kawai take.
Da tausayinta kan fuskarshi ya zauna hannun kujerar da take kai,yanzun ya gama tsawatarwa qannenshi kan rashin kunyar da suke mata
"Kiyi haquri asma'u,na tsawatar musu kuma in sha Allahu daga yanzu hakan ba zata sake faruwa ba,kimin addu'a Allah ya sake buda min ba don halina ba,in daukeki na sauya miki gida" kallonshi kawai tayi ta miqe ta shige bedroom dinta,yayin da shima ya bita da kallo,gaba daya ta sauya tun daga mutuwar daddyn tayi wani mugun sanyi,sai ya miqe ya bita,tana zaune gefan gado,kallonshi take da mamaki don ta manta yaushe rabon da tayi masa irin hakan ya biyota
"Ki daure ki yafemin asma'u,nasan cewa harda haqqinki na takureki da nakeyi da rashin wadataki bayan ina da damar haka shi yasa Allah ya jarabceni,duk da cewa ni maison kudi ne amma takaicin yadda kika dinga tatsata,quru quru ya bayyana ba don Allah kikesona ba,hakanan ba zaki aureni ba idan ban miki barin kudi ba yasa nima ma takuraki sanda mukayi auren,ashe Allah ba ruwanshi,na sauke haqqinki kawai dake kaina shine mafitata,ki yafemin asma'u don Allah" kwanciya tayi kawai ta juya mishi baya,a zuciyarta tanason tayi yaqi da khalipha ta karbi hamid,saidai hakan na nufin su zauna a qaramar rayuwa?,to idan ma bata amshi hamid ba ya za'ayi ya samu khalipha?,mutumin data tabbatar daya tsallake baya qasar,ko baya ga haka ita kanta idan ta zauna tana tuna abubuwan da tayi mishi a rayuwa saita dinga jin nauyin abubuwan da mamakin yadda akayi ma tayi wani abun,a lokacin duniyar nayi da ita,duka a ture wannan ya zatayi da nasihar daddy,da wannan tunanin zuciyarta ta yanke mata tilas zama da hamid ya kamata,saidai tasan yadda zata lallashi kanta ta amshi tayinsa ta sabunta sonshi cikin zuciyarta,don idan ma tace batason hamid din ita kanta tasan ta yiwa kanta qarya.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶