Sashe 9
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Mayafinta ta rataya tare da maqala 'yar jakarta bayan tasha ruwa ta wanke hannunta tana duban innar
"Inna zan qarasa gidansu inna kulu" wani kallonta watsa mata sannan tace
"Zaki dai je ganin uwarki ko?,uwar da bata damu da rayuwarki ba" Kanta ta kada can qasar zuciyarta tana jin babu dadi,komai lalacewar uwa uwace,sam bata jin dadin kalaman dake fitowa daga bakin inna kulu ko yaushe akan mamanta,batasan wanne irin rashin jituwa bane haka a tsakaninsu tsahon shekaru tun tasowarta amma har yau bata sauya zani ba
"Bansan ma sunzo ba inna,zanje na duba jikin kawun ne" baki innar ta tabe tana ci gaba da abinda take ba tare data tanka mata ba,har ta gaji da tsaiwa haka nan taja jikinta a hankali ta fice daga dakin ba tare data sake cewa komai ba itama.
Wannan karon tsakar gidan nasu babu jama'a sosai sai yara jefi jefi,kowacce tayi sashinta masu wankan da ba'a yiba tun safe nayi,da masu shara da wanke wanke,ba zasu sake hallaraba wajen ba kuma sai bayan sallar la'asar,hakan shinya bata damar ficewa hankali kwance daga gidan ba tare data sake jin wani abu da bazaiwa kunnuwanta da zuciyarta dadi ba,tun tasowarta haka taga gidan nasu,wannan zaman dai sai an yishi a kulli yaumin.
Da gudu yaron ya biyo tayarsa da yake garawa wadda bata tsaya ko ina ba sai gaban aisha,dafe tayar tayi ta daga kanta tana duban yaron,kallo daya ta masa ta tabbatar jininsu ne,don yana kama da umminta sosai,kana dubanshi kasan daga duk inda ya fito ba waje bane na wahala,sanye yake da wando da t.shirt wadda ta dace da kayan nashi,duk da sun debi qura da jar qasa kadan sanadiyyar wasan da yake faman yi babu ji babu gani amma kana kallonsu kasan masu tsada ne,kallonta yayi sai ya dauke kai yaci gaba da gara tayarsa alamar bai santa ba,ita dinma bata sanshi ba,amma bata tantama shine yaron data ji labarin ummin nata ta haifa bayan shekararta daya da komawa gidan daddy zuwanta na farko ziyara qauyen
"Laaaa,anty indo" taji an ambata qasa qasa,waiwayowa tayi tana duban mai kiran sunan nata,wanda tasan masu kiran nata da wannan sunan wasu kebantattun mutane ne.
Basma ce wadda a qa'idance zata kira da qanwarta,saidai a zahirance kai ba zaka ce qanwar tata bace musamman a shekarun baya da suka shude,gwara a yanzun da yanayin rayuwarta data basman ta saje,mutane da dama wadanda basu sansu ba kan sheqe da dariya idan ta nunata tace qanwarta ce saboda banbancin yanayi na rayuwa da tazara mai tarin yawa a tsakaninsu,saidai a yanzu da rayuwa ta soma zuwa mata da wasu daga cikin sauye sauye zaka gasgata cewa qanwarta ce karon farko saboda yanayi na daidaikun kamanni data dan debo nata.
Fuskar yarinyar qunshe da murmushi kamar yadda fuskar aysha ki cike da fara'a ta qaraso gabanta ta kama hannayenta
"Anty indo dama kina nan?,yaushe rabon dana ganki anty?,tunda kika koma inda kike sai a dade ba'a ganki ba me yasa?"
"Inda na koma din ba cikin garin nan bane basma,kuma makaranta nake zuwa bako yaushe nake da lokacin zuwa ba....yaushe kuka zo?"tayi dukka maganar tata cikin fara'a
"yau kwananmu uku,gobe ko jibi abbu zaizo ya daukemu" cike da zaquwa tace
"Harda ummi?" Kai basma ta kada
"Harda ita,tana cikin gida ma,shigo muje ki ganta"ta fada tana dan jan hannun ayshan, faduwar da gabanta yayi shi ya tilasta mata lumshe idanunta kafin daga bisani ta budesu,Allah ya sani tana sonta,tana son ganinta,tana son ta rabeta,amma bata san me yasa duk bata da wannan damar ba,batasan me ya haifar da wannan babban gibin da baraka dake tsakanin dangantakarta data mahaifiyarta ba da kuma gidansu mahaifinta,a hankali ta bude idanun ta dafe hannun basma dake cikin nata
"kije zan shigo,kinsan me zai biyo baya idan ta ganmuntare aiko?" Fuskarta a bace ranta a hade ta kada kai
"Shikenan,amma don Allah anty karki koma ki shigo din"
"Yanzun nan kuwa kada ki damu,zan leqa gidan mero ne".
A haka suka rabu ta shiga layin gidan meron,tayi hakanne kuwa don tana jiyewa basma hukuncin da zai biyo baya idan ummin ta gansu tare,ba qaramin aiki bane a wajentan ta lakada mata dukan da zata ji a jikinta,tunda tun kafin takai hakan take dakuwa wajenta matuqar zata gansu tare,ko zata ga ta bata wani abu,wani lokaci idan ta tsawaita tunani kan wadan nan cakudaddun al'umaran takanji kanta tamkar zaya tsage,bata da amsa bata kuma da mai bata amsar,sai tarin tsana da tsangwama da take fuskanta aduk sanda tayi yunqurin tambayar wani makusancin lamarin kan meya faru a baya?,meye sanadi?,mai ya haifar da haka,wasu sukanyi gaba su barta a nasu tunanin tasan komai,tsabar rainin wayo ko wahala ce ta soma taba qwaqwalwarta,da wannan tunanin na tsohon shafin rayuwarta ta qarasa gidan qawarta ta quruciya wato mero.
Cikin farinciki suka rungume juna ita da mero,da qyar suka samu wajen zama kowa na zumudin ganin dan uwansa,abota ce da ba zasu taba mantawa da ita ba,abota ce data yiwa aysha rana,abota irin wadda ta kasa samunta daga yan uwanta a wancan lokacin
"Indo....ashe komai na rayuwa mai wucewa ne...kin ganki ko indo kin zama matar birni,don ma har yau babu qibar da kika qara" mero ta fada tana kama habarta,qaramar dariya aysha ta saki tana kada kai
"Mero har yau halayyarki ba zata sauya ba kenan....komai na rayuwa mai wucewa ne mero,amma banda abu guda,wanda bana tsammanin zai wuce" ta qarashe maganar fara'ar fuskarta na raguwa,da alamu maganar da take cikin zuciyarta ta taba ranta sosai,hannu meron ta aza bisa kafadar aysha tana cewa
"Ba abinda ke tabbata a duniya sai ikon Allah indo,kici gaba da sakawa ranki salama,kici gaba da sawa ranki cewa watan watarana zai zama labari tamkar ba'a yiba,umminki mutum ce kaman kowa,zuciyarta na hannun ubangiji,kuma yana da ikon sata ta sauya aduk sanda yaga dama koda bata so yin hakan ba" cike da gamsuwa take gyada kanta gami da sanya yatsunta ta dauke qwallar data sauko mata,zuciyarta na samun nutsuwa da kalaman mero
"Haka ne,na gode qwarai Allah ya qara zumunci"
"Ba wannan tsakaninmu indon baffale,yanzu mutuminki zan dafa miki ko kuwa?,yau ban dora sanwa ba a gidan nan duka yaran suna gidan gwaggwan habu shi yasa ban dafa komai ba" dariya indo ta saki saboda tuno wani abu da tayi
"Hoooo,meron habuwalle,bada kanki a sare...waima yana ina" dariya mero ta saki
"Zaku taba diramar taku ne?,yau tun safe ya tafi hungu ina jin kuma bazai shigoba sai gefin magariba,amma ai tunda kina nan zaku hadu ne" ta fada tana yunqurin tashi
"Kinga yi zamanki karki wahal da kanki,ban jima da cin abinci ba na fito" komawa tayi ta zauna tana dubanta
"Wanne abinci ko muna abinci,sun baki wannan busashshiyar shinkafar tasu da ke kika jima da yin bankwana da cin irinta,ni bansan meke damun jama'ar gidanku ba,ga arziqin abinci gar abinci amma su basu raba kansu da cimar da kowa cikin karkarar nan ke fatan bankwana da ita ba" dariya aysha tayi kawai tana jin mitar mero,itadai indai aka taba indo tofa za'aji kansu da shi koda waye ma,zata iya cewa su biyu ita da aliya bata taba samun soyayya kamar tasu ba,tabbas idan wani ya qika wani zai soka haka rayuwa take.
Ledar data zabo mata atamfofi cikin nata ta miqa mata,ta daga tana ta murna da godiya,duk da cewa bata rasa komai gidan mijinta ba,habu mutum ne mai zuciyar kula da iyali wanda irinsa daidaiku ne cikin karkara a halin yanzu.
Sun dan jima suna hira sannan sukayi sallama da alqawarin gobe idan bata samu taje gidan gwaggwo asabe zata dawo susha hirarsu.
Tamkar mara gaskiya haka ta dinga taka dogon soron gidan kakannin nata,ba komai ya haifar da hakan ba illa tunani da zaton mahaifiyarta a halin yanzu na cikin gidan,tsakar gidan fetal yake babu kowa,bata ji motsi ko hayaniyar kowa ba,hakan shi ya sake bata qwarin gwiwar kutsa kai cikin gidan bakinta dauke da sallama,inna kulu dake qasan rumfar da suke girki ce zaune gaban murhu tana ta aza wuta bisa dukkan alamu wani abu mai buqatar wuta da yawa take dafawa,waiwayowa tayi tana amsa sallamar kafin daga bisani ta dan washe fuskarta tana fadin
"Indo....yaushe kika shigo garin?"
"Wallahi inna dazu dazun nan"
"To maraba,qarasa daki nima gani nan tasowa"
"Toh" ta amsa idanunta na satar kallon kebantaccen dakin da tasan cewa mahaifiyarta na sauka ciki duk sanda tazo garin,dakin a bude yake saidai an dan karashi hakan yasa ba zata iya gane da mutum ko babu ba da haka ta sanya kanta cikin dakin inna kulu dake falle daya dauke malale da leda da labulaye gami da lailayayyen gadon qarfe da doguwar kujera qwaya daya wanda dukkan wannan gyaran aikin ummin nata ne.
"Inna zan qarasa gidansu inna kulu" wani kallonta watsa mata sannan tace
"Zaki dai je ganin uwarki ko?,uwar da bata damu da rayuwarki ba" Kanta ta kada can qasar zuciyarta tana jin babu dadi,komai lalacewar uwa uwace,sam bata jin dadin kalaman dake fitowa daga bakin inna kulu ko yaushe akan mamanta,batasan wanne irin rashin jituwa bane haka a tsakaninsu tsahon shekaru tun tasowarta amma har yau bata sauya zani ba
"Bansan ma sunzo ba inna,zanje na duba jikin kawun ne" baki innar ta tabe tana ci gaba da abinda take ba tare data tanka mata ba,har ta gaji da tsaiwa haka nan taja jikinta a hankali ta fice daga dakin ba tare data sake cewa komai ba itama.
Wannan karon tsakar gidan nasu babu jama'a sosai sai yara jefi jefi,kowacce tayi sashinta masu wankan da ba'a yiba tun safe nayi,da masu shara da wanke wanke,ba zasu sake hallaraba wajen ba kuma sai bayan sallar la'asar,hakan shinya bata damar ficewa hankali kwance daga gidan ba tare data sake jin wani abu da bazaiwa kunnuwanta da zuciyarta dadi ba,tun tasowarta haka taga gidan nasu,wannan zaman dai sai an yishi a kulli yaumin.
Da gudu yaron ya biyo tayarsa da yake garawa wadda bata tsaya ko ina ba sai gaban aisha,dafe tayar tayi ta daga kanta tana duban yaron,kallo daya ta masa ta tabbatar jininsu ne,don yana kama da umminta sosai,kana dubanshi kasan daga duk inda ya fito ba waje bane na wahala,sanye yake da wando da t.shirt wadda ta dace da kayan nashi,duk da sun debi qura da jar qasa kadan sanadiyyar wasan da yake faman yi babu ji babu gani amma kana kallonsu kasan masu tsada ne,kallonta yayi sai ya dauke kai yaci gaba da gara tayarsa alamar bai santa ba,ita dinma bata sanshi ba,amma bata tantama shine yaron data ji labarin ummin nata ta haifa bayan shekararta daya da komawa gidan daddy zuwanta na farko ziyara qauyen
"Laaaa,anty indo" taji an ambata qasa qasa,waiwayowa tayi tana duban mai kiran sunan nata,wanda tasan masu kiran nata da wannan sunan wasu kebantattun mutane ne.
Basma ce wadda a qa'idance zata kira da qanwarta,saidai a zahirance kai ba zaka ce qanwar tata bace musamman a shekarun baya da suka shude,gwara a yanzun da yanayin rayuwarta data basman ta saje,mutane da dama wadanda basu sansu ba kan sheqe da dariya idan ta nunata tace qanwarta ce saboda banbancin yanayi na rayuwa da tazara mai tarin yawa a tsakaninsu,saidai a yanzu da rayuwa ta soma zuwa mata da wasu daga cikin sauye sauye zaka gasgata cewa qanwarta ce karon farko saboda yanayi na daidaikun kamanni data dan debo nata.
Fuskar yarinyar qunshe da murmushi kamar yadda fuskar aysha ki cike da fara'a ta qaraso gabanta ta kama hannayenta
"Anty indo dama kina nan?,yaushe rabon dana ganki anty?,tunda kika koma inda kike sai a dade ba'a ganki ba me yasa?"
"Inda na koma din ba cikin garin nan bane basma,kuma makaranta nake zuwa bako yaushe nake da lokacin zuwa ba....yaushe kuka zo?"tayi dukka maganar tata cikin fara'a
"yau kwananmu uku,gobe ko jibi abbu zaizo ya daukemu" cike da zaquwa tace
"Harda ummi?" Kai basma ta kada
"Harda ita,tana cikin gida ma,shigo muje ki ganta"ta fada tana dan jan hannun ayshan, faduwar da gabanta yayi shi ya tilasta mata lumshe idanunta kafin daga bisani ta budesu,Allah ya sani tana sonta,tana son ganinta,tana son ta rabeta,amma bata san me yasa duk bata da wannan damar ba,batasan me ya haifar da wannan babban gibin da baraka dake tsakanin dangantakarta data mahaifiyarta ba da kuma gidansu mahaifinta,a hankali ta bude idanun ta dafe hannun basma dake cikin nata
"kije zan shigo,kinsan me zai biyo baya idan ta ganmuntare aiko?" Fuskarta a bace ranta a hade ta kada kai
"Shikenan,amma don Allah anty karki koma ki shigo din"
"Yanzun nan kuwa kada ki damu,zan leqa gidan mero ne".
A haka suka rabu ta shiga layin gidan meron,tayi hakanne kuwa don tana jiyewa basma hukuncin da zai biyo baya idan ummin ta gansu tare,ba qaramin aiki bane a wajentan ta lakada mata dukan da zata ji a jikinta,tunda tun kafin takai hakan take dakuwa wajenta matuqar zata gansu tare,ko zata ga ta bata wani abu,wani lokaci idan ta tsawaita tunani kan wadan nan cakudaddun al'umaran takanji kanta tamkar zaya tsage,bata da amsa bata kuma da mai bata amsar,sai tarin tsana da tsangwama da take fuskanta aduk sanda tayi yunqurin tambayar wani makusancin lamarin kan meya faru a baya?,meye sanadi?,mai ya haifar da haka,wasu sukanyi gaba su barta a nasu tunanin tasan komai,tsabar rainin wayo ko wahala ce ta soma taba qwaqwalwarta,da wannan tunanin na tsohon shafin rayuwarta ta qarasa gidan qawarta ta quruciya wato mero.
Cikin farinciki suka rungume juna ita da mero,da qyar suka samu wajen zama kowa na zumudin ganin dan uwansa,abota ce da ba zasu taba mantawa da ita ba,abota ce data yiwa aysha rana,abota irin wadda ta kasa samunta daga yan uwanta a wancan lokacin
"Indo....ashe komai na rayuwa mai wucewa ne...kin ganki ko indo kin zama matar birni,don ma har yau babu qibar da kika qara" mero ta fada tana kama habarta,qaramar dariya aysha ta saki tana kada kai
"Mero har yau halayyarki ba zata sauya ba kenan....komai na rayuwa mai wucewa ne mero,amma banda abu guda,wanda bana tsammanin zai wuce" ta qarashe maganar fara'ar fuskarta na raguwa,da alamu maganar da take cikin zuciyarta ta taba ranta sosai,hannu meron ta aza bisa kafadar aysha tana cewa
"Ba abinda ke tabbata a duniya sai ikon Allah indo,kici gaba da sakawa ranki salama,kici gaba da sawa ranki cewa watan watarana zai zama labari tamkar ba'a yiba,umminki mutum ce kaman kowa,zuciyarta na hannun ubangiji,kuma yana da ikon sata ta sauya aduk sanda yaga dama koda bata so yin hakan ba" cike da gamsuwa take gyada kanta gami da sanya yatsunta ta dauke qwallar data sauko mata,zuciyarta na samun nutsuwa da kalaman mero
"Haka ne,na gode qwarai Allah ya qara zumunci"
"Ba wannan tsakaninmu indon baffale,yanzu mutuminki zan dafa miki ko kuwa?,yau ban dora sanwa ba a gidan nan duka yaran suna gidan gwaggwan habu shi yasa ban dafa komai ba" dariya indo ta saki saboda tuno wani abu da tayi
"Hoooo,meron habuwalle,bada kanki a sare...waima yana ina" dariya mero ta saki
"Zaku taba diramar taku ne?,yau tun safe ya tafi hungu ina jin kuma bazai shigoba sai gefin magariba,amma ai tunda kina nan zaku hadu ne" ta fada tana yunqurin tashi
"Kinga yi zamanki karki wahal da kanki,ban jima da cin abinci ba na fito" komawa tayi ta zauna tana dubanta
"Wanne abinci ko muna abinci,sun baki wannan busashshiyar shinkafar tasu da ke kika jima da yin bankwana da cin irinta,ni bansan meke damun jama'ar gidanku ba,ga arziqin abinci gar abinci amma su basu raba kansu da cimar da kowa cikin karkarar nan ke fatan bankwana da ita ba" dariya aysha tayi kawai tana jin mitar mero,itadai indai aka taba indo tofa za'aji kansu da shi koda waye ma,zata iya cewa su biyu ita da aliya bata taba samun soyayya kamar tasu ba,tabbas idan wani ya qika wani zai soka haka rayuwa take.
Ledar data zabo mata atamfofi cikin nata ta miqa mata,ta daga tana ta murna da godiya,duk da cewa bata rasa komai gidan mijinta ba,habu mutum ne mai zuciyar kula da iyali wanda irinsa daidaiku ne cikin karkara a halin yanzu.
Sun dan jima suna hira sannan sukayi sallama da alqawarin gobe idan bata samu taje gidan gwaggwo asabe zata dawo susha hirarsu.
Tamkar mara gaskiya haka ta dinga taka dogon soron gidan kakannin nata,ba komai ya haifar da hakan ba illa tunani da zaton mahaifiyarta a halin yanzu na cikin gidan,tsakar gidan fetal yake babu kowa,bata ji motsi ko hayaniyar kowa ba,hakan shi ya sake bata qwarin gwiwar kutsa kai cikin gidan bakinta dauke da sallama,inna kulu dake qasan rumfar da suke girki ce zaune gaban murhu tana ta aza wuta bisa dukkan alamu wani abu mai buqatar wuta da yawa take dafawa,waiwayowa tayi tana amsa sallamar kafin daga bisani ta dan washe fuskarta tana fadin
"Indo....yaushe kika shigo garin?"
"Wallahi inna dazu dazun nan"
"To maraba,qarasa daki nima gani nan tasowa"
"Toh" ta amsa idanunta na satar kallon kebantaccen dakin da tasan cewa mahaifiyarta na sauka ciki duk sanda tazo garin,dakin a bude yake saidai an dan karashi hakan yasa ba zata iya gane da mutum ko babu ba da haka ta sanya kanta cikin dakin inna kulu dake falle daya dauke malale da leda da labulaye gami da lailayayyen gadon qarfe da doguwar kujera qwaya daya wanda dukkan wannan gyaran aikin ummin nata ne.