← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 53 OF 114

Sashe 53

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Qarar wayarshi da ya manta shaf ba manta ba ta katse shi
"Ya salam" ya fada cikin salo na qosawa,ya saba idan yana so ya huta yakan kashe wayarshi ne a dare har sai gari ya waye don kada wani abu ya bullo da zai hanashi samun hutu,miqewa zaune yayi ya miqa hannunshi saman side drower ya dauko wayar,number ce babu suna,a gajiye ya daga ya kara a kunnenshi,kuka ya soma ji kafin daga bisani ya gane wace,zeenart ce,kuka take masa sosai
"Meye haka ne zeenart...me kike yi ne haka?" Ya fada cikin baci bacin rai
"Yanzu ya khalipha tsakani da Allah saboda bare shine ka gujemu ka zabi bare a kanmu?...mu 'yan uwanka ya khalipha?..." Ta qarashe maganar tana sake fashewa da kuka
"Stop it zeenart.....bana son shirme don Allah da tsakiyar daren nan" yana gama fada ya katse wayar yana sakin dogon tsaki,ba don anni bama da duk cikinsu a yanzu babu wanda ya isa ya rabo kusa da shi,baijin akwai wanda zai sake kalla a cikinsu koya mu'amalancesu.

Yana shirin sake kwanciya wata wayar ta sake shigowa,tsaki ya sake ja kaman bazai daga ba sai yaga lambar data jibanci kamfaninsu ce
"Am verry sorry sir...." Ya fada cikin ladabi mai maganar ya fadi haka
"Ba matsala joe....me ya faru?"
"Sir...ka duba email dinka,zancan kwangilar nan ne nake ga kamar akwai matsala,na tura maka komai ka duba ka gani"
"Ohk...ohk" ya fadi da sauri yana kashe wayar,sannan ya sauka a nutse ya binciko inda ya aje system din nasa,sai daya kunnata sannan ya koma saman gadon ya zauna.

Aiki yayi sosai mai yawan gaske,tun yana yi cikin marmari har idanunsa suka soma nauyi suna lumshewa,tilas ya katse duk wani aiki ya zube saman gadon ba tare daya ma samu ya kashe cumputer din ba.

Daga bangaren aysha kuwa tunda mai aikin anni ta kaita dakin tana zaune daga bakin gadon,saidai zuwa yanzun ta janye mayafinta baya sosai yadda zaka iya hangen fuskarta,a hankali take qarewa dakin kallo...,dakine falle daya mai hade da toilet,akwai gado mirrow da wardrobe a ciki,komai na dakin ruwan madara ne hakanan tsarin da aka yiwa dakin dole ya burgeka,sosai ya yiwa aysha kyau ba kadan ba,shi kadaine a rea din sauran dakunan suna daga farko.

Amal ce data kasa zama tafe a gaba,kishi sosai take ji yana cik zuciyarta saidai tana qoqarin danneshi,ji take sam ba zata iya kwana ba bataga fuskar amaryar ba,tana fata bata fita da komai ba saboda watan watarana ta fata itama ta zama mata a gareshi,mai aikin anni na biye da ita dauke da kwanukan abinci,kayan tea da flask din ruwan zafin da anni tace a kawo mata ko zata buqata.

Qarar bude qofar ya sanyata saurin sunkuyar da kanta,idanun amal qyarrrr a kanta tayi sallama aysha ta amsa,suka qarasa gabanta mai aikin ta aje kayan ta fita,kusa da ita amal ta zauna cikin salon barkwanci tace
"Haba matar ya khalipha,ban taba ganinki bafa,nima rowar ganin fuskar taki zakiyimin,ai ni ba baquwar kunyarki bace saiki bude fuskar taki na gani" ta fada tana ja mata mayafin baya fuskar ayshan ta fito,sosai gabanta ya fadi sanda aysha ta dago suka hada idanu fuskarta qunshe da murmushi,bata taba tsammanin ganinta haka ba,lallai tabbas dole khalipha yaqisu kafataninsu,ko ita da take mace ba qaramin kyau ayshan tayi mata ba balle da namiji,ba shakka ko itace zata qisu din ta zabi ayshan,da qyar ta hadiye wani abu daya tsaya mata a wuya ta miqe tana cewa
"Ni suna na amal,cousin sis din ya khalipha,ga abincin nan ko zaki buqata,akwai toilet gashi can cikin dakin,akwai kayan bacci a wardrobe,ki kwanta ki huta matar ya khalipha" ta fada taba murmushin yaqe tare da juyawa zata fice daga dakin,banbarakwai aysha taji da sunan da amal din ta bata na qarshe,wai matar khalipha
"Na gode" ta fada a hankali,sai amal din ta juyo tana kallonta, sannan tace
"Babu komai" ta qarasa ficewa daga dakin gami da ja mata qofa,kuka sosai ta rushe da shi sanda ta shiga dakinta,bata ga wata hanya ba,bata ga wata kafa da zata shigewa khalipha ba,ko ina a toshe yake.

Aysha kuwa bandakin ta shiga tayi fitsari sannan ta daura alawa,bata buqaci kayan bacci ba ta ware mayafinta da yake babba ne mai kauri tayi shafa'i da wuturi ta maida kanta ta kwanta,tana jin gajiya na nuqurqusarta,duk da cewa ba wani zirga zirga tayi ba don bata dauki hidimar da dumi ba.

To sai nace asuba ta gari ahalin gidan mai goro .

************************

A gurguje ya shirya ganin har sha daya na safe bai fita cikin gida ba,bashin baccin kwana da kwanaki ya tabbata shi ya danneshi,cikin qananun kaya ya shirya ya fito yayi tsaf da shi kamar kowanne lokaci,sannan ya zira takalminsa half cover ya fito zuwa sashen annin.

Falon nata shuru babu kowa,hakan ya alamta masa wataqila itama gajiya ta hanata fitowa da wuri,yana shirin wucewa zuwa dakinta sai gata ta fito,fuskarta wasai da fara'a ta tarbeshi,cikin girmamawa kamar yadda ya saba ya gaidata
"Yau duka munyi nauyin bacci,don har masu aikin basu jima da gama abincin kari ba,yanzu nake shirin kiranka a waya dama,mun bar baquwa ita kadai bamu bata abun kari ba,bamu san yaushe ta saba cin abincin safe ba" murmushi kawai yayi don ko shi dinma baisan yaushe take karyawa ba,kar yaje yayi magana kuma ya kwafsa shi yasa ya zabi yayi shirun
"Dubata khalipha ta fito mu karya baki daya ko?,hakan zaifi" ba haka yaso ba amma bazai iya cewa a'ah ba,saboda haka ya aje wayoyinsa ya wuce zuwa dakin.

Fitowarta kenan daga wanka tana gaban mudubi bayan ta gama shafa mai tana gyara dogon gashinta,wanda ba yadda aliya vatayi da ita a biki ba suje ayi mata gyaran kai amma sam taqi,tafi ganewa ta gyara abinta a gida da kayan gyara na gargajiya,tunda yana santsi da tsaho abinshi,jin ana kiciniyar bude qofa ya sanyata yayar mayafinta ta yabawa kanta baima yafu a dai dai ba,tayi tsan tana jiran taji wanda zai shigo.

Da sallama ya shigo suka hada idanu kasancewar idonta na bakin qofar,amsawa tayi tana saukar da idonta qasa,idanunshi yakai kan saman goshinta dake kwance da sumar da bai taba gani ba,tunda ko yaushe cikin hijabi da dankwali take bata bari sumarta ko daya ta fito,dauke kanshi yayi yana jingina da bango
"Ina kwana" ta gaidashi da muryarta mai sanyi,masa mata yayi da
"Lpy lau ya kwanan baqon waje....anni tace ki fito mu karya"
"Toh" ta bashi amsa,saidai bata iya motsawa ko ina ba saboda tana son ta qarasa shiryawa ne,ya karanceta sai ya juya yaba yunqurin bude qofa yace
"Idan kin gama ina qofar dakin" ya qarasawa fice,a gaggauce ta daure gashinta ya daura dankwalinta sannan ta gyara yafen mayafin nata ta fito.

Yana gaba ne tana binsa a baya har zuwa cikin falon,kallonta anni take fuskarta qunshe da murmushi ,tausayinta ayshan na sake ratsa zuciyarta
"Kyakkyawar yarinya mai shekarun da basu haura a shirin ba,ya ilahi ko meye aibunta oho?" Anni ke tambayar kanta,tamkar aysha zata nutse haka taji sanda anni ta miqa mata hannu suyi musabaha,sai ta rasa inda zata tsoma kanta,khalipha na jingini saman kujera kamar mai shirin yin kwanciyar rigingine yana noticing abinda yake faruwa,murmushi anni tayi
"Ki daukeni kamar uwa wadda ta haifeki aishatu kinji,daga yau nan gidanku ne,bana so ki sake tuna wani abu daya faru dake a baya,ya zama tarihi daga yau da yardar Allah" kai ta gyada cikin tsananin kunya,har yanzu ta kasa kallon annin
"Muje muci abinci.....bansan me ya hana amal fitowa ba har yanzu,duba min ita khalipha" ba'a son ranshi ba ya miqe zuwa dakinta,a lokacin tana zaune saman kujerar mudubi bayan ta fito daga toilet data shiga ta wanke fuskarta saboda kukan data ci,knocking yayi mata ta tambayi waye
"Ki fito inji anni,tym for breakfst" daddadar muryarshi ta daki dodon kunnenta,saita lumshe ido kamar yana tsaye a gabanta,lumshe idanun daya fito da wasu sabbin hawayen,tuni yayi gaba bai tsaya jin me zata ce ba,saidata sake wanke fuskarta ta goga hoda da kwalli sannann ta fito.

Dauke idanunta tayi da sauri sanda idonta ya sona tozali da aysha daje zaune saman kujerar dining idanunta a qasa ta kasa sakewa,fresh skin dinta,manyan idanuwa da zara zara eye lashes,qaramin bakinta komai dai dai kamar wadda ta zana,kai ko ita ta zana bata jin zata zana mai kyau kamar wanda Allah ya bata din,sai data zo gab da su sannan ta iya dauke idanunta,ta qaqalo murmushin dole ta sorawa fuskarta tana jan kujera daya wadda ke daura da khalipha ta zauna tana fadin
"Amarsu ta ango" kunya maganar ta baiwa aysha,gaisawa sukai sannan amal din ta gaida anni,annin na tamabayarta ko gajiya ce ta hanata fitowa,amsa mata kwai tayi da eh amma ita kadai tasan meke cin zuciyarta,kusan dai cin abincin su uku suka yishi banda aysha,ta kasa taba komai,ji take kamar kowa ma kallonta yake,amal dinma kawai qarfin hali take tana tsakura tare da basarwa,har suka gama babu abinda aysha ta iya kaiwa bakinta,anni nata qorafin hakan khalipha na jinsu,kusan baida wata idea kan halayyarta shi yasa baida abun tofawa.

Sanda ya miqe ne anni tace masa
"Ya kamata ka wuce sashenka da ita sai ta samu taci wani abin a can tunda a nan ta kasa sakewa taci komai,zan turo muku badi'a ta tayaku gyaran wajen ko?"
"Ohk...zanyiwa kamfani magana ma akwai gyare gyaren da za'a yiwa wajen"
"Ya kamata....aysha kuje yanzun zan turo badi'a"amsawa tayi sannan ta miqe tabishi a baya suka fice.

Kamar mai tsoron wani abu haka take biye da shi a baya,tana jin fargaba da tsoro hakanan,a haka suka isa sahen nashi ba wanda yace komai da dan uwansa.
Chapter 53 · 0% Book details