Sashe 60
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Minti talatin ya sake saukowa,ya tsuke cikin qananun kaya,yana dannan waya ba tare daya dubeta ba koya kula da kukanta yace
"Ina abinci na?" Shuru tayi masa da fari har na tsahon minti uku
"Ina abinci na!" Ya sake tambayarta karo na biyu cikin qaraji da fushi wanda ya kada mata 'ya'yan hanji ta soma qwallawa rebacca kira
"Ohkey.....wai na tambayeki mana?,na kawo mai aiki ne donta kula dani ko don ta tayaki aiki?"
"Duka gaba daya" ta bashi amsa cikin bacin rai,cike da fushi yake nuna kanshi
"Ni kike baiwa amsa haka kai tsaye?"
"Waikai hamid me yake damunka ne?,ya za'ayi mu rabu lafiya da kai sannan kazo kana min wasu abubuwa kaman dan qwaya?" Dariya ya saki
"Au bakisan dam qwayar bane ni?,yau zakisan ni cakken dan qwaya ne tunda baki iya zama da miji ba" ya fada a sanda rebacca ta gama jera abincin ta fice,don kusan duk a kunnenta ake komai,zama yayi ba tare daya sake dubanta ba ya take cikinsa da abinci sannan ya miqe yasa kai zai fice,har yayi gaba ya dawo da baya
"Ina canjin cefanen da lado yayi dazu?" Cikin mamaki take kallonshi,a arziqinsa bata taba tunanin zai tambayi wani canji cefane ba wanda baifi dubu daya ba,ita a wajenta dubu daya ba komai bace
"Dubu dayan kake tambayata?"
"Ita ba kudi bace?...ko satowa nakeyi?,tashi malama ki dauko min" bacin ranta da mamakin sauyawar hamid dare daya suka sake yawa
"Bazan bayar ba,wannan wane irin nuna talaici ne?,dubu daya kawai?" Mari ya kai.mata Allah yasa tayi gaggawar kaucewa
"Ni zaka mara hamid?"
"Na nuna miki kadan daga abinda zan iya yine idan har na dawo baki nemo min dubu dayata ba duk inda kika kaita" daga haka ya juya ya fice abinsa,da kallo ta bishi hadi da hawayen takaici,a rayuwarta tunda taje ta taba daukar koda dubu dari ta riqe hamid zai magana akao bare dubu daya?,tunda take rayuwar gidansu ta taba baiwa dubu qwaya daya wani muhimmanci mai yawa?anya lafiya ko hamid yake?,kanta bazai iya daukar wannan abun ba haka ya sanya kai tsaye ta soma kiran lambar mommynta
Tana dagawa mummyn ta fashe da kuka,a rikice mummyn ke cewa
"Ke...lafiya asma'u,me ya faru?"
"Mummy hamid ne..."
"Hamid?,me ya sameshi?" Nan ta kwashe duk abinda ya faru ta sanar mata,take mummyn ta cika tayi fam
"Lallai yaron nan mugun dan iska ne,ce masa akayi baiwa aka kawo masa da zaice zai dakeki?,to wallahi daga yanzu ba yarda ba,duk sanda ya sake yunqurin dukanki ki tattara ki taho gida,idan yaso babanki ya masa jan kunne mai qarfi"
"A'h mummy,basai na taho ba,kinsan ma halin daddy baya yarda da irin wannan"tasan sarai ba wai daddyn take dubawa ba kawai,tsabar son miji ne
"Karki sake ki yarda dai ya dakeki wallahi ban lamunta ba,duk abinda ya sake faruwa ki sanarmin don bazan lamunci wannan iskancin ba" da haka suka rabu da mummyn ta aje wayar tana dakon dawowar hamid din.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
A hankali ta turo qofar falon tamkar wadda ke sanda,idanunsa ya dago daga saman screen din system din da yake aiki akai,qwayar idanunshi wanda suke cikin farin gilashi da yake aiki da shi lokaci zuwa lokaci idan zai jima yana kallon screen ta fito tarwai,saidai ta danyi ja kadan gami da lumshewa saboda gajiya da kuma bacci da yake ji,a hankali ta janye tata qwayar idanun kamar yadda shima yayin ya maida kan screen din,cikin muryarta mai sanyi tayi sallama tana takowa cikin falon,tun dazun ya shigo don shi baima zauna ba a falon bayan sun gama cin abinci ya yiwa anni sallama yace yana da aiki da yawa yau,a can ya barta tana jin caftar su haidar tana kwasar dariya a ciki,ta sake sosai yau saboda rahama bata nan ta tafi gidan qanin anni zata musu kwana uku
"Zo" taji ya fadi sanda take shirin gifta shi,saita dawo da baya ta samu waje nesa kadan dashi ta zauna bayan ta nade qafafunta a qirjinta ta rungumesu kamar wata 'yar mage,bai dago ba har sai daya kammala tura wani saqo sannan ya rufe cumputer din ya zare gilashin fuskarsa yasa handkherchief ya goge idanun nasa sannan ya dubeta,kusan a tare suka kalli juna kowa kuma ya janye idanunshi,baisan me yasa sau da dama sukan kalli juna lokaci guda ba su kuma janye lokaci guda
"Meye babban burinki yanzu a rayuwa?" Ya jeho mata tambayar kai tsaye,shuru ne ya ratsa dakin tamkar ba kowa a ciki,ya kafeta da idanu yana karantarta,yayin da ita kuma take kallon tafin hannunta tana matsawa kamar wadda yakewa ciwo,abu biyu,abu guda biyu ne yake mata kai kawo a ranta,burinta na farko a duniya ta samu kusanci yarda da aminci na mahaifiyarta,burinta na biyu na biyu shine ta samu ilimi mai zurfi,ilimin da zai sauyata,ya zamewa rayuwarta garkuwa,karatun da tayi har yanzu bataji ta qoshi ba,har yanzu tana da qishirwarsa,har yanzu bata jin ta cimma gaci.
"Mahaifiyata....ina da burin naganni ni da ita tamkar kowacce 'ya da uwa" sai tayi shuru tana hadiyar zuciya kadan kadan,tana son danne mikin daya taso mata
"Bayan wannan fa?"
"Karatu" shuru ya sakeyi yana nazari,kafin daga bisani ya jawo wata paper ya danyi rubutu ya ninketa
"Kina da jamb?" Kai ta gyada da sauri
"Eh last year nayi,ta na nan"
"Good,kina da zabin makarantar da kikeso?"kai ta kada
"Duk wadda na samu inaso,matuqar dai makaranta ce" kai ya jinjina na tsahon wasu mintuna kafin yace
"Is ohk,zakije wudil?" Kai ta jinjina itama da sauri murmushi na qwacewa daga fuskarta,ganin mafarkinta na nesa na shirin zuwa kusa,burinta na gab da cika
"Ba damuwa" ya fada ta sigar dake nuna ya sallameta,da hanzari ta miqe tayi daki,cike da farinciki ta dira saman carfet din dake gefe guda wanda ta maidashi makwancinta,don ko da wasa bata taba hawa gadonshi ba,murna take sosai ita kadai a dakin,ba don dare yayi ba da ba shakka saita kira aliya ta shaida mata,don ba'a boyewa abokin kuka mutuwa.
Sai data gama dararta sannan ta soma sauya kayan jikinta zuwa na bacci masu kauri da taushi,ta saka dan qaramin hijabin da take kwana da shi wanda iyakarsa qirji ta shiga toilet ta daura alwalar kwanciya bacci(yana da kyau mu kasance cikin alwala a duk sanda zamu kwanta bacci,domin hakan ba qaramin kariya bace a garemu daga sharrin shaidanun mutane da kuma shaidanun aljanu,bama lokacin bacci ba kawai,a wuninmu gaba daya yana da kyau mu dinga zama da alwala,Allah yayi mana tsari,yasa mu dace duniya da lahira amin summa amin).
Tana zaune tana karanto addu'ar bacci taji ana knocking qofar,sai a sannan ta tuna bata rufe ba,tsuru tsuru tayi da ido ita batayi magana ba hakanan bata miqe ba,jin shuru yayi yawa yasanyashi turo qofar ya dubeta yana kauda kai
"Am sorry zan dauki blanket ne" sai kuma ya dawo da kanshi inda ya ganta,zai magana sai kuna ya fasa,ya isa ma'ajiyarsu ya dauki daya hadi da pillow sannan yace
"Me yasa kika zabi kwana a qasa?"
"Babu komai" ta fada a sanyaye,baice komai ba ya juya ya fice daga dakin,ta qarasa addu'arta ta koma ta kwanta ranta fari qal idan ta tuna batun ci gaba da karatunta.
Qarfe shida na safe ta gama shiryawa tsaf cikin lafaya,ta nade jikinta sosai kamalarta ta fito,fatarta data sake kyau da qyalli sakamakon isashshen hutu ta sake bayyana sosai cikin kalar tufafin dake jikinta,ranta fari qal,yau ita daya tasan farincikin da take ciki,duk zumudi ya cikata sakamakon screening da zata wudil,a haka ta fito parlourn ta tadda shi tsaye yana kurbar ruwan dumi a cup,wanda sabonshi ne hakan duk safiya kafin yaci komai,don yana wanke duk wani system na jikin mutum tare da inganta lafiya,ido ya dan xuba mata ganin yadda take ta faman zumudi,fara'ar fuskarta tafi tako yaushe,wanda hakan ya sake bayyana mishi irin yadda take qaunar karatu a rayuwarta,gaidashi tayi ya amsa taci gaba da tsaiwa tana jiran jin me zaice,sai daya gama shan ruwan sannan ya aje cup din
"Ban sanarwa da anni ba....bansan ya zata dauki zancan ba"duk sai taji daukinta ya tsaya,kuzarin data fito da shi ya ragu,dan soma takawa yayi ya nufi qofa a sanyaye tabi bayanshi.
A parlour suka tadda haidar riqe da muqullin mota kamar yadda khalipha ya tsara shi zai kaita,da alama magana suke da anni,dubansu take har suka qaraso cikin falon,aysha ce ta soma gaidata sannan haidar itama ya gaidata,daga bisani ta koma gefe ta lafe tana ji suna gaisawa da khalipha
"Me zasu yi a wudil da safiyar nan?"
"Screening zasu....zan miki bayani anni"
"Screening?" Ta maimaita tana danyi shuru kamar mai nazari,kada kai tayi daga bisani sannann tace
"Haka zaku tafi kenan baku karya ba?"agogo haidar ya duba sannan yace
"Zamu karya a hanya karmu bata lokaci,amma ban sani ba ko anty zata ci wani abun"
"Na qoshi" ta fada da sauri wanda har hakan ya sanya khalipha waiwayowa ya dubeta,yayin da anni ta saki murmushi saboda ta karanci zumudin da takewa tafiyar,duk da bata gama fahimtar tafiyar ta meye ba
"Allah ya kiyaye hanya,saikun dawo" anni ta fada suka juya suka fice khalipha na jawa haidar kunne kan tuqin ganganci.
"Ina abinci na?" Shuru tayi masa da fari har na tsahon minti uku
"Ina abinci na!" Ya sake tambayarta karo na biyu cikin qaraji da fushi wanda ya kada mata 'ya'yan hanji ta soma qwallawa rebacca kira
"Ohkey.....wai na tambayeki mana?,na kawo mai aiki ne donta kula dani ko don ta tayaki aiki?"
"Duka gaba daya" ta bashi amsa cikin bacin rai,cike da fushi yake nuna kanshi
"Ni kike baiwa amsa haka kai tsaye?"
"Waikai hamid me yake damunka ne?,ya za'ayi mu rabu lafiya da kai sannan kazo kana min wasu abubuwa kaman dan qwaya?" Dariya ya saki
"Au bakisan dam qwayar bane ni?,yau zakisan ni cakken dan qwaya ne tunda baki iya zama da miji ba" ya fada a sanda rebacca ta gama jera abincin ta fice,don kusan duk a kunnenta ake komai,zama yayi ba tare daya sake dubanta ba ya take cikinsa da abinci sannan ya miqe yasa kai zai fice,har yayi gaba ya dawo da baya
"Ina canjin cefanen da lado yayi dazu?" Cikin mamaki take kallonshi,a arziqinsa bata taba tunanin zai tambayi wani canji cefane ba wanda baifi dubu daya ba,ita a wajenta dubu daya ba komai bace
"Dubu dayan kake tambayata?"
"Ita ba kudi bace?...ko satowa nakeyi?,tashi malama ki dauko min" bacin ranta da mamakin sauyawar hamid dare daya suka sake yawa
"Bazan bayar ba,wannan wane irin nuna talaici ne?,dubu daya kawai?" Mari ya kai.mata Allah yasa tayi gaggawar kaucewa
"Ni zaka mara hamid?"
"Na nuna miki kadan daga abinda zan iya yine idan har na dawo baki nemo min dubu dayata ba duk inda kika kaita" daga haka ya juya ya fice abinsa,da kallo ta bishi hadi da hawayen takaici,a rayuwarta tunda taje ta taba daukar koda dubu dari ta riqe hamid zai magana akao bare dubu daya?,tunda take rayuwar gidansu ta taba baiwa dubu qwaya daya wani muhimmanci mai yawa?anya lafiya ko hamid yake?,kanta bazai iya daukar wannan abun ba haka ya sanya kai tsaye ta soma kiran lambar mommynta
Tana dagawa mummyn ta fashe da kuka,a rikice mummyn ke cewa
"Ke...lafiya asma'u,me ya faru?"
"Mummy hamid ne..."
"Hamid?,me ya sameshi?" Nan ta kwashe duk abinda ya faru ta sanar mata,take mummyn ta cika tayi fam
"Lallai yaron nan mugun dan iska ne,ce masa akayi baiwa aka kawo masa da zaice zai dakeki?,to wallahi daga yanzu ba yarda ba,duk sanda ya sake yunqurin dukanki ki tattara ki taho gida,idan yaso babanki ya masa jan kunne mai qarfi"
"A'h mummy,basai na taho ba,kinsan ma halin daddy baya yarda da irin wannan"tasan sarai ba wai daddyn take dubawa ba kawai,tsabar son miji ne
"Karki sake ki yarda dai ya dakeki wallahi ban lamunta ba,duk abinda ya sake faruwa ki sanarmin don bazan lamunci wannan iskancin ba" da haka suka rabu da mummyn ta aje wayar tana dakon dawowar hamid din.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
A hankali ta turo qofar falon tamkar wadda ke sanda,idanunsa ya dago daga saman screen din system din da yake aiki akai,qwayar idanunshi wanda suke cikin farin gilashi da yake aiki da shi lokaci zuwa lokaci idan zai jima yana kallon screen ta fito tarwai,saidai ta danyi ja kadan gami da lumshewa saboda gajiya da kuma bacci da yake ji,a hankali ta janye tata qwayar idanun kamar yadda shima yayin ya maida kan screen din,cikin muryarta mai sanyi tayi sallama tana takowa cikin falon,tun dazun ya shigo don shi baima zauna ba a falon bayan sun gama cin abinci ya yiwa anni sallama yace yana da aiki da yawa yau,a can ya barta tana jin caftar su haidar tana kwasar dariya a ciki,ta sake sosai yau saboda rahama bata nan ta tafi gidan qanin anni zata musu kwana uku
"Zo" taji ya fadi sanda take shirin gifta shi,saita dawo da baya ta samu waje nesa kadan dashi ta zauna bayan ta nade qafafunta a qirjinta ta rungumesu kamar wata 'yar mage,bai dago ba har sai daya kammala tura wani saqo sannan ya rufe cumputer din ya zare gilashin fuskarsa yasa handkherchief ya goge idanun nasa sannan ya dubeta,kusan a tare suka kalli juna kowa kuma ya janye idanunshi,baisan me yasa sau da dama sukan kalli juna lokaci guda ba su kuma janye lokaci guda
"Meye babban burinki yanzu a rayuwa?" Ya jeho mata tambayar kai tsaye,shuru ne ya ratsa dakin tamkar ba kowa a ciki,ya kafeta da idanu yana karantarta,yayin da ita kuma take kallon tafin hannunta tana matsawa kamar wadda yakewa ciwo,abu biyu,abu guda biyu ne yake mata kai kawo a ranta,burinta na farko a duniya ta samu kusanci yarda da aminci na mahaifiyarta,burinta na biyu na biyu shine ta samu ilimi mai zurfi,ilimin da zai sauyata,ya zamewa rayuwarta garkuwa,karatun da tayi har yanzu bataji ta qoshi ba,har yanzu tana da qishirwarsa,har yanzu bata jin ta cimma gaci.
"Mahaifiyata....ina da burin naganni ni da ita tamkar kowacce 'ya da uwa" sai tayi shuru tana hadiyar zuciya kadan kadan,tana son danne mikin daya taso mata
"Bayan wannan fa?"
"Karatu" shuru ya sakeyi yana nazari,kafin daga bisani ya jawo wata paper ya danyi rubutu ya ninketa
"Kina da jamb?" Kai ta gyada da sauri
"Eh last year nayi,ta na nan"
"Good,kina da zabin makarantar da kikeso?"kai ta kada
"Duk wadda na samu inaso,matuqar dai makaranta ce" kai ya jinjina na tsahon wasu mintuna kafin yace
"Is ohk,zakije wudil?" Kai ta jinjina itama da sauri murmushi na qwacewa daga fuskarta,ganin mafarkinta na nesa na shirin zuwa kusa,burinta na gab da cika
"Ba damuwa" ya fada ta sigar dake nuna ya sallameta,da hanzari ta miqe tayi daki,cike da farinciki ta dira saman carfet din dake gefe guda wanda ta maidashi makwancinta,don ko da wasa bata taba hawa gadonshi ba,murna take sosai ita kadai a dakin,ba don dare yayi ba da ba shakka saita kira aliya ta shaida mata,don ba'a boyewa abokin kuka mutuwa.
Sai data gama dararta sannan ta soma sauya kayan jikinta zuwa na bacci masu kauri da taushi,ta saka dan qaramin hijabin da take kwana da shi wanda iyakarsa qirji ta shiga toilet ta daura alwalar kwanciya bacci(yana da kyau mu kasance cikin alwala a duk sanda zamu kwanta bacci,domin hakan ba qaramin kariya bace a garemu daga sharrin shaidanun mutane da kuma shaidanun aljanu,bama lokacin bacci ba kawai,a wuninmu gaba daya yana da kyau mu dinga zama da alwala,Allah yayi mana tsari,yasa mu dace duniya da lahira amin summa amin).
Tana zaune tana karanto addu'ar bacci taji ana knocking qofar,sai a sannan ta tuna bata rufe ba,tsuru tsuru tayi da ido ita batayi magana ba hakanan bata miqe ba,jin shuru yayi yawa yasanyashi turo qofar ya dubeta yana kauda kai
"Am sorry zan dauki blanket ne" sai kuma ya dawo da kanshi inda ya ganta,zai magana sai kuna ya fasa,ya isa ma'ajiyarsu ya dauki daya hadi da pillow sannan yace
"Me yasa kika zabi kwana a qasa?"
"Babu komai" ta fada a sanyaye,baice komai ba ya juya ya fice daga dakin,ta qarasa addu'arta ta koma ta kwanta ranta fari qal idan ta tuna batun ci gaba da karatunta.
Qarfe shida na safe ta gama shiryawa tsaf cikin lafaya,ta nade jikinta sosai kamalarta ta fito,fatarta data sake kyau da qyalli sakamakon isashshen hutu ta sake bayyana sosai cikin kalar tufafin dake jikinta,ranta fari qal,yau ita daya tasan farincikin da take ciki,duk zumudi ya cikata sakamakon screening da zata wudil,a haka ta fito parlourn ta tadda shi tsaye yana kurbar ruwan dumi a cup,wanda sabonshi ne hakan duk safiya kafin yaci komai,don yana wanke duk wani system na jikin mutum tare da inganta lafiya,ido ya dan xuba mata ganin yadda take ta faman zumudi,fara'ar fuskarta tafi tako yaushe,wanda hakan ya sake bayyana mishi irin yadda take qaunar karatu a rayuwarta,gaidashi tayi ya amsa taci gaba da tsaiwa tana jiran jin me zaice,sai daya gama shan ruwan sannan ya aje cup din
"Ban sanarwa da anni ba....bansan ya zata dauki zancan ba"duk sai taji daukinta ya tsaya,kuzarin data fito da shi ya ragu,dan soma takawa yayi ya nufi qofa a sanyaye tabi bayanshi.
A parlour suka tadda haidar riqe da muqullin mota kamar yadda khalipha ya tsara shi zai kaita,da alama magana suke da anni,dubansu take har suka qaraso cikin falon,aysha ce ta soma gaidata sannan haidar itama ya gaidata,daga bisani ta koma gefe ta lafe tana ji suna gaisawa da khalipha
"Me zasu yi a wudil da safiyar nan?"
"Screening zasu....zan miki bayani anni"
"Screening?" Ta maimaita tana danyi shuru kamar mai nazari,kada kai tayi daga bisani sannann tace
"Haka zaku tafi kenan baku karya ba?"agogo haidar ya duba sannan yace
"Zamu karya a hanya karmu bata lokaci,amma ban sani ba ko anty zata ci wani abun"
"Na qoshi" ta fada da sauri wanda har hakan ya sanya khalipha waiwayowa ya dubeta,yayin da anni ta saki murmushi saboda ta karanci zumudin da takewa tafiyar,duk da bata gama fahimtar tafiyar ta meye ba
"Allah ya kiyaye hanya,saikun dawo" anni ta fada suka juya suka fice khalipha na jawa haidar kunne kan tuqin ganganci.